WAYAFI SONTA 3

????WAYAFI SONTA ?????
WANNAN LABARIN NA KUDINE…gamai bukata zata biya naira 300 kachal ta karanta ” tahanya mafi sauk’i Zaki siya Zaki tura kudin ta account number 0089110527 suwaiba Hussaini zakirai access bank… saikiyi screen shot kituro shaidar kin biya ko kuwa kituro MTN ta wannan number na 300″ 08100084251
Domin karanta bOoks namu..
Y’AR SADAKA book2 na mmn sultan dakuka dad’e Kuna nema danjin yazata kasance…naira…200 ne gamai bukata yatura kudin ta wannan account 0089110527
WAYAFI SONTA ( mmn fareesa) naira 300
Induka kakeso naira 400 ne kachal…masu bada kati suyi mgn a wannan number 08100084251….
Inkinsan Zaki fitarmana da books karki siyasa….
Free page
p3….. cike da mamakin k’aryar da Musa yasharara mama ke kallonsa Baki bud’e….bata sare da lamarinba.saida taji goggo haule nacewa,ahto innayi mgn ace ga munafuka kak’i yarda inacikin bayi inajin yadda take aibatasa…. innalillahi wa inna ilaihir Raju un! Mama tafad’a had’e da kallon baba tace narantse da ALLAH Wanda yabusamun Rai Kuma gunsa zankoma wlh duk abinda suka fad’a malam ba gsky bane!iya abinda nasani zainab ta shigo a guje ta b’uya bayana”inabtambayarta lfy Musa yashigo….ta Ida sanar Masa yadda akayi….mlm yadubi zainab yace ke gayamun mekika Masa?”
Zainab taja numfashi tace wlh baba antasomu islamiyya na mance littafina husnul Muslim gun saratu kawata,saina natuna ,yanagunta nafasa zowa nan nabita gdnsu” asoron gdnsu Mai duhu nasami Yaya Musa da yayarta harira ” hannunsa cikin hijabinta Yana….ya isa cewar baba Yana watsawa Musa wani mugun kallo” kuka goggo haule ta saka Wai mama da y’arta sunhad’a Baki sunyiwa d’anta sharri…baba yace dama dalilin biyokin kenan zaidaka dankingansa?” Zainab tace eh…baba yadubesa yace kasameni adakina kaida uwarka…bejira amsarsuba yanufi dakinsa… goggo haule ta dubi mama d zainab tayi kwafa had’e da cewa insha ALLAH saikunshiga kuncin rayuwa keda ‘yar Taki…mama tayi murmushi tace ba bakinkiba! duk abinda yafaru damu “munyi Imani damacan ubangiji yarubuta zai faru…
**********
Haka rayuwa tacigaba da kasancewa wataran da dad’i wataran sai hakuri”zainab da Umar kullum kwanan duniya k’ara son junansu suke d Kula d junansu” insunyi fad’a su shirya “ahaka har Umar yakammala krtunsa yafara service”yyinda zainab tayi SSCE inta”bayan aurensu da Umar saita Ida karatunta nason Zama Yar jarida…Umar anan kd aka samarmasa yyi service nasa…hakan yasa Yana gd Koda yaushe “sannan Yana dinkin Mata”( telane)
Sanye take cikin areviant gownt ” Tasha attachment yazubo Mata har baya”sai kamshi take zubawa”gefenta naja ce itama taci wanka”parking husna tyi tana yatsina “ta zuge glass d’in motar tana k’arewa gdnsu Umar da zainab kallo ,kamar yadda jiya da dare aka kawota har k’ofar gdn aka nuna Mata , kasancewar itama anan kaduna take” shine yau tadawo Dan Fara cin manufofinta akan Umar…zainab dake doso layin ,tun dg nesa ta hango wata arniyar mota tayi parking agaban gdnsu…har zuwa lokacin da husnah tafito dg motar tacire faskeken glass d’in fuskarta tanawa naja mgn…daidai lokacin da zainab ta iso zata shiga gd da markade ahannunta ” wata faduwar gaba zainab ta ji ganinsu husna dakumjin muryarta tanawa naja mgn”sak muryarta ta yarinyar datace ita buduwar yah Umar ce….Amma sai bata sake kallonsuba ,tayi saurin shiga gd ,tasami mma gaban murhu ta ajiye Mata markad’en,tana cewa bara na dawo mama” mama tace kada