Uncategorized

TAKUN SAKA 41

      A dalilin ganin zan iya ɓoye fuskata yace babu damuwa ma zan iya aiki kafaɗa da kafaɗa da su kamr kowane ɗan sanda a zahiri, a baɗini kuma aikin sirrinmu, sai dai zan cigaba da ɓaddabamin ɓoye ainahin fuskar Isma’il zuwa wani lokaci. Na amince da hakan. Na kuma shiga cikin tawagar horaswa da fuskar Muhammad Shuraim, cikin amincin ALLAH na fito a jerin jami’ai masu matuƙar ƙwazo. Sai dai ana kammalawa na sake ɓacewa ɓat bisa umarnin I.G. Na sake komawa cikin su Master da zuwa yanzun dukkan sirrinsa a tafin hannuna yake, dan dukkan abokan mu’amularsa a cikin manya da ƴan ta’adda irinsa na sansu nasan inda suke, nasan makamar harkokinsu. Na iya maganarsa. Na iya salon tafiyarsa na iya abubuwa da dama irin nasa wanda inhar na juye maka shi baka isa cewa bashi ɗin bane musamman idan na saka mask na fuskarsa. Indai taƙaice miki zance a wani dare batare da sanin kowaba a cikin yaran Master na ɗaukesa, zuwa safiya na maye gurbinsa, yaransa kuma duk nabi hanyoyi daban-daban aka kamasu ɗaya bayan ɗaya ta yanda babu yanda ubannin gidansu zasu iyama ganosu balle cetonsu. A gefe kuma ina aikina a zahiri tuƙuru game da dukkan abinda ya dace”.

         “Duk da kasancewana normal ɗan sanda, nayi ayyukan sirri da yawa bisa umarnin I.G ni da ɗansa Abdull da ya zama aminina tun a jami’a. Efcc Chairman da General abokaine na I.G tun ƙuruciya, hakanne yasasu sanin ayyukana a wajen I.G har suma suka fara jana jikinsu dan halayyarsu ɗaya da I.G akan ganin ƙasarmu ta dawo hayyacinta. Sai dai rashin mabiya na ƙwarai yasa basa iya tufƙa sai an warware musu. Nasha kawo musu information da yawa daya shafi ayyukansu a dalilin bincike na. Hakanne yasa a wasu lokutan nakanyi aiki kafaɗa da kafaɗa dasu tamkar yanda akasan jami’an tsaro da yawa sunkanyi hakan a sirrance a tsakaninsu. Kin shigo rayuwata a dai-dai gaɓar da nake gab da kammala tattara bayanai akan duk wasu masu hannu bisa ta’addancin Master. Naso hukuntaki, dan kin kusa ruguzamin aiki, amma sai labarin ya canja salo a dalilin I.G, shine yasa akai masa bincike akanki da ahalinki harya gano bakida wani dalili na harata tsiwace kawai da rawan kanki. Babu wani kwanakana ya bani shawarar aurenki. Ban iya cemasa komai ba dan yanada mutunci da girma a idanuna. Sai dai na dauka ɗammarar shiga jikinki nima dan tabbatarda ƙwazonki da yaketa yabawa harda kwaɗayin na aureki. Dukkan abinda su A.G sukai miki mun sani, musamman daya kasance ni suke ɗauka Master ɗinsu a halin yanzun. Muhibbat a yau na gama aikina daya shafi wancan Master ɗin, zan kuma damƙashi ga hukuma shi da su A.G, zan kuma bayyana fuskar Isma’il ma duniya, shiyyasa na fara nunata gareki bayan iyayena, baba, Habib, I.G, da kuma su Ummi. Sai dai kafin hakan inason ki sani tun randa na fara ganinki a asibiti kikaima zuciyata shigar sauri. Kece kika ruguza dukan yaƙinina akan ƙin yarda da mace, kece kika ɓata duk wani alwashina akan soyayya. Da gaske nake ina sonki”.

          Hibbah da gaba ɗaya hawaye suka gama wanke fuskarta tun fara bata tarihinsa ta matsa jikinsa da sauri ta rungumesa tare da fashewa da sabon kuka, sai kuma ta ɗago tana kai masa kananun duka a ƙirji kukan na sake kufce mata……….✍

      

TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI……_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_

_NISHADI_

_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*

*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300

2____400

3____500

4____700

5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????

#team ZAFAFA BIYAR????????????????????

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*

 

[ad_2]

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button