Uncategorized

TUBALI Page 11 to 20

“In sha Allah, Junaid bazai kashe kiba, da izinin ubangiji sai kin rayu, rayuwa mai Al’barka domin ke ayace, kuma izinace sannan taƙin shaida mai ƙarfi”.

Hannunta ya kuma riƙewa cikin irin sona uba da ɗiyarsa yace.

“Jannart zaki rayu cikin aminci. 

Domin Ubangijin daya raya Annabi Musa acikin gidan Fir’auna cikin lfy da aminci.

Shiya rayaki a gidan nan cikin lafiya da aminci.

Ya rigada lokacin ya ƙurewa Magautan, bazasuyi nasaraba, dan sunyi nasararsu tun shekarun baya sun gama nasara, yanzu nasarar tamu ce. 

Gsky zatayi halinta, in sha Allah zanci gaba da zame miki jigo. Kuma zan nema miki GARKUWA, cikin gaggawa kafin su juyo garemu”.

Shiru tayi tana jin kalaman ƙanin mahaifin nata, sai dai ta kasa sama musu mizanin da zata aunasu ta ajiyesu ta fahimci manufarsu.

Gogewar hausarta batayi surfin ta Ƙanin mahaifin nataba.

Cikin ruɗanin da kalamanshi suka saka mata tace.

“Abba ni na gaji da zaman gidan nan, dan Allah ka sake roƙon Daddy ya bakani ko zai yarda, in koma gidanka.”

Cikin sauƙe nannauyan numfashi yace.

“Jannart sake roƙar tashi tamkar wasa da rayuwarki ne, kamar dai kusanto da a …”.

Da sauri ya haɗiye ragowar mgnar sanin ƙwaƙwalwarta bazata fahimci zancen nasa ba.

Ita kuwa cikin sanyi ta zuba mishi ido.

Dai-dai lokacin kuma Mom ta shigo da tray a hannunta, cup ɗin tea ne mai kauri, sai soyayyan irish da ƙwai.

Cikin nitsuwa tace.

“Abba to..”.

Hannu ya ɗan ɗaga mata tare da cewa.

“Ya isa da yamma zan dawo muyi mgn Jannart kada ki kuma yin kuka”.

Ya ƙare mgnar yana miƙewa tsaye.

Kai kawai ta gyaɗa mishi kana ta bishi da ido har ya fita.

Bayan ya fita Bathroom ta shiga, ruwa ta ɗan watsa, bayan tayi brosh kana ta fito.

Ba laifi ta ji sauƙin sosai numfashin ta ya dai-dai-ta.

Tea ɗin kawai ta iya sha.

Kana ta koma ta kwanta dan Alllurar bata ida saketa ba.

Can cikin bacci taji wayarta na suwa.

“Mahmoud”.

Tace tare da amsa kiran.

Nan yake shaida mata cewa.

Dr Rayyern Mai-nasara yana hanyar dawowa Nigeria tun safe jirginsu ya taso.

Zuwa azahar zasu sauƙa Abuja.

Kuma yau ɗin zasu shigo Kano cikin alamun bacci tace.

“Toh ya akayi kuma lbrin ya sauya Mahmoud ba sai jibi ba kace?”

Gyara zamanshi yayi tare da cewa.

“Uhumm kin kuwa san waye Dr Rayyern, mutun yana nan tamkar Wahainiya gane shirinsa ko manufarsa fa wuyane dashi.

Ke dai in kin samu dama kiyi ƙoƙarin zuwa Airport da yamma wata ƙil a dace, zan turo miki hotuna Yah Usman PA Yayan Abokina Deen wanda yayisu a bayan motocin Dr Rayyern ɗin so sai ki ɗauki number’s ɗin motocin ta wannan hanyar zaki iya samun damar bibiyarsa”.

Cikin sanyi tace.

“Toh Ngd matuƙa”.

Daga nan sukayi sallama.

Salman ta kira yana ɗagawa yace.

“Ya jikin namu?”.

Cikin sanyi tace.

“Da sauƙi waya gaya maka?”.

“A’isha Lawal ce ta gaya min tace ɗazu data kira Mom ce ta ɗaga wai jikinki ya tashi.”

Ayyah tace a taƙaice kana ta mishi bayanin da Mahmoud ya mata ta ƙara da cewa.

“Ka shirya da yamma muje Airport ɗin bari in turoma hotunan”.

Toh yace kana sukayi sallama.

Ƙarfe biyu dai-dai jirginsu ya sauƙa cikin international Airport Abuja.

Bayan wasu ƴan daƙiƙu, aka fara fitowa.

Mutun kusan 21 suka fito.

Kana Rayyern ya sako ƙafarsa ta dama kan matakalan forko.

Wani irin sassanyan numfashi ya shaƙa a hankali tare da zuƙan iskar ƙasarshi abin sonshi da al’faharin shi.

A hankali ya fara takowa yana sauƙa cikin haiba.

Da sauri ya ratayo jakarsa a kafaɗa tare da biyoshi a baya da gudu.

Usman kuwa shima jakarsu ya ratoyo kana ya biyoshi a baya.

da sauri ya matsoshi.

