TAKUN SAKA 31

Ta faɗa da sauri kafinma ya rufe baki. Juyawa yay ya karasa ga kujera batare da ya amsa ba. Sai da ya zauna sannan ya ɗago ya dubeta. “Mike damunki?”.
Yay maganar cikin nuna kulawa duk da fuskarsa a tsuke take babu walwala.
“Ba komai”.
Ta bashi amsa hawayen da take maƙalewa suna rige-rigen sakkowa a kumatunta. Idanunsa ya janye a kanta yana ɗan furzar na numfashi. “Ummi ko?”.
Saurin ɗagowa tai ta dubesa. Sai kuma ta fashe masa da kuka tare da durkushewa a inda take. Lip ɗinsa ya ɗan taune da lumshe idanunsa. Sai kuma ya buɗe yana miƙewa. Fridge dake a falon ya nufa. Ya ɗakko gorar ruwa ya dawo inda take durƙushe tana kuka. Mika mata yayi batare da yayi magana ba. Ganin taƙi karɓa ya sashi yin wani ɗan dirƙuso a gabanta. Yatsunsa biyu yasa a kan haɓarta ya ɗago fuskar tata. Babban yatsansa kuma na goge mata hawayen gefe guda yana cigaba da kallon fuskar tata. Ɗayan hannun kuma ya karasa fincike murfin goran ruwan ya kai bakinta. Abinda ya tokare maƙoshinta ne ya sata fara shan ruwan ko zai wuce. Tasha kusan kaso ɗaya bisa uku kafin ta janye kanta. Komai baice mataba ya janye shima tare da mikewa. Ya kai hannu ya kamo nata hanun. Dole ta miƙe tsaye dan kulawar daya batan kawai yasa zuciyarta ɗan yin sanyi taji kamar daya da ga cikin su Yaya Abubakar ne.
A doguwar kujera ya kaita ya zaunar. Hannun nata ya saki ya nufi hanyar bedroom ɗinsa. Hibbah ta bisa da kallo zuciyarta na ayyano mata wata kamanceceniya data rasa a ina take son gano ta. Ta yi zurfi a tunani barci ya fara fisgar jijiyoyin idonta. Duk yanda taso hana kanta hakan ya gagara. Cikin kanƙanin lokaci jikinta duk ya saki, dole ta zame ta kwanta a kujerar batare data shiryama hakan ba.
Duk abinda take yana kallonta ta cikin ƙofa. Yana ganin ta zube kwance ya fito. Wata Wadrobe dake a gefe an shirya littatafai a ciki ya nufa. Key ya ɗauka a kasan wani littafi ya saka jikin kwabar sai ga shi ya buɗe alamar ƙofa. Yasa hannu ya juya katakon ƙofa ta bayyana. Dawowa yay ya leƙa kasa. Ya tabbatar baba saude hankalinta baya a wajen sanann ya ɗauka Hibbah gaba dayanta yabi ta ƙofar da tai ƙasa yabi ta barauniyar hanyar data fiddashi ta backyard ɗin gidan. Da sauri Habib da ke tsaye cikin parking space ya buɗe masa ƙofar motar. A bayan ya sata, shima ya shiga. Habib ya zauna a mazaunin driver suka fice a gidan bayan maigadi ya wangale musu gate………….✍
*_Kuyi haƙuri, yau gaba ɗaya na ɗauka Sunday ce ashe monday muke????????????????????_*
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????
#team ZAFAFA BIYAR????????????????????
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*
[ad_2]