A Bari Ya Huce Complete Ebooks

Har goma na dare suna can, yaran suka soma rigima, duk da an basu madara. Uwarsu suke so haikan. Amma
Amiru ya kasa bada su. Saida Habibu yayi mishi alkawarin kafin su tafi gobe zai kai mishi su ofis sannan ya
dauko su har motar Habibu, bayan Hajiya ta cika su da toshi. Daddy ma ya bada check na kudi masu yawa
yace a dinka jamfa, baya son ganin su da daura ‘suit’ irinna Ubansu.
Mairo tayi shirin barci a dakinta dake gidan Yaya Habibu. Ta sanya yaranta a gabanta tana kallon su da fuskar
mahaifinsu. Tana sunsunar su da kamshin ‘miyaki’ wanda ya tuna mata da ‘those precious moments’ da suka
shude a baya. Tana sunsunar su da kamshin ‘miyaki’ da suka kwaso, wanda ya dawo da so da kaunar mijinta
sabo fil a zuciyar ta.
Ta shiga tsakanin su ta rungume kowanne a jikinta. Ta soma sheshshekar kuka a hankali, na tashin tsohon
mikin daya jima da samun sauki. Shiyasa bata so zuwa ba, amma Habibu ya takurata. Ta fadi a ranta Amiru ya
daina son ta…….! Tunda har bai damu daya ganta ba. A karshe ta hakura ta sanyawa ranta salama. Tunda
ance komai yayi farko, to inshallahu yana da karshe WATARANA!
Washegari Habibu ya cika alkawari, ya sake diban Amir da Habib da Esta ya zuba su a mota zai fita da niyyar
kaisu office din Amiru suyi sallama kamar yadda yayi alkawari. Yana kokarin tada mota Amiru na sanyo hancin
motarsa ‘camero’ cikin get din Habibun. Don haka Habibun ya dakata har ya bude motar ya fito.
Ya karbi ‘ya’yansa ya soma ‘kissing’ kamar bazai bari ba.
Daga can saman bene Mairo ta yaye labulen dakinta don iska ta shigo. Nan ta hango su. Ta kurawa Amir ido.
Bayan muguwar ramar da yayi, ya bar lallausar kasumba mara tsari ta cika fuskarshi, abinki da mai yawan
gargasa. Sannan ya saya kwayar idon shi cikin ‘dark-spaces’ wanda ya hana mata gano halin da kwayar idanun
shi ke ciki.
Karan hancin ya kara fitowa, zirit, kamar karas. Wani irin so na fizgarta. Ta saki labulen a hankali ta koma da
baya ta fada a gadonta. Tana mai fidda numfashi da sauri-da-sauri. INAMA ACE…….hannun agogo zai dawo
baya???
***
Washegari suka koma Malaysia. Mairo ta fara karatunta cikin nasara, tana barin yaran a gida wurin mai
rainonsu da yake an fara ba su madara. Kafin su cika watanni tara suna gudunsu ko’ina, musamman Alh.
Abdurrahman ya bude mata ‘account’ a nan ‘Kuala-Lampur’ duk wata yana sako mata makudan kudi na fita
hankali, don lalurorinta da kula da ‘yan jikokinsa.
Bayan kuma ba abin da Ambassada ya rage su da shi, ga na Yaya Habibu. Gaba da baya gata ya lullube Mairo
da ‘ya’yanta, abin sai godiyar Allah.
Shekaru ukku cif, wadanda suka yi dai-dai da cikarta shekaru talatin a duniya, da kwalin digiri, master, da
digiri na kololuwa.
Dr. Maryam Muhammad Bedi, ta tattaro ta dawo gida Najeriya a garin Abuja, zuwa lokacin Habibu ya yi ficce,
bankin ‘Habib Bank’ ya samu habaka zuwa ‘branches’ a dukkan ‘thirty six states’ da muke da su a gida
Najeriya, kamar yadda Amiru Abdurrahman ya yi fata. Yau ga ci gaban ya samu, ba tare da Amiru ba.
A wannan ranar da ake (ten-year anniversary) na cikar bankin shekaru goma da kafuwa, Habibu kuka yake,
maimakon ya yi farin ciki.
A yayin da al’ummar taron suka dauka kukan farin ciki yake yi, amma shi kadai yasan dalilin kukansa, wanda
bai wuce na alhinin samuwar cigaban shikadai, ba tare da Amiru ba.
A kalaminshi na karshe, bayan ya yiwa mahalarta taron godiya mara iyaka. Ya ce,
“Ya tafi ya bar bankin da kewa, bayan shi ya kirkireshi. Ya bar bankin da babban gibin da har gobe bai cike ba.
Na kuma tabbata har abada ba zai cike ba. Sakamakon dumbin ALHERINSA gare ni. A yau na tashi daga
mamallakin ‘Habib Bank’, na kyautar da shi ga ‘ya’yan AMEERU ABDURRAHMAN GAYA”.
Amiru ya daga ido yana kallon shi, extremely puzzled! To haka Alh. Abdurrahman. Ashe wannan shine kudurin
da Habibu yace yana dashi kenan akan bankin, ya ki yarda amaida hannun jarin Amiru cikin bankin?
Ya sanya hannu cikin takardu, lauyoyi suka diba, su ma suka rattaba hannu. Sannan ya ce,
“as a servant, zan ci gaba da juya musu dukiyarsu har zuwa girmansu”.
Hajiya ma ta dauko duk takardun dukiyar Amiru dake tare da ita, ta danka mishi. Ya hada dana wajen Habibu
ya adana a bankin. A wannan ranar Habibu yayi kuka, kawai sabida tausayin AMEERU. Don gabadaya
rayuwarshi ta canza ‘completely’ ta zama ‘no meaning…’ kamar yadda ya fadawa Mairo a baya.
“My life has no meaning……idan ba tareda ke ba”.
***
Habibu ya watsa mata takardun neman aiki, a manyan jami’o’inmu, tun daga Ile-Ife, Ahmadu Bello, Nsukka,
Bayero, Lasu da sauransu, ba don neman kudi ba, sai don al’ummar Najeriya su amfana da ilimin da ta wanzar
da rayuwarta tana nema, don su amfana.
Ba da jimawa ba jami’o’i har biyar suka dauke ta, ciki kuwa har da jami’ar Abuja, wadanda ta bari a baya.
