TAKUN SAKA 46

“Yes sir!”.
Master ya sake faɗa.
Sosai yaya Abubakar ya narke a tsaye, dan shikam yau Isma’il ya matuƙar jefa tunaninsa a garari da ruɗani. C.P ya katse masa tunani ta hanyar kiran sunansa.
Maida hankalinsa yay ga C.P ɗin yana ƙoƙarin dai-daita yanayinsa. Shima yace, “Yes sir”.
“Zaka taimaka masa a wannan aikin saboda na yarda da ƙwazonka matuƙa, shiyyasa mukasa ya ɗakko mana kai, dan mune muka saka aka ɓoyeku saboda information da muka samu cewar jami’an farin kaya zasuyi amfani da ku saboda ƙanwarka dake a hannun master. Kaga wannan shine amfanin sanar da abu da wuri, da baka sanar min ba da nima zan shiga tawagar masu zargin kasan master kai da ahalinka”.
Yaya Abubakar da duk suka rikitasa ya ce, “Thanks you sir” kawai, dan yafi buƙatar jin komai da ga bakin Isma’il, zuciyarsa ta fara raya masa Isma’il rainama su C.P hankali yake kenan suma? Kokuwa wani abu ne daban……
I.G dake rubuce-rubece jikin takarda ya miƙama Master. “A.S.P a yau zaka dawo filin daga, sai kayi ƙoƙarin haɗa sabon team. Ga wannan file ɗin zaka samu dukan bayanan da zaka buƙata a ciki insha ALLAH”.
Takardan da file ɗin master ya amsa da faɗin, “Thanks you sir”.
Daga haka suka fito, Master ya sake salute ɗin I.G cike da wani salo. A waje suka bar Abdull, dan haka ya miƙe suka fice a tare magana fal bakin yaya Abubakar.
Sai da suka fito da ga katafaren gate ɗin Yaya Abubakar da abu keta masa kaikawo a cikin rai ya duba Master.
“Anya kuwa Isma’il baka ɓoye mana wani abu? Zuciyata ta kasa riƙe zargin da take maka a wannan gaɓar gaskiya. Dama kai jami’in tsaro ne?”.
“Jajirtacce ma kuwa! Gwarzo abin kwatance da alfahari ga al’ummar wannan ƙasa.”
Abdull ya bama Yaya Abubakar amsa kai tsaye yana murmushi da juya sitiyari.
“Karka yarda da shi”.
Master ya faɗa yana duban Yaya Abubakar dake kallonsa ta mirror yana wani ƙayataccen murmushi dake tafe da ma’anoni da yawa. Murmushin shima Yaya Abubakar yayi a karon farko ya ɗauke kansa yana jinjinawa. “Dama na jima ina wannan zarigin a raina, a randa aka kaimu gidan can kuma na sake tabbatarwa. Jira da sauraren zuwanka kawai nake dama ai. Amma abinda ban fahimtaba anan shine, suma su I.G basusan kaike basaja matsayin master ba kenan?”.
Shiru Master yay tamkar bazai amsa ba. Sai kuma yay murmushi da kai hannu ya zare mask ɗin fuskarsa. Yaja tissue ya goge real face ɗinsa yana furzar da huci. “Ɗan uwana nake kallonka, dan tunda har kasan wanene Isma’il wannan ma zan iya sanar maka saboda a ƙarshen tattare aikin nan nake bana son abinda zai maidani baya kodan Muhibbat.” ya ƙare maganar da ɗaga idanunsa suka kalli juna da Yaya Abubakar. Murmushi sukayi a tare, master ya sake ɗauke idanunsa. “I.G yasan komai, C.P ne bai saniba.”
Ko tari kasayi yaya Abubakar yay. dan kuwa a yau ɗinnan ya sake tabbatar da zancen nan na mutane dake kiran Master ɗin Hatsabibi duk da su ɗin bama su gama sanin wanene shi ba. Abdull dake saurarensu yay ƙaramar dariya yana ɗan duban Yaya Abubakar ɗin ta mirror shima. “Yayanmu ai mana afuwa. Wannan surikin naka baida maraba da aljanin kan kuka mai leƙa gidan kowa. Sai kun haɗa da addu’a gaskiya”.
Mangare masa ƙeya Master yayi, hakan yasasu kwashewa da dariya su duka dan Abdull sitiyarin ya saki sai da Master ya riƙe da sauri. Har yana magana cikin suɓutar baki.
“Kai ɗan iska karka zubar damu wlhy ban gama angwanci ba, Baby luv na buƙatata a kusa da ita”.
Abdull ya tsaida motar yana kwasar dariya. Yaya Abubakar ma dai dariyar yakeyi, ransa fal farin ciki duk da sun jima da fahimtar irin son da Isma’il ɗin kema autarsu.. Master ya harari Abdull yana ƙumshe tasa dariyar dan harga ALLAH suɓutar bakice. Cikin borin kunya yace, “Ɗan haɗa gurmi in bazaka tada motarba zamu fita mu barka dan munada abunyi”.
“A’a miyay zafi na Baby luv. Bara na kaiku nikam kafin ka ƙonemu a titi. Shiru Master yay bai sake tanka masa ba. Yaya Abubakar ma dai sai ya saki zancen ya cigaba da duba file ɗin da I.G ya bama Master ɗin har suka kaisa station ɗin da yake aiki suka ajiyesa bayan Master yay masa bayanin shine zai haɗa musu team ɗin, shi kuma zaije ya ƙarasa tattare abinda ya rage daga nan zuwa safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu zasu fita operation ɗin. Cike da gamsuwa Yaya Abubakar ya basu hannu sukai musabaha sannan ya fita.
Daga nan gida suka wuce suma. Inda su Habib suke jiran dawowar master ɗin dan tun a jiya ya sanar musu yau ɗin ranar aiki ce da ga nan har zuwa safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu…………✍
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????
#team ZAFAFA BIYAR????????????????????
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*
[ad_2]