TAKUN SAAKA 14

Hajiya mama ta hana ai masa gyaran karayar wai sunada mai gyaran gargajiya zaizo da ga kauye. Sai a jirasa yana hanyar tahowa. Tun yamma ake jiran mai gyara har dare ya tsala bai iso ba. Haushin abinda Hajiya mama tai musu su kuma likitocin sunce bazasu taɓa ƙafar ba har sai wanda tace ɗin yazo ya gyara masan. Duk roƙon da Momy taita musu sunce bazasuyiba wlhy.
*_WASHE GARI_*
Da safe acikin su Yaya Abubakar babu wanda yabi takan zancen duba wani Abba. Da dai su Ammar suka kammala yin breakfast suka gyara gida sai suka runguɗa asibiti wajen mahaifiyarsu. Sun isketa zaune Hibbah na shafa mata mai saboda wanka da tayo.
Ta dubesu cike da tausayi da begen ƙishirwar murmushinsu. Duk wanda ya gaidata sai ta kamo hannunsa ta shafa kansa tana ƙoƙarin haɗiye hawayenta.
“Ku daina fushi da Umminku kunji”.
Ta faɗa cikin damuwa da ƙunar da takeji a cikin zuciyarta. Komai basu iya cewa ba sai dai dukansu sunyi ƙasa da kawuna ransu fal tausayinta. Musamman Yaya Muhammad da yasan wani yanki na labarinta batare da itama ta sani ba, shima Abbansu ne ya sanar masa kafin ya rasu. Ya kuma tabbatar masa ya faɗa masane saboda wataran yasan kunnensa zaiji gorin da za’aima mahaifiyarsa kar zuciyarsa ta ɗauki wani abun daban. Shine ya fara jan numfashi da ƙyar da dubanta yana ƙoƙari haɗiye hawayen da suka ciko masa ido.
“Ummi baki mana laifin komai ba. Amma dan ALLAH a wanan gaɓar munason jin wani abu game da ke. badan bamu yarda dake bane. Sai don son sanin minene dalilin da yasa duk basa ƙaunarki?. Mi kikayi musu haka da zafi? Miyasa kika yarda kika auresa bayan shiɗin kanin Abbanmu ne? Mai fuska biyu ga mutane”.
Murmushi ta saki mai kuna da kai hannu ta shafo kan Yaya Muhammad. “Muhammadu Aminullahi zan faɗa muku insha ALLAH. Da zaran munje gida yau zakuji komai”.
A take fuskokinsu suka nuna jin daɗin zancenta. Dan danan suka ɓalle mata hira kamar yanda suka saba a baya. Itako sai murmushi take zuciyarya na kara sanyaya da ɗunbin sonsu da kaunarsu.
Dr bilal ne ya shigo, bayan sun gaisa yace suje waje zasu ɗan ƙara duba Ummin suga ya ya komai na tafiya normal. Sun masa godiya tare da fitowa su duka. Duk anan ƙofar ɗakin suke zaune Hibbah nacin abincin da sukazo da shi. Kamar ance ta ɗaga kai sai idanunta karaf akan Zahidah da Hafsat, Muhammad Shuraim biye da su.
Babu shiri ta miƙe zaram tana rarraba idanuwa. Tunkan su ƙaraso tace, “Lallai ma! Miya kawoka nan?”.
Furucin natane yaja hankalin yayun nata gaba ɗaya. A tare suka sauke idanunsu bisa kan Muhammad Shuraim da ke sanye cikin ado da kamshi na shadda da keta maiƙo, ga hular zanna da ya murza wadda ta kara masa cikar kamala da kwar jini.
A fusace Hibba ta sake buɗe baki zatai magana Yaya Umar ya harareta. Dole tai shiru tana wani mar-mar da idanu akaikaice tana ballama Shuraim harara.
Shiko murmushi ya saki yana matuƙar jin mamakin tsaurin ido irin na Hibbah. Ya cigaba da takowa a hankali zuwa gaban su Yaya Muhammad da duk hankalinsu a kansa yake suna kallonsa cike da nazari. Duk da zasu iya yin sa’anni da Yaya Umar cikin girmamawa ya shiga gaishesu su duka. Gashi yaki yarda ya haɗa idanu da su shi a dole yana gaban surukai.
