HEEDAYAH 15

bane, just swing into action, dubi fa yanda take ta harkar gabanta a gidan kamar warce tayi wata da watanni ke kuma kina nan xaune kina ta wani
kishi da damuwa, wllh tuwo da lafiyayyen miyan agushi tayi ynxu a kitchen, makauniyar kuwa na can ta kafa mata kujera a kitchen din tana xaune….”
Mumy ta fashe da kukan takaici tace “Wllh Salima har ynxu na kasa yrda cewar kishiya barrister yyi min, gani nake kamar bakuwa nayi xata wuce, baki
ji ynda xuciya ta ke min xafi ba, Kuma fa tun jiyan ko lekowa dakin nan bai yi ba, ita kuwa ta shiga bangarensa ina lura yau yafi a kirga, wllh ji
nake kamar in banka ma gidan nan wuta kowa ya huta” Salima tace “Ba wani banka wuta Yaya, gashi kin fara bata chance ta kwace maki miji ta xama ita
ce kan komai a gidan….” Mumy tace “Duk ba wannan ba nata bai tsaya min kamar yanda na makauniyar ya tsaya min a rai ba, ki bani shawara ta ina
xan fara, me kike ga xan ma wnn yarinyar in huce takaici, ni dai baxan kasheta ba amma ina son abinda xan mata kissa ya fi mata alkhairi da shi,
wllh na tsaneta, na tsani duk wani me son ya ganta kusa da shi ma, wllh sai na tarwatsa rayuwarta” Salima tayi dariya tace “Ni fa ban wani jin
yarinyar nan Yaya, minti nawa ne xa a kada ta ta bar gidan ma gaba daya, ita dai wnn yar bokon ya kamata ki fara tunanin ynda xa ayi da ita ba yar
yarinya ba” Mumy tace “To ni ta yarinyar nake tukun” Salima ta mike tace “Toh ki kwantar da hankalin ki Yaya, wnn me sauki ne, mu da muka san kan
komai, yanxu dai ana jirana tun daxu a waje, xan dawo ko xuwa jibi” Mumy tace “Ba wani nan, ke din ce xan gani kwana kusa, idan kika tafi gantalin
ki ba sai an gan ki ba” Salima tayi dariya tace “Ai ynxu na daina kwana a waje….” Mumy tace “Toh ni dai gobe xan taho gida kar ki fita don Allah”
Salima tace “In sha Allah yaya, sai mun hadu goben” Daga haka ta fice daga dakin….. Bakin gate Salima ta kusa cin karo da Junaid xai shiga cikin
compound din, ja baya tayi tana kallonsa, yace “Sorry” bata iya ta amsa ba har dai ya wuce ta, ta juya ta bi shi da kallo ko kiftawa babu,
underneath her breath tace “Waow….” Tana tsaye tana kallonsa har ya isa entrance din shiga main parlor, ya kwankwasa kofar, Mami da ta san yana
hanya ta fito daga kitchen ta bude kofar tana kallonsa tace “Har ka iso?” Yace “Ehh ina yini Mami” ta basa hanya tace “Lafiya lau” daga haka ta
koma cikin parlon ya bi bayanta, saman kujera ya xauna tace “Ya su Uncle din naka” yace “Alhmdllh…” Kitchen ta nufa tace “I have been waiting for
you since xaka dauko min sako a gida” Kafin ta shiga kitchen yace “Mami ina…” Mami ta juyo jin yyi shiru, tace “Wa?” Yace “Wannan babyn” dariya
tayi tace “Sunanta Heedayah” yace “Oh ohk, Heedayah” Mami tace “Tana can tana bacci, let me get you water” Drink ta kawo masa parlon, duk suka
kalli direction din da suka ji footstep, Mumy ce ta fito rike da makullin motarta fuskarta a murtuke, Mami ta nufi bangarenta don tado Heedayah,
Junaid yyi kasa da kai cike da ladabi ya gaida Mumy, kallonsa ta kara yi snn ta amsa a dakile tayi ficewarta xuwa gidan Hajiya Sadiya ta ji ita
kuma nata shawaran. Ba a dau lkci ba Mami ta fito rike da Heedayah dake sanye da doguwar riga iya gwiwa, duk gashin kanta a bude, kana ganinta
kasan daga bacci ta tashi, Mami ta xaunar da ita nan kusa da shi tace “Ga Yaya ki gaishesa” daga haka ta koma kitchen don karasa abinda take, hannu
Heedayah ta kai a hankali tana ta6a sa, har ta kai hannunta fuskarsa, ya kama hannun yana kallonta yace “Ina maki wasa ne?” Turo baki tayi tace
“Nasan kai ne ai” hancinta ya ja yace “Sai na…..” Ganin ynda ta 6ata fuska xata yi kuka ya jawota kusa da shi yace “Ohk sorry, let me pour you
juice, xa ki sha?” Ta turo baki sai kuma ta gyada masa kai, ya bude drink din da Mami ta kawo masa ya diba, tace “Baka kawo Farida ba?” Bai ce
komai ba ya kai glass din bakinta yace “Bude bakin” bude bakin tayi ya fara bata juice din a hankali, Mami ta fito kitchen din tana kallonsu tace
“Da baka bata ba, bbu wani abincin da take ci sai kayan xaki” Heedayah na jin haka ta karasa shanye lemon da saurinta, murmushi yyi ya ajiye cup
din, Mami tace “System dina xaka dauko min a gida yanxu” Junaid yace “Ohk…” Heedayah tana ta6a sa tace “Xaka je da ni??”