Juyowa yayi jin an riƙe mishi hannun damanshi.

“Hamma Rayyern daga nan wanne state ɗin zaka tafi”.

Ya rasa gane meyasa zuciyarsa ke bawa yaron amanna ko dan kamar da sukeyi ne.

Sam bai shiryawa amsa mishi ba kawai yaji lips ɗinshi sun furta.

“Kano”.

Wani irin tsalle yayi tare da cewa.

“Yesssss! Nima Kano zan tafi ai”.

Cike da mamaki Usman ya nufosu har yana tuntube tare da cewa.

“Sir wannan fa?”.

Juyowa yayi ya kalli Usman da salon.

Baya son shisshigi.

Shi kuwa Riyyam-nsra da sauri ya dawo kusa da Usman hannu ya bashi tare da cewa.

“Ni ƙaninsa ne”.

Baki buɗe Usman ya bishi da ido.

Daga nan masallacin cikin Airport ɗin suka wuce, ganin azahar tayi har lokacin yaso zarcewa.

Suna idar da salla Usman ya miƙe da nufin fita ya samo abinci.

Dan yasan ubangidan nasan bazai buƙaci abinci yanzuba.

Juyowa yayi ya ɗan kalli Riyyam-nsra tare da cewa.

“Bishi kuje Restaurant”.

Kai ya jujjuya tare da cewa.

“Bana jin yunwa”.

Kai kawai ya gyaɗa mishi.

Nan suka zauna har la’asar tayi.

Bayan an idar da sallane kuma, suka koma ciki.

Domin shiga jirgin da zai wuce Kano.

Ƙarfe huɗu da rabi dai-dai jirginsu ya tashi daga birnin tarayyar Nigeria zuwa Kano ta dabo tumbin giwa.

A nan cikin Kano kuwa.

Jannart ce zaune cikin motar, Salman kana shi kuma yana gaba gefe.

Baba Ado dake jansu.

Yayinda sauran garadan dake tsaronta, suke hangame da baƙi a zatonsu tana can cikin ma’aikatar nasu, dan sam basu lura da lokacin da ta fitoba, koda yake Salman ne ya bawa Baba Ado key kana ya jawo motar har zuwa bakin mashigansu ya kawo mishi.

Shiyasa suka fita, basu ganeba.

Kai tsaye filin jirgin sama na malam Aminu Kano suka nufa.

Sosai kuwa Jannart tayi kyau acikin shigar pallazo da kuma tight shirt din dake jikinta, wanda ya bayyana lafaffen cikinta, kasancewar kuma rigar nata na d’an bayyana nipples dinta ne, yasa ta daura wata Navy blue fashion top akan shigar ta ta, wanda tsawonsa ya kawo har guiwanta, Yayinda ak’afanta take sanye da wani navy blue hill shoe, na company’n gucci mai kyau da tsada da uban tsini, akanta kuwa wani had’add’en medium vail ne wanda ya sauko harkan kirjinta.

Sam akan fuskarta babu wani kwalliya sosai, saidai kuma hakan bai hana zallar kyawun fuskarta bayyana ba, Yayinda small lips dinta suka sha peach lipstick, acikin jikinta kuwa wani sassanyan k’amshi ne yake tashi.

Suna shiga cikin Airport ɗin sukayi paking a Airport parking.

Kana suka wuce suka nufi cikin.

Bayan isarsu da kamar 5 minute, jirginsu Rayyern yayi sauƙar angulu.

Bayan yan daƙiƙu ne kuma matafinyan suka fara fitowa.

Da sauri Usman ya matso kusa da uban gidan nashi, cikin yin ƙasa da murya yace.

“Sir in kira driver?” 

Shiru yayi ganin ya ɗan kaɗa mishi yatsarshi manuniya.

Shi kuwa Riyyam-nsra da sassarfa yake biye da Usman a baya.

A haka har suka fito asalin filin da matafiya kan zauna su jira masu tarbarsu.

Kanshi ya ɗan ɗago ya kalli taron mutanen, yatsarshi yasa ya ɗan gyara zaman farin glass ɗin dake idonshi.

Gefen lips ɗinshi na ƙasa ya ɗan kamo ya ɗan tauna a hankali.

Da sauri kuma ya ɗan juyo ya kalli bayanshi.

Inda ya hango Riyyam-nsra can baya yana ɗan tahowa yana waige waige a alamun shi yake nema.

Gabanshi ya nunawa Usman tare da yin mgna can ƙasa.

“Ƴan jarida ne, zanbi nan, in sun tsareka kaji dasu.”

Yana faɗin haka, ya ratsa yabi yar siririyar hanyar dake gefen damanshi.

Shi kuwa Usman ya nufi hanyar fitan.

 

Jannart kuwa da sauri cikin tsananin razana ta koma bayan Salman tare da yin ƙasa da kanta murya can ƙasa tace.

“Innalillahi Salman gacan Hakim abokin Yah Junaid idan ya ganni zai gaya mishi.”

Sai kuma ta zaro ido jikin tashin hankali ta dafe kirjinta tare da cewa.

“Na shiga ukuna tare suke da Yah Junaidu ma gashi can bayanshi”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button