Uncategorized

THE GOVERNOR’S WIFE 3

Bayan fitar Bilkisu daga falon, Alhaji Kachallah ya faɗa kogin tunani. Ta ina zai fara? Akwai gaskiya a hasashen Bilkisu dole ne ya san yadda zai yi ya shawo kan matsalar tun kafin lokaci ya ƙure a juye ma sa baya.

***

“Miyake faruwa naga kwana biyu ba kya fita”

SSK yai maganar yana zama gefen gadon Bilkisu tareda kissing goshinta.

“Ba na jin fitan ne kawai. Ina buƙatar hutu ne ma”

“Nima ina buƙatar hutun nan Allah. Inaga tunda Gwamna ya dawo why not mu je UK hutu ko da na sati biyu ne?”

“Its a good idea gaskiya. Muna buƙatan hutun nan sosai” ta yi maganar tana murmushi.

SSK bai jima da fita daga ɗakinta ba wayarta ya hau ruri. Madam Bintu ta gani a jikin screen ɗin hakan ya sa ta faɗaɗa murmushinta. Ta yi saurin ɗaukan kiran tana faɗin ” mutanen Turkiyya kin shigo kenan”

Daga ɓangaren Madam Bintu ta ce “na shigo jiya da dare zan shigo wajen ki anjima”

“To sai kin zo”

Ƙarfe biyar da rabi sai ga Madam Bintu a gidan ta.  Hansa’u ta kira ta kawo musu abin taɓawa.

“Har yanzu ba ki rabu da wannan matar ba bayan shirmen da ta yi kwanaki”

“Bintu tausayi ta ke bani Allah. Besides yanzu ta iya aiki sosai ba kaman farkon kawota ba sai dai ba a rasata da shirme kam. Most importantly tana sani dariya and that’s help alot ga mu ma su hawan jini”

“Ok” ta faɗa tana ƙarewa Hansa’u kallo. Gani ta ke  kaman idon matar na mata kama da wacce ta sani amma ta rasa gano ko wacece.

Bayan Hansa’u ta bar wajen Madam Bintu ta tambayi Bilkisu yadda taron matan Gwamnoni ya kasance dan lokacin da aka yi taron ba ta ƙasar.

“Ba abunda zan ce miki Bintu sai dai in ce kawai taro yayi kyau. Kuma za a sake wani taron nan ba da daɗewa ba”

Madam Bintu ta kalli Hajiya Bilkisu cikin rashin fahimta, maimakon ta mata ƙarin bayani sai kawai ta fashe da wata ƙasaitacciyar dariya.

**

A chan gidan Yallaɓai kuwa Chief of Staff (COS) ɗin Gwamna ne a gaban Yallaɓai yana ma sa bayani mai mahimmanci wanda ya sa Yallaɓai nitsuwa na ban mamaki. Har ya gama bayanin Yallaɓai bai ce komai ba sai ma  murza gemunsa da ya fara yi a hankali.

Ba kasafai ya ke samun ma su taurin zuciya irin ta KACHALLAH ba. Shekaru da dama an taɓa yunƙurin aikata irin wannan abu sai dai kuma komai ya zo ya chanja a ƙurarren lokaci.

“Ka haɗa meeting da Kachallah cikin satin nan”  Yallaɓai ya faɗa bayan yayi dogon nazari.

COS yai murmushin gefen baki dan ya san yanzu liyafa za ta cigaba. Ya ƙwallafa rai sosai akan Gwamna Saminu Bacchi sai dai cikin shekaru uku da yai a kan mulki sun samu saɓani sosai domin lokacin da idon Gwamna Saminu ya buɗe da kuɗi sai ya zamana yana ƙoƙarin take duk wata hanya da su suke  yagan rabon su, yanata wawure komai shi kaɗai da iyalin sa ba dan Yallaɓai ya tsayar ma sa ba wasu abubuwan haka za su dinga wuce shi.

Saifuddeen Sa’ad Kachallah daban ya ke da Gwamna Saminu, kuɗi ba za su ruɗe shi ba. SSK ya gaji arziƙi irin arziƙin da ko da ba zai yi wani aiki ba zai isheshi ci da iyalen sa har iya karshen rayuwar su ba tareda sun yi talauci ba.

SSK shine mafita a gareshi da shi da KACHALLAH.

***

“Wallahi an cuceni Ya Ubayd. MD mugu ne wallahi”

Ubayd yai murmushi ya ce ” ni kam ya min dai-dai, dama daurewa kawai na ke yi amma kullum aka nunaki a TV sai na ji kamar zuciyata za ta fashe”

“To ta Allah ba taka ba. Sai an maidani reporting unit”

“Ina kishin ki Asiya na haƙura ne kawai saboda babu yadda zan yi amma Allah idan ki ka shigo gidana ba za ki sake bayyana a TV ba, ko dai ki tsaya aiki a bayan fage ko kuma ki haƙura da aikin”

“Ya Ubayd you are joking right”

“I’m not Asiya. Gara ma ki saba da inda aka kai ki yanzu”

Sati ɗaya da suspension ɗin ta aka kirata akan ta dawo. Yau ta fara fita aiki amma duk ta ji ba daɗi ba ta son ɓangaren da aka kaita ko kaɗan.

