SAMEEHA Q

_????SÂMÊÊHÂ????_*
(Q)
A guje momy tayi kan zee dai dai lokacin sameer ya shigo ɗakin aruɗe ya furta,”Lafiy momy me ke faruwa,ya tambaya yana mai ƙarasawa in da zee ke kwance baje baje tana ihu momy ta amsa masa da.
“Ina fa lafiya Sameeha ta rufe zee da dukka ta ko ina kamar zata kashe ta tsabar kishi da baƙar zuciya irin ta sameeha tashi maza muje asibiti zainab a duba min ke kar taji miki ciwo a ƙafa ta cuce mu wai ma me ya kai ki kai mata duka da ƙafa ai da marin ta kika yi ko ki ɗauki madoki ki mammakawa shegiya a jika da yafi ko gaba karki kuma haɗa jiki da ita bamu san dame tazo gidin ba.
zee ta saka kuka tana”
“bazan iya tashi ba momy ƙafa ta zafi take mini tana ciwo kamar zata cire ku kai ni asibiti momy kar na mutu.
“insha Allahu bazaki mutu ba zee yanzu zamu tafi kinji yi shiru ƙafar zata dena ciwo ni ban san tsautsayin daya aike ki dukan ta da ƙafa ba wallahi duk na ruɗi hankalina ya tashi kaga ko Sameer.
miƙewa Sameer yayi daga duƙen da yayi ya fara zare belt ɗin wandonsa yana huci kamar wani zaki ya nufi inda Sameeha ke tsaye tana ƙoƙarin ja da baya,hannu sameer ya ɗaga da belt ɗin ya shiga dukan sameeha ta ko’ina tana ihu da karajin kiran momy ta taimaka mata amma momy tayi burus da Sameeha sai ma wani kallo data bita dashi Sameer na kuma dukkan ta momy ta kama zee zasu fita sai cewa ta yi da Sameer””
“zane ta da kyau kaci ubanta ƙafar da cikin zaka fi dukka tunda ba mutunci ne da ita ba wallahi duk abinda yasami ƴata bazan barki ba sameeha sai na ɗai ɗai ta ki nasa kin shiga wahala da dana sani arayuwarki har ki mutu,momy ta ƙarasa bakin ƙofar falon ta shiga kwarawa jalolo kira da ƙarfi da sauri jalolo ya fito gaba ɗaya hankalin sa ya kasu gida biyu da kiran momy zai ji ko da ihun dake fitowa daga cikin falo jalolo yayi ƙofar falon zai faɗa kenan momy ta daka masa tsawa da ya dawo baya yaje maza ya ɗauko mota su tafi asibiti,cikin sauri jalolo ya juya ya nufi inda motocin gidan suke a guje ya ɗauko ɗaya daga ciki yazo ya tsaya momy ta kama zee suka nufi motar kai tsaye,mazaunin baya momy ta shiga ta tura zee chan ƙarshen kujera tace da jalolo yaja mota su tafi da sauri kar ya bi inda zasuyi tsaye tsaye,jalolo ya amsa da ‘to hajiya,ya ɗauki hanya momy na daga mota tana jiyo ihun sameeha da ƙarar belt ɗin da Sameer ke dukan ta dashi har suka fita daga cikin gidan.
tsaye baba me gadi yayi yana kolon ɓangaran momy da ihun sameeha ke fitowa ya rasa me zai yi ya koma jikin bango ya jingina yana jiran ko me zai fito daga ɓangaran.
jina jina sameer yayiwa sameeha ko motsin kirkir sameeha kasawa ta yi sameer ya yarda belt ɗin hannun sa ganin irin laushin da sameeha tayi ya janyo ta a ƙasa har ɓangaranta ya tura ta ciki yasa key ya ƙule ya koma ɓangaran momy ya chanja kayan jikinsa ya fito ya bi bayan su momy asibitin da suka je kasan cewar momy ta kirashi ta sanar dashi asbitin da suka tafi duk baba me gadi na tsaye yana kalon ikon Allah har sameer yabar gidan.