Amma ta zavi BAYERO domin a ganinta al’ummar Kano su ne al’ummarta.
Habibu bai takura mata da zancen aure ba, ko tayin ta koma gidan Amiru. Sai dai shima yana ganin lokacin
yayi daya kamata a maidawa Amiru matarsa sabida yadda zawarawa manya-manyan kusoshi ke yi mishi
rubdugu, a gida ne ko ofis. Alh. Abdurrahman ya fara tsawatar mata da cewa, ba zata koma Kano ba har sai
ta fidda miji ta yi aure.
Sai ta sa musu kuka tana rokonsu, kada su kara yi mata zancen aure, idan ba so suke ita ma CIWON ZUCIYAr
ya kamata ba. Me zata yi da wani da namiji ba Amiru ba? Me zata nema a jikin wani namiji bayan Amiru?
Amiru yasa ta raina sauran maza, ta yadda har basa burgeta, duk ilminsu da mukamin su kuwa.
Gashi da alama Daddy baya son komen nasu. Tunda koda wasa bai tava furtawa ba. Itama kuma tunda
hakane bazata tava nuna tana son komawar ba, koda hakan na nufin ta auri wani ne ba shi ba!
Alh. Abdurrahman ya ce,
“Aure ya zama dole Mairo, domin shi ne cikar kima, mutumci da darajar diya mace. Duka wadannan kwalayen
naki aikin banza ne idan babu aure”.
Ta yi masa alkawarin su barta ta fara aikinta, a hankali za ta zavi wanda hankalinta ya kwanta da shi. Ya so ya
karve yaran, amma ta roke shi ya bar mata, zuwa wani dan lokaci kalilan, don suna debe mata kewa.
Gida guda suka bata cikin ‘new site’, suka tare ita da ‘ya’yanta da mai rainonsu, mai suna Lami. A lokacin
Lawan da Ahmad ‘ya’yan Baffa suna karatu a Bayeron, sai suma suka dawo gidan suna zaune a baskwata.
Baffa yana zuwa duba su akai-akai, su ma suna zuwa idan sun sami lokaci. Mairo ta fara ‘lecturing’ a
‘department of sociology’ cikin nasara da sanin makamar aiki. Ta sanya yaranta a ‘staff-school’ kullum su
Lawan suna kaisu su dauko su, da yamma kuma su kaisu islamiyya da ke nan cikin ‘New-site’.
Sannan ta soma rubuce-rubuce akan fannin da ta ke karantarwa, wanda ya kaita ga matakin zama ‘proffessor’
cikin dan lokaci kalilan.
Kyawunta, zurfin iliminta, sakin fuskarta da yawan taimakonta ga dalibanta, ya sanya ta zamo abar so ga
dalibanta. Sai dai fa kowa yana bin kwakkwafi ya yi mamaki idan aka ce ba ta da aure. Sukan ce kyakkyawar
mace kamar wannan ace ba ta da aure, ai abin mamaki ne sosai. Sannan kallo daya zaka yi mata ka tabbatar
ba da wannan aikin ta ke cin abinci ba. Tana dai yi ne don ra’ayi, amma ba don neman wani abu wai shi ‘kudi’
ba.
Proffessor Maryam Bedi, ta zamo daya daga cikin malaman da ake ji da su a jami’ar Bayero, ko sabida
karyayyen harshenta na Turawan America zallah. Don haka da yawa suke bin kwakkwafi akan rayuwarta, har
su san inda ta samo wannan ‘background’ din. Wani dalibinta ya soma rubutu a kanta, sai dai duk yadda ya so
ya ji tana da aure ko ba ta da shi, ba ta bada wannan damar ba.
Dr. Mairo ta shiryawa dalibanta masu fita a wannan shekarar ‘conference’ mai taken, “YADDA ZA A GYARA
AL’ADA TA YI DAI-DAI DA ADDINI” Wanda take so Mai girma sabon V.C ya halarta. Don haka ta je ta nemi
‘appointment’ na ganin V.C a ofishinsa. Aka sanya ta cikin jerin wadanda za su ga V.C a safiyar washegari.
Da ta dawo gida ta tarar Lawan ya dawo da su Habib, Amir yana kwance shiru cikin kujera ba kamar yadda ya
ke ba. Ta dora hannu a kanshi, zafi rau, Lawan ya ce.
“Amir ba ya jin dadi tunda safe”.
Ta ce
“Za mu je asibiti da safe, idan na ba shi ‘paracetamol’ zazzavin bai sauka ba”.
Ta dauko ‘paracetamol’ cikin ‘first-aid bod’ dinta ta ba shi da dan kankanin cokali. Har zuwa washegari
zazzabin bai sauka ba. Ga shi kuma tana da ‘appointment’ na ganin V.C, don haka ta sa yaran a bayan mota
suka nufi cikin makaranta da zummar idan ta ga V.C sai ta wuce da su asibiti, don mawuyaci ne daya ya yi
ciwo dan uwansa bai kama ba.
Ba ta barsu a mota ba, sanya su ta yi a gaba suka soma taka matattakala wadda zata sada su da ofishin V.C.
Mutum biyu ne a gabanta, sai da ta jira suka fito, sannan ta kama hannun Habib da Amir suka sanya kai cikin
ofishin, bakinta yana mai furta sassanyar sallama.
Ya juya baya yana zakulo wasu takardu cikin loka. Idanunshi saye cikin farin gilashi, sanye cikin farar shadda
‘edcelsior’ dinkin Muhammed. Hular kanshi na aje bisa teburinshi.
Gaban Mairo ya yi wani irin mugun faduwa, takardun da ke hannunta suka kwace suka watse a kasa. Amir ya
tsugunna yana tsince mata. Shi kuwa Habib tattakawa yakeyi da cambos dinsa.
Ko mutuwa ta yi ta dawo, ba zata mance surar UNCLE JUNAID ba, wanda ke tsaye nan a gabanta. Sai dai
wannan Junaidun, ya sha ban-ban da wanda ta sani shekaru goma a baya. Wannan cikakken magidanci ne, da
yasha gwagwarmayar rayuwar neman ilmi cikin fanninnika daban-daban, ba dan saurayi Junaid Galadanci ba.