Hakan ba karamin dariya da burgesu yay ba. Ammar sai wani ƙara buɗe ƙwanji ake su a dole yayu. Yaya Muhammad ya ce, “To sai dai bamu gane baƙon namu ba?”.
Murmushi Shuraim yay cike da ladabi yana ɗan shafar ƙeya yace, “Yayanmu bazaka sanni ba. Dama ina jiran lokaci ne nazo gareku. Sai dai jin Momy babu lafiya yasa nazo dubata kafin hakan. Sunana Muhammad Shuraim Aliyu. Mai fata da addu’ar samun nutsatstsiyar yarinya mai tarbiyya kamar Muhibbat….”
Wata malalaciyar harara Hibba ta zuba masa tamkar zata fashe dan takaici da haushinsa. Yayinda Ammar dake guntse dariya a kaikaice yace, “Dama dai a tarbiyyar ka tsaya dana yadda. Amma ba Nutsuw…..”
Gwiwar hannu Yaya Umar dake gefensa yasa ya bugesa. Yay azamar rumtse ido da ɗaura hannunsa a wajen yana faɗin, “Wayyo Ya Umar zaka kashe ni”.
Yaya Abubakar kam murmushi ya sakarma Shuraim shi da Yaya Muhammad. Haka kawai su dai Shuraim ɗin ya birgesu matuƙa. Dan haka Yaya Abubakar yace, “Masha ALLAH mun gode matuƙa. Bara doctor ta fito sai mu shiga ka dubata”.
Sosai daɗi ya kama Shuraim, ya shiga jera musu godiya da addu’ar samun lafiya ga Ummi. Su ma su Zahidah suka shiga gaishesu da tambayar jikin Ummi ɗin. Hibbah kam taƙi kulasu suma wai haushinsu takeji sun faɗama Shuraim sirrinta.
Suma basu kulata ba dan sun gane manufarta sarai. Haka ta ringa antaya musu harara suna ramawa har Doctor ya fito suka shiga su duka.
Tunda suka shigo Ummi take kallon Shuraim da ya durƙusa har ƙasa ya gaisheta da tambayar jikinta. Fahimtar ƙarin bayani take buƙata yasa Ammar fara rattafo zance. Sosai murmushin fuskar Ummi ya sake faɗaɗa. Dan har cikin ranta taji ƙaunar Shuraim da samun nutsuwa da shi. Tana kuma fata da addu’ar ya zame musu mafita akan haɗa Junaid aure da Hibbah da ake ƙoƙarin ƙullawa.
Basu wani jima sosai ba yace zai wuce, bayan ya ajiyema Ummi ledan dubiya. Godiya suka sake masa Ammar ya tafi rakasa. Yana ƙoƙarin ficewa Isma’il ke ƙoƙarin shigowa. Baya ya koma ya bashi hanya. Batare da tunanin komai ba Ammar ya gabatar da Shuraim ga Isma’il ɗin. Shima Shuraim Ammar ya gabatar masa da Isma’il matsayin ɗan uwansu. Hakan ya basu damar yima juna kallon ido ciikin ido. Da alama kallon da Isma’il yayma Shuraim ɗin na tsantsar kishi ne da shima kansa baisan yayi ba. Haka shima Shuraim kallon alamar tambaya da tsoron sakkiyar da babu ruwa yayma Isma’il ɗin kai tsaye. Cike da basarwa kuma sai suka saki hannun juna kowa na ƙoƙarin haɗiye abinda ke ransa da cikin idanunsa, kafin su kalli Hibbah a tare Shuraim ya ida ficewa, Isma’il ya karasa shigowa…………✍
*_Tofa mazaje ya take ne?????????????????, kodai Hibbahr mu ta mutunci ta haɗa karo ne????????????. To muje zuwa muga wane mai rabon zai ɗauka a ciki, dan har yanzu itaɗin allura ce a cikin ruwa mai rabo ka ɗauka. zamuga yaya TAKUN SAƘAAR zai kasance a filin dagar dan ga Junaidu ma bin Halilu a gehe yana jiran waman dakala bati siddan. Ga kuma oga master da tabbas sai ya binciko hibban tunda ya ɗau alwashin hakan????????????._*
_Please kuyi manage da ga nan har Monday na ƙara samun sauƙi????????????_
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*