TAKUN SAAKA 45

Yaya Umar yace, “Auta ajiye wannan labarin naki sai anjima faɗa mana mikike son gaya mana?”.
Kanta ta jinjina masa tana gyara zama, “Wani abu zan sanar muku akan Abba wlhy kuma da gaske nake. Ummi kindai san bana ƙarya, bakuma nayima mutun sharri dan kince ɗan aikene idan ka aika zai dawo kanka komai tsahon shekaru”.
Ummi ta gyaɗa mata kai kawai. Hibba tace, “Yauwa Ummi ranar ɗaurin aure da yaya Muhammad ya sakani fita amsa waya…………”
Wani irin zufa ke ketoma su Ummi a jiki da kiɗima tunda Hibbah ta fara basu labari. A fuskokinsu kawai ya isa ka irga yawan tashin hankalin abinda sukeji. Dan numfashin Ummi har fita yake a sarƙe kamar mai Asthma. Hibbah dake kuka rurus itama zuwa yanzun ta faɗa jikin Ummi tana faɗin, “Ummi na tsaneshi, bana son sa, bana son sake ganinsa a rayuwata har abada. Ummi dan ALLAH karki sake zaman aure da shi, yaya kuma ku daina cemasa Abba shi ba abbanmu bane fasiki ne azzalumi mai aikata saɓon ALLAH batare da yaji kunya ba”.
Cikin rawar murya Ammar yace, “Hibbah kin tabbatar maganar nan taki da gaske kikeyinta?”.
“Wlhy Yaya Ammar da gake nakeyi, kama tambayi Yaya Isma’il yasan komai shima. Nama san zai sanar daku idan ya kammala abinda yake sonyi”.
Innalillahi wa-inna’ilaihirraji’un suketa faman maimaitawa zufa na sake gudu a jikunansu. Yaya Usman mai ragon zuciya kam harya fara kuka dan kallon abin yake tamkar a mafarki ƙanin mahaifinsu da aikata homo duk da kasantuwarsa dattijo a yanzun. Ummi kam a take zazzaɓi mai zafi ya lulluɓeta duk da kuwa akwai wani lokaci kafin rasuwar mahaifin su Hibbah data taɓa zargin Abban da wannan ƙazantar akan abokinsa Alhaji Balele. Sai dai gudun karta aikata zato akan abinda bata da tabbas yasata kauda al’amarin ta nema tsarin ALLAH daga sheɗan. Lallai dolene rashin imaninsa ya sake ƙarfi a zuciyarsa. Dubi da yanda yake mata fyaɗe cike da cin zarafi da tozarci a gareta. Su duka babu wanda baiyi hawaye ba hatta yaya Umar mai ƙarfin zuciya, sai suka godema ALLAH ma da yaya Abubakar baya nan baiji wannan kwamacala ba. A fusace Ammar yace, “Wlhy Ummi sai mun tona musu asiri, dan barin irin waɗan nan shaiɗanun a duniya haɗarine da barazana ga matasa, musamman waɗanda suke a halin rayuwa na rashin aikinyi. Dan da kuɗi ake jan ra’ayinsu a gurɓatasu kamar yanda nake hasashen shi kansa halilun baƙin matsiyaci ya shiga”.
Kai Ummi dake sharar hawaye ta girgiza masa. “Ammar tona masa asirinsa tamkar tona namune. Zai ma iya musawa akan hakan. Idan muka zuba ido ma ALLAH da kansa zai tona asirinsu wa duniya insha ALLAH. Sai dai ban yarda Isma’il yana cikin masu aikata wannan kwamacalarba nima Tanee. Koke kin taɓa ganin wata alamar hakan tattare da shi?”.
Kai Hibbah ta girgiza, dan batason faɗa musu komai da Master ya sanar mata tunda ya gargaɗeta. “Ummi bana tunanin hakan gaskiya, nafi zarigin akwai dalilin da yasa yake tare da su ɗin tamkar yanda ya faɗa…..”
“Ko kuma wancan master ɗin daya ɓoye sukema tunanin shine Yaya Isma’il ba. Anya kuwa Yaya Isma’il ba jami’in tsaro bane ba?”.
Ammar ya faɗa yana duban su Yaya Muhammad.
Yaya Umar yace, “Nima na fara zargin hakan Ammar, tun ma a randa yayma Junaid dukan nan nakeji a jikina jami’in tsarone ɓadda kama kawai yakeyi a cikinsu kamar”.
“Koma dai miye muɗan sauraresa muji daga bakinsa to”. Ummi tai maganar tana share hawayen dake sakko mata na baƙin cikin halin Abba halilu har yanzun. ALLAH sarki Hajiya mama, ta ƙyamaceta akan tazo cikin ƙaddara bada aure a tsakanin iyayenta ba. Yau ga ɗan data haifa nan yana aikata aiki mafi muni da yafi wanda mahaifinta ya aikata wajen samar da ita. Haka rayuwa take, shiyyasa karka ƙyamaci abinda UBANGIJI ya ajiye bisa ALƘALAMIN ƙaddarar faɗakarwa ga wasu mutane. Kai dai kazamto mai faɗar alkairi ko kawai kayi shiru.
Haka suka cigaba da hira gwanin sha’awa. Duk yanda sukasha cikin Hibbah akan jin wani abun mara kyau daga Master taƙi yarda ta faɗa koda da suɓutar baki. Sosai kuma ta birgesu suka sake yarda autarsu ta daɗo hankali kenan.
Addu’a Hibbah ta dingayi kar Master ya dawo yace su koma gida, cikin amincin ALLAH kuwa sai gashi har dare babu shi babu yaya Abubakar. Taji matuƙar daɗi dan yau koba komai a bayan Umminta zata kwana………..✍
[ad_2]