Duk da alamun shekaru da suka hau kansa, har yanzu yana nan a Junaidunsa da ta sani, ma’abocin zati da
kamala, gami da kwarjini bayyananne daga Sarkin halitta. Ta rasa cikin halin da ta samu kanta, rudewa ce ko
gigicewa ce? A’a, ko kuwa gaba daya makuwa zata ce ta yi?
Ta juya da baya–da-baya zata bar ofishin, ya juyo a hankali ya dubi mai shigowa.
“Mairo!”
Maironshi da a kullum ta ke zuwa a farke, ko cikin mafarkinshi. Mairon da dai-dai da rana daya cikin shekaru
goma sha shidda, zuciya ba ta tava hutawa da kaunarta ba. Ruhi bai bar mafarkinta ba, haka tunani bai taba
kuskuren manta ta ba.
Ya dago Habib ya dauke shi tare da kama hannun Amir ya zauna a kujerar da mutane suke zama don ganawa
da shi. Cikin wata irin kassararriyar murya, ya ce.
“Ya ya za ki koma? Ko ba ke ce ‘Proffessor Maryam Bedin ba?”
Ta ja tunga a jikin kofa, ba tare da ta juyo ba. Ita bata fita ba, ita bata juyo ba. Hannunta jikin marikin kofa, ta
ce
“Ni ce”.
Ya ce
“To mene ne ajandar?”
Ta ce
“Na zo neman alfarmar V.C ya samu halartar ‘conference’ dina ne”.
Ya yi murmushi yana dauke da Amir ya tako har inda ta ke tsaye. Wani irin sassanyan kamshi da ba zata ce ko
na wanne turare ne ba a duk iya sanin da ta yi wa turare ya kassara mata gavvai.
“Na kasance ma’abocin son ‘twins’ Dr. Mairo, ko za ki bani aronsu? Na dawo miki da su bayan awanni goma
sha biyu?”
Wannan karon ne ta juyo ta dube shi, wasu kibbau na tsohuwar soyayya suka soki idanun kowannensu.
Tsohon tsimi ya tashi, wanda ya yi sandin tashin tsigogin jikin kowannensu. Da kyar ba tare da ta sake yarda
sun hada ido ba, ta ce.
“Idan iyalinka suka tambaye ka ina ka samo su mai girma V.C me zaka ce musu?”
Babu vata lokaci, ya ce da ita.
“Ya’yana ne, wadanda Mairon Gurin-Gawa ta haifa mini……………”
Kuka ya kece mata, don haka da gudu ta fice daga ofishin tana ji a ranta, ta fasa yin ‘conference’ din, tunda shi
ne ya yi sanadin da ya taso da tsohon gyambon da ya dade da warkewa a zuciyarta.
Gidan Baffa ta wuce kai tsaye, ta nufi dakin Habiba ta kwanta tana sakin ajiyar zuciya mai nauyi. Ta yi juyi a
lallausan gadon Habiba tana tariyo abinda ya faru cikin ‘yan mintina kalilan.
Baffa ya shigo dakin ya zauna a kujera yana fuskantarta, ta goge hawayenta, ya ce.
“Me ya faru? Ke dai har gobe abun kuka ba shi da wuya a wurinki?
Yanzun nan Habiba ta yi min waya ta ce, kin shigo da gudu kina kuka. Idan ka girma sai kasan ka girma, ka
koyi dauriya da juriya irin ta manya. Ba akan kowanne kankanin abu ka vare baki ka yi ta kuka a gaban
mutane ba”.
Ta yi murmushi tana goge hawayen idanunta, ta ce.
“Baffa, Uncle Junaidu na gani, bayan wucewar shekaru goma. Ya tuna min da abubuwa da dama da suka faru
cikin rayuwata, shine dalilin kukana, domin na tuna abubuwa da dama da yanayin shekaru da cigaban rayuwa
ba su sani na manta ba”.
Ya ce,
“kwanannan naji a labarai anyi ‘appointing’ din shi matsayin shugaban jami’ar Bayero ai. Har yau har gobe
kuma bai fasa zuwa gidan nan yana gaishe ni ba, bai fasa yi min manya-manyan alhairori ba. Sannan son ki
har yau bai barshi ba.
Ban tava ganin ‘SOYAYYAH’ irin ta Junaidu ba. Don haka ni ma har gobe ban fasa yi mishi addu’ar budi da
nasarar rayuwa ba”.
Mairo ta cika da mamakin jin cewa Uncle Junaidu na zuwa wajen Baffa har yau. Amma koda wasa Baffan bai
tava gaya mata ba. Ba ta gama mamakinta ba su Habib suka shigo suna ta tsalle, kowannensu rike da kit-kit
da leda fal ‘choculates’ suka fada jikinta.
“Mummy mun dawo… Daddy yana gaishe ki”.
Sai Baffa ya tashi ya fita, ya tarbi Junaid a dakin bakinshi.
Habiba ta shigo dauke da kulolin abinci. Su Amir suka makale ta suna ta ba ta labarin inda Daddy ya kai su.
Ta ce,
“Wai wane ne wannan Daddyn?”
Amir ya ce
“Daddyn Mummy ne”.
Mairo ta ce
“Rabu da shirmen su Mama, shugaban jami’armu ne”.
Habiba ta yi murmushi ta ce.
“To ko da shi za a yi ne?”
Ta yi shiru ta daure fuska bata bata amsa ba. Don ba abin da ta tsana a rayuwarta irin a yi mata zancen aure.
Baffa ya dawo dakin yana murmushi, ya same ta tana cin abinci.
Ya ce
“Idan kin kare sai ki je ku gaisa da Alhaji Junaidun. Daga nan ya ce yana so zai kai Amir asibiti, don ya ga
alamun ba shi da lafiya”.
Matsayin Uncle Junaidun da kimarshi da ke zuciyarta, ya fi gaban ta ce ba zata je ba. Baffa ya ci gaba da yi
mata nasiha mai sanyaya zuciya da sanya imani, akan lokaci ya yi da ya kamata ta tsaida hankalinta wuri guda
ta yi aure, domin cikar mutuncinta a duniya da lahira. Tunda Amiru da Daddynshi basa bukatar komen.
Ta yi sallama a kofar dakin, yana zaune cikin kujerun (leather) da suka yi wa dakin kawanya, Habib da Amir
akan cinyoyinsa, yana ta haba-haba da su kamar ya maishe su cikinsa. Ya dago idanunshi da suka yi fari sol,
yana dubanta.
