Uncategorized

THE GOVERNOR’S WIFE 3

“To. Amma ka dai yi tunani akan abinda na ce”

Dariya Gwamna ya fara yi sai kuma ya dafe ƙirjinsa saboda yadda ya ji ƙirjinsa na suya kaman an saka masa wuta.

“Your excellency jikin ne?”

Kafin ta ƙarisa maganar Excellency ya kai ƙasa.

“Your excellency, miya faru? Ƙirjin ka ne?”

“Waye a nan? a kira likita. Excellency… Saminu…Saminu ka tashi”

Lokacin da aka garzaya da Gwamna Asibiti ya riga ya cika likita ya ce zuciyar sa ce ta buga (cardiac arrest)…

***

Mataimakin Gwamna na zaune a  office Chief security officer ya kira shi, kiran da ya ɗaga ma sa hankali  sosai dan kuwa a kiɗime ya fice daga office ɗinsa ya wuce Asibiti.

Mummunan labarin da aka gaya ma sa a waya shi ya tarar a wajen domin kuwa  Allah yayiwa Gwamna Saminu Bacchi rasuwa.

A chan Kachallah House kuwa Alhaji Sani Kachallah ne ke waya da mijin ‘yar sa wato Saifuddeen wanda ya jaddada ma sa mutuwar Saminu Bacchi.

“Mi aka ce ya kashe shi?”

“Baba ba zan iya cewa komai ba yanzu”

Alhaji Sani Kachallah ya ce “ba komai zan kiraka anjima”. Yana kashe wayar ya shiga kiran numbar Yallaɓai.

A chan gidan mataimakin Gwamna kuwa Bilkisu Kachallah ce zaune a falo tana cin gasashshiyar kifi da soyayyen dankalin turawa haɗe da lemo mai sanyi.

“Hansa’u, Hansa’u ” Hansa’u ta fito da gudu.

Miƙo min remote ina son kallon news.

Hansa’u ta miƙa ma ta remote ɗin Bilkisu ta chanja channel daga Zee world zuwa Congo news…

***

Asiya Shahidah na zaune a sabon office ɗinta tana aiki akan computer abokin aikinta Ɗahiru ya shigo office ɗin da sauri.

“Shahidah kin san labarin dana ji kuwa daga fitata a office ɗin nan?”

“Miya faru?”

“Yanzu Abigail ta ke kawo rahoto cewa Gwamna ya rasu”

“Wani Gwamnan?”

“Gwamnan Congo mana”

“Innalillahi! Dan Allah?”

“Allah kuwa”

Asiya Shahidah ta miƙe ta bar office ɗin da sauri…

Kusan awa ɗaya da rasuwan sannan Mataimakin Gwamna kuma acting Gwamna ya bada sanarwan mutuwar Gwamna Saminu Bacchi.

*”Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji’oun. Haƙiƙa dukkan mai rai mamaci ne. Muna yiwa Jahar Congo ta’aziya bisa rasuwan Mai girma Gwamna Alhaji Saminu Bacchi wanda Allah yai wa rasuwa yau shabakwai ga watan Nowamba. Haƙiƙa wannan jaha ta yi babban Rashi”* hawayen da ya zubo ma sa yai saurin sa hankerchief ya goge sannan ya cigaba da bayani

*” Insha Allahu za ayi jana’izar sa a gidan gwamnati da ƙarfe biyar na yamma”*

Asiya Shahidah da ke kallon news ɗin a talabijin da ke office ɗin su CY ta ce “Ikon Allah har da kukan munafurci kaman bai ji daɗin abinda ya faru ba, Shege. Ai yanzu kam jahar nan ta shiga uku a hannun wannan Wawan”

A ɓangaren Yallaɓai kuwa yana gama kallon bayanan da SSK yai ya danna remote ya kashe T V sannan ya kai duban sa ga Kachallah ya ce

“To kyan alƙawari dai cikawa. Ina fata Saifuddeen zai bamu haɗin kai”

“An gama Yallaɓai”

Yayinda wasu ke cikin baƙin ciki da rasuwan Saminu Bacchi wasu kuma na nan suna planning yadda za a juya Gwamnati.

Duniyar kenan. Tunma kafin a sa shi cikin ƙasa har an riga an cire shi daga lissafi.

Da ‘yan siyasa za su dinga tunawa da cewa akwai ranar da dukiya ko matsayi ba zai amfanesu ba ƙila da za su tausayawa talakawan su.

[ad_2]

Previous page 1 2 3 4

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button