HEEDAYAH 16

16
Mikewa Junaid yyi ya da makullin sa yace “Sai na dawo Mami” Mami tace “Alright” a hankali Heedayah tace “Mami ki ce in rakasa plss” Mami ta kalleta sannan tace “Ki rakasa ina?” Tace “Inda xai tafi” Shi dai Junaid bai ce komai ba ya nufi kofa har xai fita sai kuma ya juyo yace “Mu je da ita
Mami?” Mami ta hade rai tace “Ku je da ita ina” Yace “A’a na ji tace xata je ne” Mami tace “To baxa ta je ba, kayi wucewar ka malam” Heedayah ta tashi tsaye kamar xata yi kuka tace “Mami nooo, pls ina son in je, I want to meet with farida, ki ce in bi sa” Mami ta kamo hannunta tace “Farida na Abuja Heedayah, she is not back yet, idan ta dawo you will see her” Shiru Heedayah tayi kamar xata yi kuka, Mami ta kalli kofa ta ga har Junaid ya fita, bangarenta ta tafi ta dauko ma Heedayah hularta da takalmi sannan ta dawo ta sa mata, ta kama hannunta suka nufi kofa, Mami na kallon Mai gadi tace ya leka yace ma wanda ya fita yanxu ya tsaya, hakan Mai gadin yyi, Heedayah ta ji dadi jin fresh air ta gane sun fito waje, sai da suka kusa gate Heedayah tace “Mami kin san me?” Mami ta kalleta tace “Aa my dear, what?” tace “Ina jin kamshin ruwa….” Da mamaki Mami tace “Kamshin ruwa ku ma daughter?” Heedayah tace “Ehh” Mami tayi yar dariya ta leka gate, ganin Junaid tsaye jikin motarsa tace “To ga ta ku tafi amma kar ku dade plss ka ga yamma yyi” ya karaso ya kama hannunta yace “Toh Mami” daga haka ya wuce mota da ita, Mami na tsaye har taga ya nufi mota da ita sannan ta koma ciki, front seat junaid ya bude, kawai ya ga ta fara kokarin shiga, ya dagata ya sa ta cikin motar ya rufe sannan ya xaga ya shiga maxaunin driver ya tada motar suka bar layin. Heedayah ta juya Inda take tunanin yake tace “Ya sunan ka? Sai in dinga kiran ka” Bai kalleta ba idonsa na kan titi yace “Ke ya sunan ki” Tace “Sunana Heedayah Ahmad….” Yace “Heedayah is not a real name” Ta wara ido tace “Ohk, Ammina tace min sunana Fatima” Sai a sannan ya kalleta, ya dai ci gaba da tukin da yake, tace “To ka gaya min naka sunan” Yace “Sunana Fatima nima” ta xaro ido kamar tana ganinsa tace “To ai kai ba na mace bane” yace “To ni na menene?” Tace “Kai namiji ne mana” Ya d’an yi murmushi yace “Ya aka yi kika sa ni namiji ne? ni ma mace ne kamar ki” Ta kyalkyale da dariya har da kyakyatawa, juyawa yyi da sauri yana kallonta, murmushi kawai yake ya ci gaba da tukinsa, tayi dariyarta mai isarta sannan tace “Toh ai naji muryarka kato ne, ba irin na mata ba, kuma…..” Matsawa tayi kusa da shi ta fara tattaba sa tun daga saman kansa, Bai san sanda ya samu waje yyi parking ba da sauri yana kallonta, ta sakko da hannunta har fuskarsa ta fara jan dogon hancinsa sannan ta shafa beard dinsa ta sakko da hannunta har chest dinsa, dariya ta kyalkyale da tace “Namiji ne wllh” kasa daina kallonta yyi, can yayi murmushinsa me kyau yace “How did you know?” Tace “Gashi naji gashin kan ka d’an kadan ne ba irin nawa ba, kuma kana da beard a fuskar ka, kuma you don’t have breast” He couldn’t help it but laugh out loud jin maganar ta na karshe, ita ma ta fashe da dariya tana taya sa, sosai Heedayah ta basa dariya, lkci daya ya daina