A zahiri Maironshi ce, sai dai fa wannan Mairon babbar mace ce ‘yar shekaru talatin da doriya, wadda kuma a
idanunka da kiyasinka ba zata fi shekaru ashirin da biyar ba.
Wannan bakauyar da aka kawo mishi kafafuwanta jawur cikin lalle, fatar kamar shuni, yau idan ka dube ta,
tsammani zaka yi Balarabiyar Omman ce, ba wai ‘yar asalin kauyen Gurin-Gawa ba.
Kallonta ya ke, kallon da ke nufin al’amura da dama. Ita ma kallonshi ta ke, kallon da ke tuna mata da
al’amura da dama. Da gaske Uncle Junaidunta ne, sai dai wannan ya kara yi mata GiRMA. Ta TUNA BAYA… ta
tuno ALHERInsa gare ta, ta tuno SIRADIN RAYUWArta, ta yi ALKAWARI ko BAYAN RANTA matsayinshi ba zai
tava canjawa daga zuciyarta ba. Cikin muryar GIRMA ya ce.
“Mairo, ina Amiru Abdurrahman?”
Ta kai gefen mayafin abayarta ta dauke wasu siraran hawaye da suka kawo mata zarya. A hankali tace
“mun rabu!”
Duk suka yi shiru na ‘yan dakikai. Can kuma ta kawar da shirun da cewa.
“How comes kai ne sabon V.C dinmu, amma ban tava sani ba?”
Shi ma ya yi murmushi ya ce.
“ni nasan kina cikin ‘proffessors’ saidai ban tabbatar ba, sannan ban tava tunanin ba kya tare da maigidanki
ba, a wane dalili zan nemeki? Sannan bani da tabbacin ke din ce ko ‘namesake’ dinki ce, na dai ga sunan da ya
tsayamin arai ‘among the proffessors’,
Sannan ai ban dade ba ai, banyi dadewar da zaki san ina cikin makarantar ba” tace “haka ne”. Ta sunkuyar da
kai kafin ta dago ta sake cewa
“Ikon Allah kawai”.
“Ni ma sai ki dauke shi a hakan, wato kudurar Allah, ta fi ga haka”.
Ta jinjina kai, ta ce
“Kwarai kuwa”.
Suka maida idanunsu akan Habib da Amir, wadanda ke ta dabdalarsu cikin dakin, dukkaninsu sai suka yi
murmushi, yaran suka burge su.
“Kuruciyarsu na da ban sha’awa”.
Ya fada a zuci, bai san cewa a fili yake fadi ba.
“Kamar kuruciyar Mairo, Mairon Baba da Inna, Mairon Kausar da Nabilah……..”
Ta yi dariya ta juyar da kanta. Wani ala’amari mai girma na cin zuciyarta. Sai dai ba irin wanda take ji a tsohon
mijin ta ba. Ya kura mata ido, zuciyarshi na harbawa.
“Ina labarin Nabilah da Yaya Habibu?”
“Nabilah tana nan Kano, ‘ya’yanta biyar. Yaya Habibu yana Abuja”.
“Nima na yi aure Mairo. A lokacinda na riga na sallamawa zuciyata cewa na rasa ki, bazan same ki ba, kin riga
kin yimin nisa, kin zama matar wani na. Ina da ‘ya’ya biyu, tareda ‘yar uwata Ikhlas. Sai dai har wannan
lokacin da tunanin Mairo nake kwana nake tashi. Sannan dashi nake ‘functioning, will you believe it?”
Ta dago fararen idanunta ta haske shi da su. Tace “sabida me Uncle?”
Babu jinkiri, babu inda-inda ya rausayar da kai ya ce
“sabida Soyayyarki Mairo!
Soyayyar da na ke yi miki a wancan lokacin Mairo, ta zarta hankali, ta zarta duk wani kokarin hankali na ya
fassarata. Mahaukaciyar soyayya ce Mairo, wadda ta makantar da ni daga daga ido na dubi sauran mata. Ta
dakusar da hasken mata ta Ikhlas daga cikin idanuna.
Na tabbatar tunda na rasa Mairo, to bazan samu makwafinta ba. Don haka ne Hajiya tasha wuya da fari
kamin inyi aure. Don nasan ko na yi, to bazan baiwa matar hakkokin da addini ya ce na ba ta ba. Ba zan iya
sallama mata zuciya da gangar jikina ba”.
Ya taso ya tsugunna a gabanta, yana so su hada ido, amma ta ki hakan. Ya dora hannunshi akan tafin kafarta.
Ta lumshe ido a hankali ta bude su akan yatsun hannunshi da ke bisa tafin kafarta. Ya dauke hannunshi ya
zauna sosai a gabanta, ya ci gaba da cewa.
“Hajiyata ta shiga tashin hankali mai yawa, ta yi kuka, ta yi rokon duniya akan na yi aure, na kasa Mairo.
Daga baya sai malamai ta sa suke yi min rokon Allah, sun tabbatar mata da zan yi aure, sai dai da sauran
LOKACI, tunda zuwa yake. Daga baya sai ta koma nasiha, amma zuciyata ta riga ta bushe. Na tabbatar mata
idan dai ba so ta ke na auri matar na dinga daukan alhakinta ba, to ta kyale ni.
Haka ta hakura ta zuba min ido, amma ta ce ba ta fasa yi min addu’a ba. A yau ina da yakinin Allah Ya amsa
addu’arta. For the first time da na ke ji a jikina LOKACI ya zo da zan yi auren dana keso ba irin na Ikhlas da ya
zamto hadin iayayen mu ba. Wanda akayi ba tareda anyi shawara dani ba.
Ikhlas diyar kanin mahaifina ce da Hajiya ta nema min aure bayan na kammala phD dina. A yanzu haka muna
da Maryam (namesake) dinki da Sabir.
Yau ne na ji wani ‘feeling’ a zuciya da gangar jikina, mai tuna min da cewa nima namiji ne KAMAR SAURAN
MAZA. Wadanda ke da buri a rayuwa, da kuma ‘hope’ (fatan) cikar burin nasu. Shin za ki tallafe ni Mairo? Ki
auri tsoho in his fourteeth?”
