MAKAUNIYAR KADDARA 47

itama ganinsa tayi.

     Bata samu zama da mahaifiyartaba sai dare bayan yaran sunyi barci, 

kasancewar ɗakin mmn sadiq ɗin zata kwana suka sami damar yin hira, 

yayinda mmn sadiq ketama ƴar tata nasiha a kaikaice akan aure da 

muhimmancinsa da darajojinsa. Ita dai Zinneerah saurarenta kawai takeyi 

bawai fahimtar dalilin yinsuba. Sai dai suna shiga kwakwalwarta tana 

kuma ƙoƙarin adanawa da fatan yin aiki dasu a duk sanda ƙaddara ta 

tilasta mata yin aure dan bata kawosa a lissafinta sam. ita kullum 

lissafi da budget ɗinta akan karatune mai zurfi kawai.

     Washe gari ma bayan tafiyar su Abdul skull sake zaman hira tayi da 

mamanta. A yau ɗinma hirar ta kasance kusan duk nasiha da dabarun zaman 

gidan aure koda da kishiya. Harma dai takai abin ya fara bama Zinneerah 

mamaki amma saita danne a ranta kawai.

     Karfe huɗu dai-dai sai ga Ni’ima da driver sunzo ɗaukarta, jitai 

kamar ta fasa kuka. Amma jin mmn sadiq tace zasuje taron biki Danya kuma 

harda ita nanda kwanaki tara yasa taɗanji daɗi a ranta har fuskarta ta 

nuna. Bayan ta gama matse-matsen hawayenta ta shirya suka wuce ɗauke da 

madaidaicin botikin gullisuwa da mmn sadiq ɗin tai musu.

          Koda suka iso gidan cike da murna suka tari juna dasu Bahijja 

daketa mata ƙorafin basusan zataje wajen mama ba da sun bita. dan sai da 

su Mommy suka dawo suka sani. Haƙuri ta basu kawai, daga haka suka shiga 

hidimar cin gwullisuwa kuma.

         Ana idar da sallar magrib hajiya iya tai baƙuwa. Bayan sun 

shiga ɗaki kusan awa ɗaya aka kira Zinneerah, kai tsaye hajiya iya tace 

mata ta shirya zasu tafi da baƙuwar gidanta. Mamaki ya kama Zinneerah, 

amma ganin yanda hajiya iya ta fiske dole itama ta shanye mamakin nata.

     Bayan ta shirya Hajiya iya ta jata gefe tai mata ƴar nasiha da 

gargaɗin duk abinda akai mata a inda zataje kartai jayayya, karkuma tai 

wasa wajen koyon komai ɗin. Ta amsama hajiya iya da girmamawa ita dai 

tana matsar ƙwalla, dan hankalinta ya tashi jin wai sati ɗaya zatai 

acan, a hakanma hajiya fadi take waje ya ƙure ba haka tasoba.

      Zinneerah naji na gani ta tafi tabar su Meenal tana hawaye suma 

sunayi tamkar masu rabuwa har abada. Hajiya iya kanta sai da taji 

kewarta, to amma wannan shine kawai gatan da zatai mata ta miƙata wajen 

kwararrun mata ta fannin sanin gyaran jiki da wasu sirrika irin su 

hajiya Falmata su gyara mata ƴar jikallen tata. Dan idan tai dubi da 

abinda ya faru da kuma kishiya irin Farah saita ƙara jin wannan shine 

gatan.

      Koda suka iso gidan hajiya falmata bata tsaya sanyaba saboda 

gargaɗi da sharuɗɗan hajiya iya akan irin salon gyaran da take buƙata 

aima Zinneerah ɗin, itako hajiya falmata dama aikinta kawai ta sani 

batasan wasaba. Musamman ma aiki irin wannan na manyan mutane kamar su 

hajiya iya da suke alaƙa tun zamanin ƙuruciya ba abinda zatai sanya 

bane. Dan haka tun a ranar ta fara gyara Zinneerah daga isowarsu gidan 

ko hutawa batama bari sunyi zaman yiba. Tun Zinneerah na kallon abin 

wani iri hardai ta fara jin yana shiga jikinta da sha’awarsa ganin yanda 

ta fara canjawa da ƙamshi mai kama jiki da gogewar fata a cikin kwana 

biyu.

       Babu abinda ke damunta sai kewarsu Jamal da hajiya iya dan ko 

abinci da ake bata na musamman ne. Hajiya Falmata kuwa nata aikinta da 

koya mata abubuwa kai tsaye har kunya na neman kashe Zinneerah da ganin 

hajiya falmata zata iskantar da ita shekarunta basu kai ba. A ranta kuma 

tana mamaki yanda ake mata magana mai kama da harshen damo akan aure da 

zamantakewarsa. Ta rasa wannan dalili itakam, takumayi alwashin bazata 

tambayaba zata cigaba dabi da ido da kuma saurare.

      A Ɓangaren su Hajiya iya kuwa Zinneerah na barin gidan aka ware 

fara tsare-tsaren biki da maganar invitations dan hajiya iya da Baffah 

fa shiri suke gagarumi kodan ƙular dasu Mammah dake can hotel suna jiran 

tsammani daga mai bincike, AK kuwa daketa ƙoƙari akan aikin shinkafarsa 

yana sane dasu, dan tuni yasa aka bincika masa inda suke, ya kuma shirya 

ɗaukar mataki akan Farah data bijirema maganarsa. 

     Akan gyaran gidansa kuwa Dr Mahmud da Huzaifa ne tsaye akai duk da 

gidan bama taɓa zamansa Farah tayiba. Garamashi yankan zauna lokacin da 

yake shigowa ƙasar a munafunce.

     Ranar da Zinneerah ta cika kwanaki huɗu wajen Hajiya falmata lefen 

da Momie ta haɗa gudunmawarta ya iso, sai kuma ga Adilah da Mahma daga 

london suma sun iso da nasu kayan lefen, dan AK na sanar da ita komai 

bai ɓoyeba, takuma bashi goyon baya ɗari bisa ɗari. 

     Zokaga yanda Adilah ke murna da farin cikin kasancewarta cikin ƴan 

uwa. mahma kuwa abinci kawai taci anan taɗan huta ta nema inda su Mammah 

suke, dan bata son ita kanta su san da maganar auren har sai ranar 

tariyar insha ALLAHU…………..✍

[ad_2]

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button