dariyan yana kallonta yace “To ai ke ma baki da shi balle ni” ta tsuke fuska tace “Teacher na tace grown up people ne kawai suke da breast ni yar yarinya ce ai” Murmushi yyi yace “Ashe kema namiji ne kamar ni” Lkci daya ta 6ata fuska tace “Ni ba namiji bane, ni na mace ne…” tana fadin haka ta cire hularta dogon gashinta ya xubo kasa tace “Ka kalla ka ga” Ya fi second ashirin yana kallon gashin nata sannan ya motarsa after watching and making sure there is no car coming, sai da ya d’an yi nisa yace “Ke ma dai namiji ne bbu ruwana da gashin ki” rungume hannunta tayi ta jingina da motar ta ki cewa komai wai tayi fushi, bai kuma ce mata komai ba har suka isa gida, Mai gadi ya bude masa gate ya shiga yyi parking, fitowa yyi ya xaga ya bude side dinta yace “To na ji ke mace ce, sakko” ta turo baki xata sakko ya dagata ya fito da ita, tace “It is going to rain” kallon sky yyi yace “How did you know?” Tace “Ina jin kamshi” ya kalleta da kyau ya sake kallon sama, da hadari amma ba sosai ba, ya kama hannunta suka nufi cikin gidan, tare ya tafi dakin Mami da ita ya dau system din ya kamo hannunta suka fita, tana bin sa a hankali tace “I want to take tea” Yace “Me yasa baki gaya ma Mami a can gida ba” tace “Tace baxata sake bani tea ba” downstairs ya sakko da ita ya xaunar da ita saman kujera yace “Wait for me” ya ajiye system din hannunsa ya wuce kitchen ya kunna gas ya sa mata ruwan tea, Yana tsaye kitchen din yana jiran ruwan shayin ya tafasa aka fara iska sosai, muryar Heedayah ya ji with all her strength tace “Where are youuu” ya kashe gas din ya fito, tsaye ya ganta duk a tsorace, ya karasa inda take yace “I’m here” ta kamo hannunsa tace “Kar ka bar ni, ina jin tsoro” tana rike da shi ya tafi ya kulle duk windows din gidan har upstairs, lkci daya aka fara ruwa sosai, ya duka dai dai fuskarta jin kamar magana take yi yace “What?” Tace “I told you I smelt rain” d’an murmushi kawai yyi yana tunanin baiwa ne kilan nata, downstairs suka koma ya xaunar da ita saman kujera yace “Let me make the tea for you” da sauri tace “Noo, kar ka bar ni, ka tafi da ni plss” tare ya koma kitchen din da ita, tana makale jikinsa har ya hada mata shayin sannan suka dawo parlor, ya ajiye shayin saman center table yace “Ki jira ya huce” bata yarda ta xauna ba sai da ta tabbatar kusa da shi ne, ta jinginar da kanta shoulder dinsa tayi shiru, ya dau wayarsa ya haske fitila don tuni aka dauke wuta da ake iska, missed calls na Mami ya gani guda hudu, yayi dialing number ya kai kunne, yana fara ring ta dauka, a fusace tace “Junaid da ku ke tafiya baka ga hadari bane, me yasa baka dawo min da yarinyar ba??” Yace “Mami ni ban lura ba sai da muka iso nan gida” Mami tace “Where is she now?” Ya haska fuskar Heedayah ya ga idonta a lumshe, ya mayar da wayar kunnensa yace “She’s sleeping” Mami tace “I don’t care ko kana tuki cikin ruwa ko baka yi, just in the next 20 mins ina son ka dawo min da ita, I don’t want to call you back after this” daga haka ta katse wayarta, kallon Heedayah ya sake yi xai kwantar da ita ya duba karfin ruwan da ake a waje ta bude ido da sauri ta rikesa cikin muryar kuka tace “Noo where are you going” yace “Ba Inda xanje kiyi baccin ki” kin sakesa tayi, ya koma ya xauna, ta kwanta jikinsa, Yana ta xaune parlon ita kuma tana ta bacci, har kusan karfe shidda, har sannan kuma ruwan ko raguwa bai yi ba sai ma karuwa, idan akwai abinda bai iya ba a rayuwa to driving ne cikin ruwa, sarai kuma Mami ta san hakan, duk motsin da xai yi Heedayah sai ta kara makale masa, bayan wani lkci ya haska fitilar wayarsa a fuskarta yaga fararen idonta a bude, duk tunaninsa bacci take, yace “Kin tashi?” A hankali tace “Idan nayi bacci xaka wuce ka bar ni ni kadai” Ya kwantar da ita jikinsa sosai yace “Noo baxan tafi in bar ki ba yi baccin ki” sai bayan Magrib ruwan ya tsagaita yana son yaje yyi sllh Heedayah ta ki sake sa duk da har sannan bata koma bacci ba, haka ya wuce dakinsa da ita yyi alwalan a can sannan yayi sllh suka fito tare, tace “Where is my tea?” Gaba daya ya manta da shayin dake kan center table, yace “let me make another one, wannan yyi sanyi” cikin few minutes ya hada mata wani shayin amma ba mai xafi ba, suka koma parlon ya xaunar da ita ya kai mata cup din baki, ta rike ta fara sha…. Tana gama shan shayin ya dau makullin motarsa yana rike da ita da system din Mami suka fita gidan, ya kulle gidan sannan ya nufi motarsa, sosai garin yyi sanyi, ya bude front seat ya xaunar da ita bayan ya ajiye system din a baya, ya xaga ya shiga motar suka bar gidan, dai dai kofar gidan Abba yyi parking, nan gabansa ya fara faduwa don yasan Mami won’t take it likely with him this night, ya dai fito ya xaga ya bude ma Heedayah side dinta, ta laluba ta kamo hannunsa kamar xata yi kuka tace “Ina jin sanyi” ya saukar da ita yace “We are home” dai dai bakin gate suka hadu da Shuraim xai fito, Junaid na kallonsa ya sake hannun Heedayah ya basa hannu, Shuraim ya amsa yana kallon Heedayah daga sama har kasa, suka gaisa da Junaid, Shuraim xai fita Junaid yace “Ehm naga it’s late already, pls can you go in with her, ina d’an sauri ne” Shuraim ya sake kallon Heedayah sannan ya kalli Junaid yace “Alright” Junaid yace “Thanks” daga haka yyi patting kan Heedayah ya sa hannunta cikin na shuraim yace “Ki gaida Mami, xan kawo mata laptop din gobe” juyawa yyi ya fita gate din ya nufi motarsa, Heedayah ta 6ata fuska xata yi kuka jin Junaid ya wuce ya bar ta, Shuraim dake ta tsaye Heedayah na rike da hannunsa gam, ya saci kallon motar Junaid ganin har yyi reverse ya xame hannunsa daga nata yayi wucewarsa masallaci, Heedayah dai na ta tsaye ga sanyi da take ji sosai sai juye juyen idonta take gwanin tausayi, Mai gadi ne ya fito daga dakinsa alamar shi ma xai wuce masallaci don yin Isha ganinta yace “Me kike yi a nan yarinya, ki shiga ciki mana” Cikin rawar murya tace “Bana gani ai” yace “Bakya gani kuma?” Ta gyada masa kai, lkci daya hawaye ya cika idonta, kama hannunta Mai gadin yyi ya fara tafiya xuwa entrance din shiga gidan yaga tana bin sa a hankali, lkci daya jikinsa yyi sanyi, yace “To wa ya ajiye ki bakin kofa?” Tace “Sake ni yyi ya wuce ya bar ni” dai dai kofa suka hadu da Abba, Abba na kallonsu yace “Wa ya dawo da ke Heedayah?” Tace “Ban san sunansa ba” Kama hannunta