AZIZA DA AZIMA COMPLETE HAUSA NOVEL

AZIZA DA AZIMA 21-30

“me ya kamata nayi? Dole na haɗa maganin ganowa idanuna, amma kafin na samu furen surfa sai naje jejin gangare, kuma kafin na dawo sai na samu kwana biyu sabida dogon tafiya ne ban ci ta zama ba, In sha Allahu zan tafi gobe” yana gami fadi ya fito ya shiga bukkar Hajja ya gaya mata gobe da safe zai tafi jejin gangare Hajja ta ce

“Me zaka je yi?”

“Akwai maganin da nake son haɗawa ne, kuma furen da ganyen dole sai naje jejin gangare”

“To Baffa yan biyu Allah ya kaimu lafiya” Baffa ya amsa da amin ya fice, bai zarce ko ina ba sai wajan Ardo bai boye masa komai ba kasancewarsa mahaifinsa ya gaya masa komai, sosai hankalin Arɗo ya tashi ya kallesa ya ce

“Magaji bana so ka gaya ma kowa wannan batun ka ji ko? Har sai ka tabbatar” Baffa ya gya ɗa kai cike da damuwa, nan suka ci gaba da tattaunawa a kan lamarin.

    ????????????????????????

COMMENTS AN SHARE

BY MOMYN AHLAN

[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: ????????????????????????????????????????

    ????✨ *AZIMA DA AZIZA*????✨

    (???? _Macizai ne_????)

    MALLAKAR.

*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*

SAHIBAR KAINUWA.

Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din

0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.

Sanarwa.

Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*____________________________________*

*????KAINUWA WRITERS✍???? ASSOCIATION*????????

”'{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}”’

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*????????

https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association

*____________________________________*

*MARUBUCIYAR.*

1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._

2- _GUDU A JEJI._

3- _SHUHADA._

4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._

5- _WA’YA KASHE ZAHRA’U?(#200)._

6- _COLONEL UBAIDULLAH._

7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._

8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._

9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._

10- _DA NA SANI NA._

  11- _BADAWIYYAH_

12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_

Now

13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE????)_

_Follow me on wattpad,@Fateemah’0_

   ????????????????????

*YAR UWA ZO BIYA KUDIN KARATUNKI DAN JIN YADDA ZATA KAYA A CIKIN BOOK DIN AZIMA DA AZIZA MACIZAI NE, BIYA DARINKI KACAL YANZU,IDAN KUMA NA KAMMALA CMPLT DARI UKU ZAKI SAMESA.*

*LAST FREE..*

????️==2️⃣3️⃣↪️2️⃣4️⃣

Da washe gari asubanci Baffa ya yi ya bar yankin kwana dan bai ga ta zama ba, ko da Aziza ta farka ita ce kawai ta tambayi ina Baffa yake nan Hajja ke gaya mata ya tafi jejin gangare dan samo wasu ganyen magani, Aziza ta ce

“Allah ya dawo min da Baffana lafiya” Hajja ta amsa da amin.

     Ita kuwa Azima tunda ta fara bacci ba ita da farkawa ba sai gefen sallar la’asar, ko da ta farka Aziza na shirin ɗora mata hannu a goshi ta yi saurin rike hannun Aziza ta ce

“Ba bukata Aziza, yau ina cikin farin ciki babu wanda zan kashe amma za a mutu dayawa gobe! A’a ba wai ina nufin ta hannuna ba fa,dan naga kina min wani kallo! Wallahi babu wanda zan kashe! Amma gobe akwai zubda jini a yankin kwana!” tana gama fadi ta tashi ta fito ta samu Hajja a tsakar gida, Hajja ta ce

“Azima wannan baccin naki ya yi yawa, haba dan Allah mutum ya ta faman bacci ba sallah ba salati ko kina fashin sallah ne?”

Yatsine fuska Azima ta yi kafin ta ce

“Ni fa Hajja wannan fashin sallan da kika fadi me ma yake da suna? Al’ada ko? To ni banayi! Kuma ban taba yi ba! Sallah gabadayanta ne bana yi,kuma ma Hajja sadda Aziza ke zuwa islamiyyar Malam Saini ni kin taba gani naje ne? Har Aziza ta yi sauko ni ban taba zuwa Islamiyyar Malam Saini ba,ko kuma kin taba gani da watan ramadan ina azumi? Ki kyaleni da maganar wani abu wai shi sallah!” tana gama fadi ta fice, Aziza na tsaye a bukka tana kallon Azima, bayan Azima ta fita Hajja ta kalli Aziza hankali tashe ta ce

“Aziza meke damun yar uwarki!?” murmushin tausayin Hajja Aziza ta yi ta matso kusa da Hajja ta kama hannunta ta ce

“Kun kusa ku sani Hajja nan ba da jimawa ba, dan bazan iya jure ganin hawayenki na zuba a kanmu ba, zan gaya miki gaskiya da zaran Baffa ya dawo ko da kuwa za a kashemu!” 