Hawaye na gudu a kundukukinta, ta ce.
“Uncle Junaidu idan ka kira kanka ‘tsoho’ ni kuma na kira kaina me? Tsohuwa (second hand) ko bazawara…?”
Ya yi saurin kai hannu ya toshe mata baki.
“Ni har gobe a Maironki na sanki, koda kuwa ace ke kika haife B.U.K baki dayanta……”
Ta janye hannunshi daga bakinta, ta ce.
“Idan haka ne, ni ma har gobe a Uncle Junaidu na sanka, bana son kara jin wannan kalmar ta fito daga
bakinka ‘tsoho’.
Ya yi murmushi, ya ce.
“Da dai ana sakewa tuwo suna ne Mairo…”
Ta ce
“Ni ma ban ce a sake masa ba, a barshi a tuwonsa, don haka zauna a Uncle Junaidunka ba V.C Junaid ba, na
zauna a Mairona…….”
Suka bi junansu da kallo, kallon yarda, so da kauna da aminci. Gaskiyar masu iya magana da suka ce, ‘Soyayya
ba ta tsufa, sai dai msoyan su tsufa’. Don haka sai mu bi JUNAID da MAIRO da fatan
ALHERI.
***
Ta dauko biro da takarda ta dora mishi akan cinyarshi. Ya manta yadda ake sarrafa alkalami, har ya bada
kalma, kalma ta bada jumla balle ya rubuta mata abin da ta bukatan. Ta daka mishi tsawa mai firgitarwa, ta
ce.
“Zaka bi umarnina ko ka zabi Mairo a kaina?”
Cikin sarkewar harshe ya ce.
“Na zabe ki Hajiya,……. wallahi na zabe ki”.
Ta ce
“To rubuta ka ba ni”.
Yatsun hannunshi suna karkarwa ya rubuta abin da bai san me ya rubuta ba. Ya mika mata, ta duba ta
tabbatar ya rubuta din, sai dai ita kanta ta kasa karanta wannan cakudadden rubutun. Ya mike ba tare da
yana ganin abin da ke gabanshi ba, har ya tarar da kofar dakin Mairo.
Durkushe ta ke a tsakiyar dakinta tana kelayo wani irin koren amai fatau kamar zata amayar da ‘ya’yan
hanjinta. Ya isa gare ta da gudu ya tallafe ta. Ta kuwa sake kelayo mishi wani koren aman a farar sassalkar
shaddarshi. Wannan bai dame shi ba kamar mugun zafin da ya ji jikinta ya dauka, kamar an jefata a wuta.
Babu bata lokaci ya sunkuceta ya yi mota da ita. Bai shimfideta a ko’ina ba sai a ofishin Dr. Fredrick, ko nurses
da suka so su taimaka masa wajen daukarta a keken tura marassa lafiya, bai karbi taimakon nasu ba.
Dr. Fredrick ya dora mata ‘drip’ sannan ya shiga bincike a kanta. Zuwa can kuma ya ba ta umarnin da ta yi
mishi fitsari a roba. Bada jimawa ba sakamako ya fito na karamin ciki dan watanni biyu da ‘yan kwanaki. Ya
rasa a halin da ya tsinci kansa ciki, farin ciki zai yi? Ko kuwa hannu zai dora aka ya rusa ihu? Ba shi da sauran
buri a rayuwa, tunda ya rasa Mairo, Hajiya ta raba shi da farin cikin rayuwarshi ta hanyar da baisan ya zaiyi ya
fassara ba.
Ga shi kuma shi kansa bai san abin da ya rubuta ba, don haka bai samu kanshi da yin murna da abin da ake
neman samuwarshi shekara da shekaru ba, wanda kuma rashinshi ne silar duk kasancewarshi cikin halin da
yake ciki a halin yanzu, dama wanda ya gabata.
Ina amfanin ‘ya’yan ba tare da uwarsu ba? Ba dan Mairo yake so ba, ita Mairon yake so kanta, ba abin da za
ta haifa ba. Da ba Hajiya ce ta haife shi ba, cewa zai yi ba ta kaunarsa…….
A tsaye yake jingine da garu, ya harde hannayenshi a bayanshi. Idanun shi a rufe. Numfashi ya soma yi mishi
wuyar shaka. Idan ya tuno shi da Mairo shi ke nan? Yanzu ta zama haramiyarshi? Ga albarkar haihuwa Allah
ya kawo, sai hawayen su sake shatata.
Kafin Dr. Fredrick ya dago daga kan Mairo, Amiru ya sulale a tsakar ofishinsa, babu alamun numfashi ko
kankani a tare da shi. Ya danna wani abu akan tebur dinsa, likitoci biyu da ma’aikatan jinya suka bayyana a
ofishin cikin sauri. Suka kwashe shi suka aza bisa gado, kasancewar akwai ‘file’ dinshi tare da su suka shiga
kokari don ceto numfashinsa.
Dr. Fredrick ya dauki waya cikin aljihunshi ya kira Alh. Abdurrahman. Ko kafin ya iso the condition has become
worst! Ya gamu da abin da suka kira ‘heart stroke’, zuciyarshi sauran kiris ta buga, don haka yana isowa ya
nemi da su hada mishi ‘report’ din komai zai fitar da shi New York.
Duk inda hankalin Daddy ya ke idan ya yi dubu to ya tashi. Bai nemi kowa da zancen ba, sai da ya kammala
shirye-shiryensa sannan ya nemi Habibu a waya ya sanar da shi asibitin da suke a New York.
Don haka a washegari Habibun ya yi shiri shi ma ya bi su, ya bar Dina cikin damuwa mai yawa. Hankalinshi ya
yi matukar tashi da ganin halin da aminin nashi ke ciki, bai san inda kansa yake ba, baya shaida kowa, yana
cikin injina rankatakaf, kafafunshi ne kawai ba a sanya cikin inji ba.
Kwanan Mairo biyu a asibitinsu Dr. Fredrick yana sanya mata karin ruwa sannan ya sallame ta. Babu waya
tare da ita don haka shi Dr. ya kira Hajiya ya ke sanar da ita a zo a tafi da Mairo ta ji sauki. Hajiya ta ce
“Ina Amirun?”
