TAKUN SAKA 27

Cikin takaici Engineer ya karɓe, “Nifa wlhy namafi tsanarsa sama da maƙiyan namu a yanzu. Nakanji kamar na kar shege a wuce wajen tun yanzu”.
“Kulll” Alhajin Mande ya faɗa yana gyara zama. “Kudai mu cigaba da lallaɓashi da haƙuri kuɗaɗen nan da aka tara su dawo hannunmu. Cikin sauƙi zamu sakashi a tarko mu da kammu musa a kamashi, sai mun ƙasƙantar da shi a gaban duniya da kullum burin kowane jami’i ya ga gwiwarsa a ƙasa kafin mu ɗurama shege allurar guba namansa ya zaganye kowa ya huta. Dan ba karamar fitina uwar wannan ta haifama duniya ba”.
“Mu kuma ta haifa mana abinda ya amfanemu ai”. Cewar A.G.
Dariya suka sheƙe da ita baki ɗaya suna tafawa.
★★★★★★
A gidan Ummi kuwa zuwa magrib duk wasu baƙi sun kama gabansu. An kimtsama kowacce amarya sashenta an barta ta jira shigar ango. Sashen Ummi ma dai babu kowa sai ita da samarin ƴaƴanta. Suma ɗin sun fita sallar isha’i basu kai da dawowa ba.
Da Ummi taji motsi sai ta kalla ƙofa da tunanin ganin Hibbah ta shigo. Sai dai shiru kakeji. Harga ALLAH zuwa yanzun zuciyarta a matuƙar raunane take. ji take kamar numfashin Hibbah baya tare da nasu a cikin gidan. Dan babu yanda za’ai Tanee ɗinta ta kwana ta yini batare data sakata a ido ba. Musamman idan ta tuna miya faru akan aurenta.
Kai anya kuwa bata yaudarrar kanta ma. Tayama akai ta amince cewar Hibbah na tare da su Zahidah bayan abin daya faru, dan babu kuma yanda za’ai ace Hibbah bata sani ba. Zaram ta miƙe da ga zaune da take a saman sallaya dan idar da sallarta kenan ta isha’i.
A yanayin kiɗima ta fito falon ƙirjinta da zuciyarta na wani tsitstsinkewa. Gaskiya haƙurinta ya ƙare da kanta zataje sashen su Zahidah ta bincika.
Yanke wannan hukuncin a rantane ya sakata nufar ƙofar falon. A dai-dai nan suma su Yaya Muhammad suka kawo jiki zasu shigo. Baya Ummin tai tana dubansu cikin rauni.
A take suma kuma yanayin nata ya saka gabansu faɗuwa. “Ummi lafiya? Kuwa”.
Yaya Muhammad ya faɗa yana matsowa kusa da ita sosai.
A raunane ta ce, “Muhammad Tanee. Dan ALLAH ku faɗa min gaskiya ina yarinyata take ne? Zuciyata na tabbatar min kuna ɓoyemin wani abu”.
Cikin son kauda mata hankali yaya Umar ya kama hannunta yana faɗin, “Ummi zauna kiji, kwantar da hankalinki indai auta ce tana cikin ƙoshin lafiya.”
“Ban yarda ba Umar, dan zuciyata tana bani numfashin Tanee yana nesa da nawa”.
Cikin in ina Yaya Abubakar ya buɗe baki zai yi magana akai knocking ƙofar.
“Tanee!”
Ummi ta ambata da sauri tana duban ƙofar. Gaba ɗayansu suma ƙofar suka duba, sai dai sanin Hibbah bata tare da su yasa su basuyi wannan zaton ba. Mikewa Ammar da illahirin jikinsa ke tsuma yay ya nufi ƙofar. Batare da tunanin tambayar wanene ba ya buɗe ƙofar da janta baya yana kai kansa zai leƙa aka ɗaura masa bindiga.
“Innalillahi wa-inna’ilaihirraji’un”. Ya ambata yana jan jikinsa baya.
Hakkane kuma ya bama wanda ya ɗaura masa bindigar akai damar sakko ƙafarsa cikin falon. A zabure su Ummi duk suka miƙe saboda jin sallallamin Ammar ɗin. Yayinda idanunsu ya sauka akan bindiga da mai shigowar duk suma sai suka ɗauki ambaton ALLAH.
Mutumin da dukkan illahirin jikinsa ke a rufe ya cigaba da takawa Ammar naja da baya cikin rawar jiki har suka iso tsakkiyar falon. Wani irin kyarma jikin Yaya Abubakar ya shigayi na tsantsar ɓacin rai, ya yunƙura zai nufesu Ummi da jikinta ke karkarwa itama tai saurin damƙe hannunsa tana girgiza kanta.
Idanunsa ya rumtse da ƙarfi cikin tsumar jiki da riƙon da Ummi tai masa a kausashe ya ce, “Who are you?!”.
Shiru bai amsa ma yaya Abubakar ɗin ba, sai hannu da ya kai saman fuskarsa ya janye hiramin da ya naɗe fuskarsa da shi.
Lokaci ɗaya suka zabura a tare, har suna haɗa baki wajen faɗin…………✍
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????
#team ZAFAFA BIYAR????????????????????
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*
[ad_2]