TAKUN SAKA 23

“Dalla malamai karkuyi mana hayaniya anan kuja a samu barcin dole”. Cewar Adam yana harar su Zaidu da suka ƙanƙame ledojin.
Cikin ƴar dariyar shaƙiyanci Musbahu yace, “Wanann kaɗan da ga aikin Master. Balle fa yau ango yake a gidan nan kuna ganin harda kazar tarbar amarya”.
A tare suka wage bakuna zasu ƙyalƙyale da dariya Idris yay musu nuni da sama. Saurin saka hannayensu sukai suka dafe bakunan kowa na ƙoƙarin danne ta shi. Da ga haka suka koma tsakkiyar falon zaune Salis na ƙoƙarin buɗe ledojin dake ɗauke da kwalayen pizza da shawarma.
Sosai suka shiga farin ciki kowa yaja shawarma ɗaya dan dama a lissafe suke. Pizza kuwa kwali huɗu ce itama.
Da ga ɓangaren oga Master kuwa koda ya haura sama a falo ya ajiye ledar ya nufi bedroom ɗinsa. Kusan mintuna goma sha biyar sai gashi ya fito. Ya sake ɗaukar ledar ya nufi ɗakin da ya kai Hibbah ɗazun. A yanda suka barta a haka ya isketa. Ya ajiye ledan a saman mirror fuskarsa na sake tsuƙewa. Ledar da Habib ya ajiye ɗazun ya ɗauka. Ya zaro handkerchief ɗin cikinta yana nufar gadon. Wata ƴar ƙwafa yayi dai-dai yana ranƙwafowa akan Hibbah da batasanma ya nai ba. Kansa tsaye ya ɗora handky ɗin saman hancinta. Tsahon minti ɗaya taja wani irin dogon numfashin da zai iya razanar da mai tsoro. Bai ɗaga handkerchief ɗin ba sai ma sake danna mata shi da yay akan hanci.
Numfashin ta kuma ja da ƙarfi tare da sakin tari lokaci guda. Ya janye hannunsa da jikinsa yana mikewa da ƙyau. Ganin yanda take jujjuya kanta da cigaba da tarin ya sashi ɗaukar goran ruwan da ya ajiye a bedsite tare da ɗora kafarsa ɗaya akan gadon ya sake ranƙwafowa kanta. Murfin gorar ruwan mai ɗan sanyi ya ɓalle ya shiga tsiyaya mata a saitin wuyanta duk da akwai hijjab a jikinta har yanzu dan basu cire mata ba. Yanda yake kwarara ruwanne ya sashi tsalle har saman fuskarta zuwa ƙirjinta da kan gadon.
Tai wata irin zabura da jawo numfashinta da ƙarfi ya iso har cikin hancinta. Duk da wani irin nauyi da jikinta yay mata hakan bai hanata ɗago hannunta ba ta shiga ƙoƙarin sharce ruwan da har yanzu yake kwarara matan.
Ɗayan hannunta ta kai cikin lalube da rashin ƙarfin jikinta da nufin ture ruwan da ke sakko matan. Sai dai hannun nata bai kai ba, sai kafarsa data ɗan shafo kaɗan ta ajiyesa yaraf tana ƙoƙarin son buɗe idanunta da sukai matuƙar nauyi.
Dakatawa yay da tsiyaya mata ruwan jin ta fara magana a fisge. “Y… y… ya… ya… Mu…. ham…. mad… kar… Kar…ku ɗaura zasu kashe ku”. Ta shiga faɗa a rarrabe cikin ƙoƙarin fisgar numfashi da yunƙurin son tashi. Sai dai kuma luuu ta koma yaraf bisa gadon dan sam babu wani ƙarfi tare da ita. Hasalima abin bai gama sakinta ba baki ɗaya.
Fahimtar hakan da yayi ne ya sakashi jan tsaki da cillar da goran ruwan yana sauke kafarsa ya miƙe tsaye sosai. Kallonsa ya kai ga agogon hannunsa yana sake tsuƙe fuska.
Tunanin mi yayi oho masa, sai kawai ya ja bargo aɗan fusace ya lullu ɓa mata, tare da sake ranƙwafowa ya kama hijjab ɗin jikinta yaja da ƙarfi ya farkesa. jansa yay baya ya fita da ga wuyanta. Da ga haka ya ɗauka ledan da ya shigo da ita ya fice ransa fal takaici.
Bedroom ɗinsa ya wuce, duk da yana jiyo hayaniyar yaran nasa da ke cigaba da kallon ball da ciye-ciyen abinda ya kawo musun suna zabga gardamar da sukafi ƙwarewa akai.
★★★★
Su Ummi sun isa katafaren sabon gidan da su Yaya Muhammad sukai matukar ƙoƙari wajen ginasa. Dan babu abinda su Hajiya Mardiyya ke ambato sai masha ALLAH. Ƙwarai da gaske matasan samarin na Ummi sun nuna ƙwazon da za’a yaba musu ƙwarai da gaske. Dan komai yayi cif a talauce ba’a sarauce ba. Sashen Ammar ne kawai ba’a karasa ba daga linta aka barsa.
Kai tsaye sashen Ummi da ke a farko suka shiga. Inda nanma dai su Hajiya Nafisa keta sakama yaran albarka dan komai yayi a asashen tamkar bana dattijuwa Ummi ba. Akwai ɗakin Ammar da na Hibbah a sashen Ummin. Sai bedroom ɗinta dana baƙi guda biyu. Ga babban falukanta biyu da kitchen da dining babba da ke ɗauke da dogon dining table na family baki ɗaya. A kallo ma zaka san sashen Ummin yafi kowanne sashe girma a gidan, sai dai nasu kawai upstairs ne su kuma. Itama kuma catai bataso shiyyasa akai mata nata flat da ya kayatu da zamani.
Suna shirin fara gabatar da salloli dan mazan sun fice sai ga kuloli ana shigowa da su. Cikin mamaki Ummi ke tambayar da ga ina?. Matasan samari biyu da ke shigo da kulolin suka bata amsa kai tsaye da faɗin. Isma’il ne ya turosu.
Rasama mi Ummi zatace akan wannan yaro ɗan albarka tayi, sai kawai ta saki murmushi zuciyarta na ƙara jin matukar ƙaunarsa har cikin jini…………✍
*_Amin afuwa da jina shiru. Ciwo me ya kadani a bazata._*
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????
#team ZAFAFA BIYAR????????????????????
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*
[ad_2]