Dr. ya tuna umarnin da Alh. Abdurrahman ya ba shi, na cewa kada ya sake ya sanar da kowa dan shi ba shi da
lafiya ko ya tafi da shi wani wuri. Don haka ya ce da ita yana tare da Alhaji tunda ya kawo ta bai dawo ba.
Hajiya ta ce, ya ce da Mairon ta jirata ga ta nan zuwa.
Mintuna ashirin suka shude, Mairo ta yi zugum cikin tunanin halin da mijinta ke ciki, tun faduwar da ya yi
akan idonta ba ta kara ganin shi ba, tun sanda likitoci suka yi waje da shi. Ta soma yi mishi addu’a cikin ranta
cewa koma mene ne sanadin ciwonshi to ya kasance mai sauki ne.
Dr. Fredrick bai kara fada mata wani abu akan Amiru ba, baya ga cewa ba shi da lafiya. Hajiya ta banko kofar
dakin ta shigo, babu ko sallama, dai-dai lokacin da Dr. Fred ya sawo kai zai shigo. Ta dauko takarda cikin
jakarta ta dora mata akan cinyarta. Ta ce.
“Yadda kika sa Amiru ya saki Hanan, to kema ga naki tikitin nan. Amiru ya sake ki! Ki fadawa Habibu idan a
tafe yake, ni a can na kwan!! Kada ki sake na kara ganin farar kafarki a gidana, duk wata allurarki da ke cikin
gidan na aunata cikin akori-kura, an kai muku tsiyarku, matsiyatan banza. Hanan na zabawa Amiru, matsayin
matar aure, kuma da ita zai zauna don haka sai ki san inda dare ya yi miki ba dai GIDAN AMIRU BA!”
Ta juya ta fita, daga Mairo har Dr. Fredrick suka bi ta da kallo cike da wasu-wasin anya lafiyarta? Don kwatakwata basu fahimci kan zancenta ba, balle shi da ba ya jin harshen Hausa. Mairo ta dawo da idanunta akan
takardar da Hajiya ta aje mata bisa cinyarta.
“Na saki matata Maryam saki daya… ba da son raina ba… ..” Sa hannun
Amiru Abdurrahman Gaya.
“Daga Allah muke! Kuma gare Shi za mu koma!!”
Abinda Mairo ta fada ke nan a fili da boye, kafin wasu irin dunkulallun hawaye su mirgino a kundukukinta.
‘Ya’yan hanjinta suka dunkule waje daya, cikinta ya murda jini ya kece kamar da bakin kwarya. Ta yi baya
luuu…! Ta fadi akan dandaryar kasa, ba ta kara banbance abin da ke faruwa cikin duniyar ba.
***
Dr. Fredrick, Dr. Ma’u, da sauran likitoci ne tsaye a kanta, a lokacin da ta farfado, kowanne yana aikinsa cikin
kwarewa da sanin makamar aiki. Ga ledojin jini da na ruwa duka ana kara mata. A lokacin ne abin da ta
karanta cikin takardar ya soma dawowa cikin kwakwalwarta.
Da gaske ne Amiru ya sake ta! Wannan sa-hannun nashi ne ba na kowa ba.
Wasu dumammun hawaye suka soma fito daga idanunta, Dr. Fred ya soma ba ta baki, yana cewa ta yi hakuri,
ta dauki komai ya faru da ita da sauki idan har tana son dan cikinta ya zauna, wanda ke gab da ficewa. Ya kara
da cewa ta ba shi wata lamba ya kirawo mata wani, duk da bai san me Hajiya ta fada mata ba, ya lura ba abin
arziki ba ne.
Tana kuka ta ce, ita kawai ya kai ta gidan Yayanta. Ya ce, ba zai sallame ta ba, sai cikin jikinta ya zauna sosai,
don haka ta ba shi lambar Dina.
Karfe hudu na yammacin ranar Dina ta iso tare da babban danta Muhammad, hankalinta a masifar tashe.
Mairo tana ganinta ta fada jikinta ta fashe da kukan da ke cin ranta, Dina ma kuka ta ke tana fyacewa, don
yanzu suka yi waya da Habibu, yana kuka riris kamar ba namiji ba, ya ke fada mata rayuwar Amiru sai wani
babban ikon Allah.
Sai ta dauka kukan da Mairo ke yi kenan, wadda ita bata san abin da ke faruwa da Amirun ba.
Ta ce
“Ki yi hakuri, ki kwantar da hankalinki Mairo, da yardar Ubangiji, Allah zai ba shi lafiya”.
Mairo ta saki Dina, hawaye ba su bar gudu a kundukukinta ba. Ta dauko takarda karkashin filonta ta ba ta.
Cike da mamaki Dina ta warware takardar ta karanta, sannan ta ninke, Allah kadai Ya san halin da ta tsinci
zuciyarta a ciki.
Tsayin mintuna goma ba ta ce komi ba. Ta yi tagumi, ta zubawa Mairo ido. At last! Akalla Hajiya ce da nasara
ba su ba! Idanunta jawur ta ce.
“Ki kwantar da hankalinki Mairo, wannan ba shi ne karshen rayuwar ba”.
Ta mike ta nufi ofishin Dr. Fredrick suka tattauna akan matsalar Mairo. A nan ne ma Dinan ta ji ciki gare ta. Ta
ce.
“Ikon Allah! Ga samu, ga rashi!!”
Dina ta fada a fili, wani kududun bakin ciki na tokare mata a zuciya.
Dr. ya ce, ta lallaba Mairo idan har ta kwantar da hankalinta ko gobe sai ya sallame ta.
Dina ta dinga jinjina al’amarin a zuciyarta. Tausayin Mairo da Amiru ya ishe ta. Ba ta ga laifinshi ba ko daya, ta
tabbata silar shigarshi cikin halin da yake ciki ke nan. Tana tausayin Mairo, kasancewar abin da ya fi muni ga
diya mace (zawarci) ya same ta a ‘yan kananan shekarunta da ba su kai ga cika talatin ba.
Da asubahin ranar juma’a Amiru ya bude ido ya ganshi rungume a kirjin mahaifinsa da amininshi Habibu a
gefe, yana mai furta Alhamdulillahillazi Ahyana….baada ma amatana wa ilaihinnushour…..”. Ya sake maida
idonshi ya lumshe. Kalmomin dake fita daga bakinshi a wannan lokacin cikin gushewar hayyaci sune ;
“Habibu ka yafe mini……. Na sake yi maka gagarumin laifi ba da son raina ba……..!!!”
