Uncategorized

TAKUN SAKA 39

         A gaggauce yay alwalar ya fito yana duban gadon. “Tashi kiyi salla”. Ya faɗa yana shinfiɗa sallaya ya tada salla. Ganin ya fara sallarne ya sata yunƙurawa ta tashi da ƙyar. Alhmdllh taji matuƙar daɗin jikinta, da alama maganin daya bata na kashe raɗaɗi da zogi ne. Sai dai jitake bakinta babu daɗi. hakama jikinta fayau kamar isaka zata ɗauketa. Sai da ta ɗan samu ta sake shiga ruwan zafi ya ratsata fiyema da ɗazun da taita raki dan batajin dai-dai a wajen har yanzun sannan ta sake samun nutsuwa, tana fitowa ta samu ya idar da sallar, motsinta yasa shi juyowa suka haɗa ido.

        Saurin maida kanta tai ƙasa hawaye na sakko mata. “Dan ALLAH ka cire fuskar nan, ni basai ka suffanta kanka da yaya Isma’il ba zanyi haƙuri har ALLAH ya kuɓutar dani da ga gareka”.

       A yanda tai maganar saita bashi tausayi da dariya. komai baice mata ba ya miƙe, har inda take tsaye yazo ya kama hannunta. Ɗayan hannunsa kuma yasa ya ɗago fuskarta tare da ɗan matso tasa gab har sunajin saukar numfashin juna. “Karki tsananta tunani, duk abinda kike buƙatar fahimta zaki tabbatar da shi nan da kwanaki biyu kacal insha ALLAH. Kiyi sallan ki sake kwanciya ki huta zan fita bazan jimaba, kukan nan kuma ya isa haka ok”. Ya ƙare maganar da sumbatar laɓɓanta.

     Komai ita dai batace ba, sai ma sake rikitata da yay. Shiko ganin yanda time ya ja ya sashi daukar wayarsa da jacket ya daura saman t-shirt ɗin jikinsa da sabon mask ya fita a ɗakin da ɗan hanzari. Takardun da ya bari a falon Habib ya tattare masa lokacin da ya kawo abinci ya ɗiba ya fito cikin zafin naman da ALLAH ya azurtashi da shi. Mota ya buɗe ya zuba kayan hannunsa sannan ya zagaya mazaunin driver. Su Habib da keta aikin da ya sakasu a sashensu sai jiyo fitarsa sukai. Basu damu ba. dan tunda safe suka fahimci jikinsa da sauƙi Alhmdllh. Sun kuma san a yanda komai ya rikice bazai zauna ya zuba ido ba. Dan tun ɗazun da yamma labari da ɗumi-ɗuminsa keta yawo a kafafen sada zumunta da gidan redio dana tv akan binciko wasu mafakar master ɗin da sirrikansa da jami’an tsaro sukayi. Harma suna iƙirarin cewar suna gab da kamashi harma da samo iyalan su A.G da ke a hannunsa.

         Sun san wanene Master ɗinsu sarai akan iya taku, duk da kuwa akwai ƙaddarar ɓacin rana da kan iya gittawa tamkar ta jiya da har yakai sun harbesa. amma basa tunanin wannan binciken da suke iƙirarin yi yana akan layin dai-dai. Dan a duk gidan da ya fahimci za’a iya ganesu cikin sauƙi idan sukai aiki sau ɗaya basa sake maimaita ko bin layinsa ma balle shigarsa. So duk inda zasu binciko sai dai ya sake sakasu a ruɗani badai a hanyar kama master ɗinsu ba.

         A ɓangaren Hibbah kam tana idar da sallar ta miƙe. So take tayi wani abu amma tasan duk hanyar da zatayin bazai bari ba sai ya toshe ta kafin ya fita. Tunda ta sha shi sau ɗaya bazaiyi sakaci na biyu ba koda da kuskure. Gadon ta sake hayewa ta kwanta da cigaba da cuɗawa da kwancewa akan wannan sabon salon da ya dauka na zuwa mata da fuskar yaya Isma’il dan yaji ta ambaci nagartarsa ga reta ga ahalinta kuma. Tun tana lissafin dai-dai har idanunta suka fara lumshewa, dan dama barcin ma ba sakinta yay ba. 

★★★★

          A ɓangaren Master kuwa tafiyar da bata gaza mintuna goma sha bakwai bace ta kaisa babbar headquarter ta ƴan sandan jihar. Tunda yay horn securitys da ke a wajen suka leƙo suka gansa sai suka wangale masa ƙofar cike da girmamawa da ɗokin ganinsasuna sara masa. Ɗan salute ɗinsu yay shima yana tura hancin motar tasa ciki. 

        Cike da ɗoki wasu jami’an samari biyu suma suka iso garesa dai-dai yana buɗe motar ya fito. Wellcome sir!”. Suka haɗa baki wajen faɗa. Murmushi yay musu tare da miƙa masu hannu alamar suyi musabaha. Ɗabi’arsa ce hakan tunkan yay balaguron da babu wanda yasan ina yaje, sudai sun bar ganinsa ne kawai. Hannun suka bashi suma suka gaisa. Kafinyay musu nuni da Kayayyakinsa da ke cikin motar alamar su ɗebo.

          Yayinda shi kuma yake bin ko’ina na station ɗin da kallo cike da kewa, duk da dai yakan shigo dama a sace cikin ɓadda kama. 

      Duk da dare ne akwai jami’ai sosai a ciki ta kowanne department, kuma mafi yawancinsu sun duƙufa ne akan batun Master ɗin, dan shine aikin da gaba daya ya birkita kowacce hukuma daga jiya zuwa yau.

      Duk ta inda ya gitta sannu da zuwa ake masa bisa balaguron da yay na kusan shekaru biyu da rabi da girmamasa tamkar yanda shima yake bama kowa girma a rayuwarsa. A gefe kuma abokansa da manyansa na nuna jin daɗin dawowar tasa a dai-dai gaɓar daya dace. Masu kuma jin haushinsa najin takaicinsa dan mutum ne jajirtacce akan duk abinda yasa gaba tun ma yana ƙaramin ɗan sanda.

         Katafaren office ɗin da yafi kowanne girma da alfarma a headquarter ɗin ya nufa kai tsaye su Rayyan biye da shi. Tun kan ma suyi knocking aka buɗe musu ƙofar alamar ansan da zuwansa. I.G da ke zaune shi da wasu manyan ginshiƙai na hukumar ƴan sandan EFCC da General na sojoji suka maida hankalinsu ga ƙofar fuskokinsu cike da fara’ar tarbar gwarzonsu, wanda ya yarda zai sadaukar domin ƙasarsa da yankinsa bisa aikin sirri na haɗin kai da suka shirya a tsakaninsu kawai saboda tashin hankali da rikicin da kowa ya kasa gane bakin zarensa a yankunansu……….✍

_________________________

TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI……_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_

_NISHADI_

_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*

*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300

2____400

3____500

4____700

5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????

#team ZAFAFA BIYAR????????????????????

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*

 

[ad_2]

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button