kiyi nisa kinsan bansan yawace yawancen da bbu dalili…gdnsu yah Umar zainab ta shiga ta lab’e zaure tanajiyo maganar su Inna da husnah…bayan wucewar zainb su husna suka shiga gdnsu Umar” naja sai wani yatsina fuska take had’e da toshe hanci…sallama sukayi ,Inna dake fama da hura wuta ta amsa musu “tana kallonsu da mamaki Dan tasan badai k’awayen Maryam bane (yarta ta5) Dan tasan sun wuce ajin Maryam azatonta ko wni gu suke nema…maraba ta musu had’e da Basu kujeru y’an tsigunne suka zauna suka gaisa…Inna na lura da yadda suke k’arema gdn kallo da yadda naja ke toshe hanci…kafin tace yara! Meke tafe daku,ko wani guri kuke nema??” amm mama ba haka bane,cewar naja had’e da da nuna husna tace wannan sunanta As’ma’u y’ar gdn Alh mukhtar dalah…Inna ta zaro Ido sbd tasan mukhtar dalah Yana cikin manyan masu kudin kaduna…najah tace to shine suke makaranta guda d Umar na nan gdn jininsu yahadu danata sosai suna son juna shine dg baya yace Wai tahakura auren gd za’amasa…Inna ta dubesu Dan tasan dama makarantar da Umar yake gwamnati ke biyamasa sbd k’okarinsa…subasuda halin sakashi kodaba ba takudiba.. Inna tace shi Umar din yafad’a muku haka?” Eh cewar najah had’e da cewa to yanzun ita Kuma babanta yabata damar ta fito da Wanda takeso ,shine tasanar Masa Umar ne zabinta “to yace Umar yaturo bayan sun Gama service nasu sai ayi auren…ayanzun zai canza muku gd yabawa Umar mota da kud’i yaja jari….Da sauri Inna tad’agawa naja hannu had’e da cewa ya isa! nasan waye Umar…Amma kiramunshi awaya kice yazo inajiransa….najah takalli husna ta kiftamata Ido…abinda Basu saniba Inna duk tana hankalce dasu…kafin suyi mgn baba yafito dg d’akinsa Baki washe duk maganar dsukeyi yaji komai…da sauri suka rusuna suna gaidashi…ya amsa jiki na kirma had’e da cewa Ina surukar tawane acikinku?”
Najah na murmushi tanuna husna tace gata nan baba…yyi murmushi yace Masha ALLAH insha ALLAH Muna nan tafe ayi mgn sbd…..haba mlm miye hakane Wai?” Zaka biyewa yara kana mgn dasu….iya nan zainab ta iyaji” zuciyar ta namata nauyi kirjinta na buguwa fatanta duk abinda suka fad’a k’aeyane sbd tasan waye Umar…saidai inta tuna kalmar hausawa dasuke cewa nmj beda tabbas! Saitaji gabanta yafad’i….hawaye masu zafi suka wanke mata fuska…ta juyo sbd ta tafi suka had’a ido da Maryam kanwar Umar…da sauri Maryam tace lfy zainab kike kuka ??” Girgiza Kai zainab tayi batace komai ba tajuya d gudu ta fice…. Maryam ta fita itama Dan Kiran Yaya Umar dake shago yazo yaji meke damun zee…
Baba kuwa kallon Inna yyi yace Ina ruwanki ?” Kirabu Dani…kafin yadubi naja yace ai tunda tanasonsa bbu komai dama yarinyar da zanmasa auren gd da ita itama d’iyatace Dan haka sai abawa wani dama yafito acikin masu sonta….Inna ranta yakai k’ololuwar b’aci cikin b’acin Rai tadubesu had’e da cewa Kai yara kubar gdn nan tun muna girma da arziki nafadamu ko?”baba yace bbu inda zasu sai Umar yazo anyi mgn…da sauri husna da tund’azun bata mgn tace ah ah baba bara mu wuce munyi mgn da Umar awaya kaidai kamishi mgn da kanka… tafad’a cikin rudewa sbd bataso Umar yazo yasameta agdnsu yji bayanin dasuka zo dashi itada naja…kud’i najah ta fito dsu kusan dubu50 Yan dubu dubu tamik’a baba….hannu na rawa yamik’a dan k’arba…..inhar kkabawa mahaifina k’azaman kudinki ya rik’e sainamiki abinda yafi Wanda namiki askul…..d sauri suka juyo su duka sukaga Umar tsaye Maryam na bayansa data kirasa……
Share