Duk wani gwaji da dube dube likitan ya gabatar akan ƙafar zee sakamako ɗaya yake bashi babu abinda ya samu ƙafar garau ƙafa take zee kuwa sai ihu take tana wayo Allah ƙafarta zata ciri hankalin momy yayi mugun tashi tace da likita su dai kuma dubawa da kyau sugani.
har ɗakin gwajin aka kuma shiga da momy da Sameer aka gwada amma sakamako ɗayan nan yake bayarwa likitan da kansa ya ce su koma gida suyi na hausa ko kuma su gwada wani asibitin su gani shi dai ga abinda ya ke gani idan yayi gwaji ga kuma alamar wahalar da zee ke sha kamaninta har sun fara sauyawa hankalinta ya fara barin jikinta tsabar azabar ciwon rana ɗaya,shawara sameer da momy sukayi su tafi wani asibitin kawai a kuma dubawa yanzu haka kayan gwajin na asibitin sun taɓu basa bada ainihin abinda ya kamata su bayar,hakan kuwa akayi bayan sameer yabiya kuɗaɗan duk aikin da aka yi wa zee suka ɗauki zee na ihu da sambatun azabar ciwon ƙafa sukayi wani asibitin na kuɗi babba.
An karɓe su da hanzari aka gama cike ciken takardu da biyan komai yanda abin yake a gaggauce akayi da zee ɗakin gwajin ƙashi na ƙafa likitan ya duƙufa akan aikinsa duk wani ƙashin ƙafar zee na saƙo da lungu da sangalalon ƙafar sai da akayi masa hoto na ƙurila amma sakamakon daya fito ƙafar zee garau take babu abinda ya sameta momy kasa jure tsayuwa tayi ta nemi ƙasa ta zauna haɗe da fashewa da kuka mai cin rai ta shiga sambatu tana””
“”Na shiga uku nan ɗin ma ba komai ƴata guda ɗaya tilo Sameer bazan bar duk wanda yake ƙoƙarin nakasa min ita ba na rantse da Allah sai nayi fito na fito da ko waye.
cike da damuwa Sameer ya ce da momy.
“yanzu meye abun yi momy ya zamiyi ga ciwo na damun baby.
*????KAGA SU BABY MANJA IN ZAKA GINA RAMUN MUGUNTA GINA SHI GAJERE GUDUN AFKAWA CIKI SU ZEE AN SHIGA KOMA????♀️*
Banda kuka babu abinda momy take ta kasa cewa da Sameer komai wani haushinsa take ji wai tambayarta yake yi ma meye abun yi,likitocin suka fito da zee duk an ɗaɗɗaure hannayen ta ajikin godon da suka turo ta akai,a fusace momy tayi kansu tana””
“Ku kwance mun ita mahaukaciya ce zaku ɗaɗɗaure mun ƴa ko……..likitan ya dakatar da momy da”hajiya fusge fusge takeyi idan mun bar miki ita a haka ta faɗo daga gadon wani abu ya faru kuma kuce munyi sakaci zaki rufe mu da faɗa nan fa asibiti ne akan aikin mu mukeyin komai.
na rufe ku kazo ka dakeni ƴar tawa ƙwaya ɗaya tal za’ayiwa haka kamar wata dabba wallahi sai Allah ya saka mana.
momy kiyi……..
kar ka faɗa min komai Sameer ban son jin maganarka anan kiyi min shuru,momy ta juya kan likitocin.
ku bamu sallama tunda mun biya ku kuɗaɗan ku.
ko baki faɗa ba yanzu zamu rubuta muku kuma dan Allah hajiya a ringa tawakkali da haƙuri da ƙaddara.
baza ai ba marasa mutunci daɗin abin da kaɗin mu a hannu asibiti tun daga Nigeria har waje zamu iya zuwa ko anini bai ciwan kai daga dukiyar mu ba shashashai kawai.
babu wanda ya tankawa momy cikin likitocin sai ɗaya likitan daya ja hanun sameer suka nufi offc ɗin sa,takardar sallama likitan yabaiwa sameer da wasu ƴan shawarwari sameer ya fito ya sanar da momy ko tata bata furta masa ba suka ɗauki zee suka danna a mota suka nufo gida.
Ko da suka shigo gidan ko tsayar da motar jalolo bai gama yiba momy ta buɗe murfin motar ta fito da gudu gudu tayi ɓangaran Sameeha tana”””
“””””””Fito fito matsiyaciya ƴar matsiyata wallahi sai kin faɗan uban da kika yiwa ƴata kika kasara mun ita,dukan ƙofar momy take da ƙarfi bata lura da mukuli dayake a jikin ƙofar ba tsabar bala’i na cinta sai da Sameer ya……………
*Akafta Comments fan’a????*
_*By*_
_*Maman Dr*_