Abba yyi ya wuce part din Mami da ita, Mami ta mike ganinsu, Bai ce ma Mami komai ba ya sake hannunta ya juya ya fita, kana ganinsa kasan he is angry and don’t want to talk. Mami ta kamo hannun Heedayah tace “Ina Junaid din?” Heedayah tace “Ya wuce” Mami bata ce komai ba ta wuce daki da ita. Sai kusan sha daya na daren Mami ta tafi bangaren Abba bayan Heedayah tayi bacci, xaunawa tayi kusa da kujeran da yake xaune tace “I’m truly sorry barrister, hakan baxai kara faruwa ba in sha Allah, nasan you are not happy” Yace “It’s okay, but pls ki sa ido a kan wnn yarinya fisabilillah, don’t expose her much to anybody, let her be home all through, kin san condition dinta, tana bukatan kulawa sosai Rahinah, ina jin yarinyar nan tamkar jinina bana fatan wani abu ya sameta…..” Mami tace “In sha Allah” yace “Yaushe Farida xata dawo?” Tace “Ranan laraba” yace “Alright, na sa a nema ma Heedayah lesson teacher soon, Shuraim kuma xai dinga mata karatun qur’ani da asuba na gaya masa, so after prayer kar ki bari ta koma bacci….” Mami ta kallesa sai dai bata ce komai ba… Dai dai wnn lokacin kuma Mumy na dakinta ta shige can cikin bathroom tana ta waya kasa kasa, Mumy tace “Kai ni har na gaji da bayani har yanxu baka fahimta ba, ce maka nayi makauniya ce fa yarinyar, kuma dududu Rabi’ah ta ma ta girmeta ina ga, yar yarinya ce fa sosai, bata wuce sha biyu ba ma kila….” Dariya sosai wanda take wayan da yyi yace “Haba Hajiya, to meye kuma xaki daga hankali kan yar yarinya? Ni wllh na xata ma kishiyar ce kike….” A fusace Mumy tace “To kai ina ruwanka? ba dai kudin ka kawai ka sani ba, ni fa na riga da na gama magana da kusan mutane uku, kawai raba kafa nake ta yi ta ko ina shi sa na kira ka ba wai wani abu ba don kai ka fiye shiririta, ina ruwanka da kankantan yarinyar?? kaga…. idan har ka shirya kaga xaka iya sai ka kirani gobe da safe ni kwanciya xan je inyi…” Tana kai wa nan ta kashe wayar ta fice daga bandakin ta kwanta kan gadonta tana fata ta samu bacci ko xata ji saukin xafin da ranta ke mata, rabonta da baccin kirki tun ranan da ta dawo kaduna. Da asuba Shuraim na dawowa masallaci ya shiga parlon Abbansa don gaishesa don kusan tare suka dawo masallacin, Abba dake hada wasu files ya amsa ba tare da ya kallesa ba yace “Yau xa ku fara karatun da Heedayah koh?” Shiru Shuraim yyi da farko, yana mamakin why all of a sudden Abba xai fi karkata hankalinsa gaba daya kan makauniyar nan, Bai ma ce suyi har da su Rabi’ah ba wai Heedayah, jin shiru Abba ya juya ya kallesa, Shuraim yace “Sure in sha Allah” Abba yace “Good, a can parlon Aunt dinka xaku dinga yin karatun” shiru ya kuma yi na kusan second goma sannan yace “I prefer mu yi a inda nake yi ma su Rabi’ah” Abba yace “Ina kenan?” Yyi kasa da kai yace “Balcony” Abba yace “Noo, akwai sanyi waje, you look for another alternative” mikewa Shuraim yyi ya nufi kofa ya fita, gaba daya ji yyi ya kara tsanar Heedayah har ransa, WTF, ba don he can’t look into his father’s eyes and tell him baxai yi ba da bbu abinda xai hanasa yin hakan, ya fi minti biyar tsaye a parlor kafin ya nufi part din Mami ya tsaya ya kwankwasa kofar fuskarsa daure.