Sannan ya dubi Alh. Abdurrahman hawayenshi na zirara, yace “Daddy ka taya ni bashi hakuri, abotata da shi
bata kare shi da komai ba, sai tarin tozarci da kaskanci a gareshi, alhalin shi ya kasance aboki nagari, wanda
babu kamsrsa a wannan zamanin, mai yawan uzri da sadaukarwa a gareni, wannan karon na mishi laifi mai
girma Daddy…..”.
Kallon tambaya Daddy yabi Habibu dashi, don son jin laifin me Amirun yayi masa? To shi kansa Habibun ya
shiga rudu, bai sani ba. Don haka ya sunkuyar da kanshi kasa. Kuka riris Amiru yake yi. Likitocinsa suka rufu a
kansa suna gwaje-gwajen daya dace. Suka tabbatar ayyukansu sunyi kyau lafiya ta soma samuwa. Bacin rai ne
kawai yayi masa yawa.
Saidai fa ga dukkan alamu patient din nasu na son maido musu da aiki baya, sabida yadda ya kuntata
zuciyarshi. Suka shiga bashi shawarwari masu amfani ga lafiyar shi. Wadanda idan ya bisu zai tserar da
rayuwarshi. Ciwon zuciya in ya riga ya sameka ya same ka kenan kai zaka cigaba da kula da kanka. Lafiyarka
tana hannunka su taimako kawai suke yi. Bayanin da likitocin ke masa kenan cikin tattausan lafazi, amma ta
inda suka shiga, ta nan suke fita ba sauraron su yake ba.
Habibu ya kira Dina. Zuciyarshi ta bushe rayas kamar soyayyiyar gyada marau-marau. In banda wani irin suya
da zogi, ba abin da ta ke yi. Sabida damuwar halin da aminin nashi ke ciki.
Ya sanar da ita ciwon Amiru na baya ne ya tashi suna tare dashi a New York. Don haka tashin hankali kan
tashin hankali wajen Dina yau ba’a magana. A take zazzabi ya rufeta amma bata gayawa Mairon ba.
Bayan sati biyu aka dawo da Amiru gida, ba don ya warke ba sai bisa tursasawarshi, bayan ya karbi taimako
na kwararru daga likitocinsa. Ya dage lallai a maida shi gida, zai iya jinyar kansa. Ya amince abinda ya faru da
shi, kaddara ce daga Allah!
A babban masallacin Abuja suka yi sallar juma’a shida Habib da Alh. Abdurrahman Gaya, amma shi a zaune
yayi sabida rashin karfin jikinsa. Tareda dubban al’umma daga cikin Abuja da wajenta, ciki har da Alh. Abbas,
wanda Habibu ya yankarwa tikitin jirgi ya zo, musamman don kawai yaga lafiyar Amirun. Shi Amiru kunya
bata bari ya iya hada ido da Baffan ba, duk Alh. Abdurrahman na hankalce da shi. Ya lura Amiru kunyar
Habibu da Alh. Abbas yake ji. Ko ido baya iya hadawa dasu. Baya hira dasu. Ga dukkan alamu sukuma basu
san dalili ba. Sababbin halayensa garesu sun jefa su rudani.
Hajiya Aisha ta idar da sallar azahar ke nan su Daddy suka shigo da Amiru a rirrike. Yana tsakanin kafadunsu.
Suka kwantar dashi a doguwar kujera. Ta dubi mijinta, sannan ta dubi Habibu ta maida idonta ga Amirun dake
kwance, ta tabbatar Amirun ta ne yayi wannan lalacewar cikin dan lokacin kalilan. Ta yi neman duniya ta rasa
shi tun ranar data tursasashi sakin Mairo. Bata san tare sukeda Daddy ba don tasan Daddy yayi tafiya. Sai a
lokacin Daddy ya gaya mata cewa a binciken likitoci ciwon zuciyar Amiru bai rabu dashi ba, a wancan lokacin
kwanciya yayi sabida samun kwanciyar hankali, a yanzu yazo matakin da dole a guji daga masa hankali, yana
so yasan neye matsalar Amiru daga ita da Habibu tunda Amiru ya ki gaya masa? Sannan ina Mairo?
Maimakon ta bashi amsa sai ta dora hannuwanta duka biyu aka tana kuka, ta ce.
“Kaicona, ni Aisha! Na cuci kaina!!”
Duk yadda Daddy ke lallashinta kan ta nutsu tayi masa bayani ciwo ba mutuwa bane amma ta ki, sai kuka ta
ke tana fadin ta cuci kanta. Wannan ya su su fitar da Amirun daga gidan zuwa nashi gidan. Anan Daddy da
Habibu suka ga wayam, babu Mairo babu ko allurar ta. Cikin tashin hankali Daddy ya dubi Amiru, yace
“ina Maryama?”
Ya sunkuyar da kai wani dunkulallen abu mai kama da sasari na daure kirjinsa yace “NA SAKETA Daddy!”
“What?????”
Inji Abdurrahman Gaya.
***.
Ita dai Mairo tunda tazo gidan, Yaya Habibu ya dawo daga tafiyar da yayi, tana ganinsa yana shigowa gidan
yana fita baya magana, ita ma Dinan ba ta magana, wanda ya haifarwa da su Muhammad rashin walwala,
koda yake su rabin rayuwarsu duk a makaranta suke yinta safe da yamma. Ta tabbatar bakin cikin sakin
aurenta da Amiru yayi ya taba zuciyar Yaya Habibu fiye da tunanin mai tunani. Fiyeda kintacen mai kintace.
To ita ma ai ta damu, damuwa irin wacce bazata fassaru ba, amma damuwar Yaya Habibu da Dina, tana bata
mamaki. Tana tsorata ta. Domin ta wuce hankali.
Ba tare da shawara da ita ba, Habibu ya soma yi mata shirin tafiya Malaysia gidan su Dina. A cewarshi ya
samar mata jami’ar Kuala-Lampur (inda yayi), idan ta haihu a can zata yi PhD dinta.