“Ya Ubayd ba haka mu ka yi da kai ba baka ce za ka rabani da aikina ba”

“Ba rabaki zanyi da aikin ki ba na dai ce bayan munyi aure ba ƙaton da zai sake ganin ki a TV yana ƙare miki kallo especially with irin shigan da ki ke yi” yai maganar da ɗan ƙarfi

Asiya ta miƙe daga kujeran da ta ke zaune ta ce “ba ka isa ba kuwa”

Ta wuce ta barshi a wajen baki buɗe.

Washegari ko jiran sa ba ta tsaya yi ba ta  hau keke ta wuce office…

***

” na gaya miki babu kuɗi a ƙasa, duk wani abu da zamuyi yanzu mutane za su yi magana. We need this year to work on something saboda campaign da za a fara nan da watanni huɗu ma su zuwa”

Gwamna Saminu Bacchi kenan yana ƙoƙarin lallashin matar sa. 

“Kana so ka ce min ba ka da kuɗin da zamu celebrating 8years anniversary na mu?”

“Ba wai ba kuɗin bane amma kuɗin campaign ne”

“Kar ka gaya min magana dan Allah. Uban me Saifuddeen Kachallah ke da shi da zai iya celebrating 15yrs anniversary na su a tsakiyar teku  shekaru biyu da suka wuce. Na je party ɗin fa. Sati biyu aka yi a cikin jirgin ruwa wanda komai da komai da mutanen ciki su ka yi yana wuyan sa”

“Sha’awanatu. Saifuddeen Kachallah  millionaire ne tun kafin mu hau gwamnati ko mi zai yi ba wanda zai zargeshi amma ni…”

“Ba zan yadda ba fa. Dole ne ayi anniversary party namu a Italy. Wallahi kai ka ke sawa ma Bilkisu Kachallah tana raina ni. Ina matar Gwamna amma  ko motan da ta ke hawa tafi tawa”

“Yanzu kinsan ya za ayi ne? Za mu yi party amma a nan Nigeria. Bamu jima da dawowa daga ƙasar waje ba idan muka sake fita mutane za su yi magana…”

“Wai ina ruwanka da mutane ne. Kai fa Gwamna ne. Gwamnar jahar CONGO wancan tafiyar Asibiti ka je wannan tafiyar kuma yana cikin yiwa iyalinka hidima ne”

” Amma Sha’awa…”

Daga haka Gwamna Saminu Bacchi ya haɗiye sauran maganar sa saboda haɗe bakin su da Sha’awanatu ta yi.

Washegari da safe Gwamna ya tashi da wani irin ciwon kai da ciwon ƙirji, ciwon ne ma ya tashe shi daga bacci tun ƙusan ƙarfe huɗun Asuba.

Wasa-wasa har ƙarfe shida jikin ba sauƙi duk da kuwa ya sha magungunan sa. 

“Za mu wuce Asibiti ne ko a kira maka likita?” First lady ta tambaya cike da fargaba.

“Ki kira Likita”  ya faɗa da ƙyar saboda yadda ƙirjinsa ke takure.

Bai kai awa ɗaya ba saiga likitan sa ya iso koda ya duba shi cewa yai jinin sa ne ya hau sosai idan akwai wata damuwa da ke ransa to yai ƙoƙarin kauda ita dan   abunda ya sa a ransa ka iya jawo ma sa bugawar zuciya.

Shi dai ya sani bai sa komai a ransa ba. Ba a fara campaign ba balle ya ce shine ke ɗaga ma sa hankali. To kodai Barasar daya kwankwaɗa jiya da dare ne? Duk da likitan sa na chan Germany ya hana shi shan barasa. Duk da kuwa ya san ba zai iya dena sha ba, sai dai ya rage sha ba kamar da ba.

 Allura da Likitan ya ma sa ya taimaka ma sa sosai dan har ya samu yayi  bacci. Lokacin da ya farka kusan ƙarfe goma shaɗaya na safe. 

Sha’awanatu ta taimaka ma sa yai wanka ta kawo ma sa abinci har kan gado amma bai iya ci ba sai shayi kawai ya sha.

Ƙishirwar giya ce ta dameshi dan duk da yana jin jiki yayi amanna idan ya ɗan kurɓi kaɗan zai samu sauƙi. Fita yai  daga ɗakin Sha’awanatu ya wuce na sa ɗakin a nan ya fito da kwalbar giya ya kwankwaɗa ya girgiza kai ya sake kurɓan kaɗan sannan ya mayar da sauran ma’ajiyar sa.

Shiryawa yai ya fita saboda akwai meeting da zai yi da wasu contractors ƙarfe biyu na rana.

“Yanzu yadda baka da lafiya haka za ka fita?” 

“To ya za ayi dole ne mu yiwa talakawa aiki” 

Previous page 1 2 3 4Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button