    Hajja ta bude baki za ta yi magana da sauri Aziza ta ce

“Dan Allah Hajja karki ce komai, Azima bata sallah bata salati bata Azumi duk wani aikin ibada bata yi,na gaji da miki karya Hajja, bazan iya jure miki karya ba!” tana gama fadi ta fice da gudu da kuka.

Aka bar Hajja da kakkarwar jiki.

        @@@@@

Da yamma sai ga wasika daga yankuna uku izuwa yankin kwana, zasu kawo musu farmaki gobe da safe, hakika wannan sako ya hautsine hankalin jama’ar kwana inda mata da dama har ma da mazan wasu suka fara kuka, sarki Chubaɗo da mai unguwa ori suka ce ga shi Magaji baya nan, kuma babu halin yi masa saƙo har sai ya dawo, saukinta ma Garkuwa ya ɗan samu lafiya, kafin kace me Sarki Chubaɗo ya bada umarnin ayi shela a yankin kwana gabadayanta za a kawo farmakin yaƙi gobe kuma yankuna uku,dan haka kowa ya kasance cikin shiri amma bana tarban yaƙi ba.

@@@@@@

       Hajja da Aziza sun kasa zaune sun kasa tsaye sabida tashin hankali sai jeka ka dawo suke yi a tsakar gida amma Azima na zaune hankali kwance tana fizgar dogon gashinta, Aziza ce ta kallenta ta ga babu alamun damuwa a tattare da ita,cikin haushi da tsanar Azima da ya fara ɗarsuwa a zuciyarta ta ce

“Wai ke Azima wace irin dabba ce ke ana maganar kawo farmakin yaƙi amma kina zaune kina tsifar kai?”

    “Macijiya!” Azima ta faɗa ba tare da ta ɗago ta kalli Aziza ba, Hajja ta juyo a firgice ta ce

“Ma mai kika ce Azima! ?” tana shirin kara nanatawa Aziza tayi saurin faɗin

“Mahaukaciya kawai!”

“Ga ki kuwa babbar mahaukaciya!” Azima ta faɗa tana dagowa a fusace.

    “Dan Allah fadan ya isa haka!” Hajja ta katsesu, 

“Kuyi ta addua kawai Allah ya bamu mafita yafi wannan fadar naku” ko uhum basu kuma cewa ba.

      ????????????????

      

Da washe gari kamar yadda sako ya iskesu haka kuwa ta kasance inda yankin ja’i da yankin jimo da yankin tudu sukayi cincirindo sun zo yaƙar yankin kwana, amma abun mamaki babu wani daga yankin kwana da ya dauki makami, abun ya basu mamaki, Arɗo shine wanda ya fito ya fara magana kasancewarsa Babba, tsohon bafulatani mai dattako

“Mu ba zamuyi yaƙi daku ba, idan har kuna so duk ku sa takwabi ku kashemu! Har ga Allah munyi imani wannan ita ce kaddararmu! Bamu kashe Innu Maciji ba, a ranar da aka kashe Innu muma munyi rashin mutane a yankin nan har mutum sha huɗu, haka ma jarman macizai, sannan sarkin fulanin tudu bamu aikata muku komai ba kawai neman fitina kukeyi,idan kuma yaronka da aka kashe a yankin nan ne laifi ya aikata aka masa hukunci, na rantse da wanda ya busamin numfashi idan har aka samu ɗan wani yankin kwana da laifi makamanciyar wanda ɗanka yazo yankin nan ya aikata wlh mun yarje muku ku fille kansa ku kawo mana kamar yadda mukayi, ba a barin laifi a ɗoran kasa, dan ba a san mai zai kuma aikatawa a gaba ba, mu sabida muna bin al’ada da ibada shiyasa yankinmu ta yi baƙin jini a wajan sauran yankuna, idan har maganar da nayi baku gamsu ba kuna iya shafemu a doron kasa ko kwayi farin ciki” Arɗo na gama fadi jama’ar kwana suka miƙa wuya,ganin haka yasa yankin jimo jikinsu yayi sanyi suka ce ba zasuyi yaƙi da yankin kwana ba,nan take suka juya, yankin tudu da yankin ja’i kuwa sunce suna nan, sai sun shafe yankin kwana.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button