HALIN GIRMA 30

” Mutuwa? Me yayi miki Bashir din?”
Shiru tayi ta rasa me zata ce, dan bata isa ta fadi abinda ya faru tsakanin ta da Bashir din ba, a sanyaye tace
” Mama yana da Mata, kullum sai ta sakani aikin wahala babu dare babu rana, ga tsangwama, karshe ma Mama a BQ nake wallahi.” Sai ta sake fashewa da wani kukan,salati Mama ta saka, ta kama zagaye a dakin tana jin bayanin Zeenat din
” Yana ina, bashi wayar.”
Tun kafin ta bashi ya karba yana mata murmushi,
” Hello Mama.”
” Kana ji? Wallahi tun muna shaida juna da kai ka dawo min da ‘yata, wannan ai wulakanci ne, wallahi ka dawo min da ita kafin kasha mamaki na.”
” Kiyi hakuri Mama, amma Zeenat matata ce,a yanzu nine nake da iko da ita,dan haka kiyi hakuri dai.”
” Kan bala’i, ni kake fadawa haka Bashir?”
” Ayi hakuri Mama, gaskiya ce, sai mun sake kira mu gaishe ki.”
Kafin ta sake magana ya kashe kiran, ya kuma kashe wayar gaba daya ya jefa ta aljihun sa, yayi gaba zai bar dakin ta chakumo shi ta baya
” Na rantse da Allah sai ka rabu dani,sai ka sake ni wallahi ba zan zauna ba, na tsane ka bana son ganin ka.”
Maganganun ta sun masa zafi kwarai, amma sai ya danne ya jawota ya hadata da bangon dakin, ya dalle mata baki sannan ya bi ta da kiss me zafi.
“Idan kika sake yi min ihu wallahi sai nayi fata-fata dake, aure na dake babu saki ko yaji, auren mutukaraba kenan, ko nace miki auren zobe, idan bakiyi wasa ba sai na tabbatar miki da haka a yau din nan, ta hanyar zuba miki ajiyar da baki isa ki guje min ba.”
Tofar da yawu tayi ta durkushe a wajen tana sakin kuka gwanin tausayi. Tsallake ta yayi, yayi ficewar sa yana dariyar mugunta, yana son Zeenat din da gaske, amma kuma ba zai dauki rashin kunyar ta ba, ko kuma ya kyale iyayenta su taka shi ba, sai abinda yaga dama zai yi da ita tun da dai shine me iko da ita a yanzu.
_ZAFAFA BIYAR 2022????_*
*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*
_SO DA ZUCIYA_
*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI’AR ZUCIYA_
*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_
*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_
*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_
*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*????????
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k
*_Zaku tura kudin a_*
6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*
*Sai shedar payment dinki a*????????????
08184017082
*Kokuma katin waya na MTN anan*????????
09134848107
[ad_2]