SULTAN 15-16

Ina nan zaune kamar gunki mamakin mugun sauyinsa duk ya cikani ya haye gado ya kwanta, sai nai kamar an dasani zuciyata duk babu daɗi, jiki a mace na tashi na koma nawa ɗakin, duk yadda na so na rintsa abun gagara ya yi, duk tunanin me na aikata masa da zafi haka ya hana min sukuni. Washegari ko da na tashi da wuri na kammala girki na kai mai ruwan wanka, zaune na tadda shi jikin gado idanunsa a lumshe
“Ga ruwan wanka” na ce ina kallonsa, tashi ya yi ya shiga bathroom ɗin ba tare da ya tankani ba, ko kafin ya fito na shirya masa abinci, shiryawa ya yi cikin wani coffee and black soft clothes wanda suka yi mai matuƙar kyau, ina ta satar kallonsa don gani nake kamar an canza min shi, zama ya yi hakan ya sa na zauna a gefensa na zuba mai abinci, bai yi alamun ci ba hakan ya sa na ɗebo na kai bakinsa, mugun kallon da ya yi min ne ya sa na sauke jikina ya ɗauki rawa, a hankali na ce ” me na yi maka ne?”
Ɗago dara-daran idanunsa ya yi ya sauke a kaina sai ya taɓe baki tare da ƙoƙarin miƙewa, duk yadda na so na jure sai na kasa kawai na fashe da kuka, a hankali ya dawo tare da tsugunnawa ya ɗago haɓata ya tsurawa fuskata ido da hawaye ke ta faman bi, ido cikin ido muke kallon juna yayin da hawayena ke ta zaryarsu, hannunsa ya sa ya shiga share min. A hankali na ce “me na yi maka?”
Lumshe idanunsa ya yi tare da waresu a kaina sai ya ɗan langaɓar da kansa tare da kama hannuna ya shiga musu wani irin murzawa, sosai na fara fita daga hayyacina don ji nake wani masifaffen yanayi na saukar min, cikin kasala na kallesa na ce “me ya sa kake fushi?”
Bakina ya tsurawa ido tamkar yana kallon majigi, ban yi aune ba na ji saukar tattausan lips ɗinsa saman nawa, a hankali ya shiga tsotsa tamkar ya samu sweet kafin ya janye don kansa, idanunsa sun ɗan canza yanayi sun cika da sha’awa ya kalleni, sai kuma ya ɗauke kai gami da tashi, wani irin shock da ya kamani har ya koma gado bai sakeni ba, na yi kiss har ban san adadinsu ba, but na shi is so special duk jikina ya mutu and I’m hoping for more, sosai kiss ɗin nasa ya shigeni ya karya duk wani kuzari na jikina, zuciyata ce ta shiga ingizani na…
*INA GAF DA RUFE FREE PAGE, LET’S WALK THROUGH THIS JOURNEY TOGETHER, DON ALLAH KAR KU BARI WANNAN LAGWADAR LABARIN MAI CIKE DA ZAZZAFAR SOYAYYA MAI TSUMA ZUKATA DA SANYA NISHAƊI HAKA DA ZALLAR… YA WUCE KU, KI YI SUBSCRIBING DAIDAI ƘARFINKI*
*????FITATTU HUƊU????*
*????SULTAAN* # Nml grp ~N~ 300 vip ~N~ 500 via 1401611541 Access bank, shaidar biyanki ta wannan numbern 08167888934
*Mss Flower????*
TSINTACCIYA
Nimcyluv
Baƙar fata
Autar manya
DATTIJON ARZIƘI
Real ladingo
Gaba ɗaya 800
Via 6850917335 Na’ima Shu’aibu Sulaiman Fidelity Bank, masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 za ku tuntuɓa. To show evidence of payment 08142105218
*Mss Flower???? 08167888934* For more information????
[ad_2]