Ko kadan ranta ba ya son wannan tafiyar. Bata son gusawa daga kusa dasu. Su kadai take gani taji sanyi a
xuciyarta, ta ji tanada sauran masu son ta a duniya. Iyalin Abdurrahman Gaya sun sa ta a zargin kanta da
kanta da halayenta bayan rashin haihuwa. Rashin haihuwa kadai bazai sa ayi mata nnan tozarcin ba, saidai in
halayenta ma ababen kyama ne. Ta rasa dalilin da yasa ita ma ba ta jin dadin ranta, kewar mijinta da
soyayyarsa sun shafe duk wani burin da ta ciwa rayuwarta, gaba daya karatun ma ta tsaneshi. Me zata yi da
kwalayen babu Amiru mai nuna soyayya, kauna da karfafawa?
Duk da haka ba ta yi mishi musu ba, kada ya ce ta faya kulaficin mijin da ya riga ya sake ta, ko ta zauna zaman
jiran ya maida ita. Don haka ta bi umarnin shi ba tare da musu ko nuna bacin rai ba.
Habibu da Dina ne suka kai ta airport ta bi jirgin ‘MEA International’ zuwa ‘Kuala-Lampur’.
Baban Dina da kanshi da Hajiyarta suka zo suka dauketa a filin jirgi. Su Hafsat duk an yi musu aure a garuruwa
daban-daban, don haka babu kowa gaban Hajiya da Daddyn Dina.
Irin yadda Daddyn da Hajiyar ke tausayinta, sai ta ji ita ma tana tausayin kanta. Idan haka dacin mutuwar aure
yake, to ba ta fatan shi koda akan makiyarta.
Irin kulawar da Hajiyar Dina take bata ko Innarta iyakarta ke nan. Tana ganin likita akai-akai, (awo) domin
kulawa da lafiyarta da ta abin da ke cikinta.
A yau Daddy ya yi musu sallama zai wuce gida Najeriya. Hajiyar Dutsinma babu lafiya. Ashe zai je ne duba
Amiru a Abuja. Wanda ciwonshi ya kara tashi kamar bazai kai labari ba. Hajiyar Dina ta yi mishi rakiya har
bakin mota. Mairo daga saman bene inda dakinta ya ke ta bude taga tana hango su suna magana fuskokinsu
babu annuri. Kanta ya yi masifar daurewa, kada dai Hajiyar Dutsinma mutuwa ta yi shi ne Daddy zai tafi
Nigeria?
Don haka bayan fitarshi ta samu Hajiya a daki, wadda ta yi tagumi da dukkan hannuwanta biyu a bakin
gadonta. Yanayin Mairo take nazari a ‘yan kwanakin nan. Magana take ita kadai inta shiga daki. Ba dama ta
kadaice sai taji tashin sunan A.A a bakinta ko bacci take yi. Ta yanke shawarar fadawa Mairo halinda Amiru ke
ciki don ta dinga yi masa addu’a, amma ba don wani abu ba.
Mairo ta yi sallama cikin dakin, sanye da doguwar riga mai hade da hula samfurin Oman, ta zauna a gaban
Hajiyar Dina, cike da damuwa ta ce.
“Don Allah Hajiya me ya faru da Hajiyar Dutsinma ne?”
Hajiya ta ce, “Ciwon suga ke damunta, don haka Daddy zai taho da ita idan zai komo don ta samu kulawa
sosai daga kwararrun likitoci”.
Sai yanzu ne hankalinta ya kwanta da ta tabbatar Hajiyar ba mutuwa ta yi ba. Amma wannan damuwar da
kowa a gidan yake ciki tana damun ta, don ya wuce ace akan mutuwar aurenta ne kadai.
Hajiya ta dubi Mairo cikin tausayi, ta ce.
“Maryam ina so ki ba ni hankalinki, tunaninki da nutsuwarki. Nasan saki a zuciyar diya mace ba abu ne mai
sauki ba. Nasan zafin sa nasan radadin sa. Ki dauki abin da za ki ji daga bakina ba wani abu daban ba; so nake
ki yafewa Amiru duk wani kullacinsa dake ranki da zuciya daya ba tareda shi din ya sani ba, ki taya kowa
addu’ar nema masa lafiya”.
Shiru Mairo tayi, kamar ruwa ya cinye ta. Anya tabon da Amiru ya ji mata a zuci abinda zata iya yafewa ne???
Hajiya ta ce
“Amiru ya kamu da ciwon zuciya a bisa tafarkin soyayyarki. Irin ciwon da yayi kafin ya same ki, shi ya dawo
mishi a lokacin da ya rasa ki. Wato bacin rai da tashin hankalin da ya samu kanshi a ciki, a dalilin ya sake ki.
Wannan abin alfaharinki ne Mairo, mijinki na son ki, soyaya irin wadda babu a wannan karnin, kaddara ce ta
raba ku,, yana mai yarda da ke, da sa miki albarka. Na fada miki ba don komi ba, sai don ki dubi Allah ki yafe
masa, ki dinga yi mishi addu’ar samun sauki, albarkacin soyayyar sa gareki…….”.
Hajiya magana ta ke, a sanda ta lura Mairo ba ta jinta. Tun sanda ta ambaci kalmar ciwon zuciyar Ameeru ya
dawo….’ ba ta kara fahimtar abin da ke fita daga bakinta ba. Damuwoyin sun yiwa zuciya da kwakwalwar ta
yawa. Ji tayi kamar Hajiya tace Amiru ya rasu…Ji ta ke kamar ana mata ihu a cikin kwakwalwarta. Can anjima
kuma taji kamar ana gudun famfalaki a cikin kanta. Hajiya ta ga idanuwan Mairo sun birkice. Tamkar ba’a jikin
ta suke ba.
Ba karamin tsorata ta yi ba, ta soma nadamar karambaninta. Kawai sai taji Mairo ta soma yi mata sambatu.
Sambatu iri-iri.
“Don yayi aure sai ya sake ni? Nayi duk iya kokarina don ya samu kwanciyar hankali a auren da yake so yayi,
na bashi dukkan go ahead, na bashi amana da soyayya ta, na sakankance we’re to live for life! Na san Hajiya
ta daina so na tunda banna haihuwa amma ai na yarda ta aura masa mai haihuwa meyasa bazata barmu tare
ba?”
Can kuma ta kara duban Hajiya, ta ce.
“Ai Hanan din tana da kirki, ni bazan cuce ta ba! Hajiya ki mayar dani in ba ni na yi jinyar sa ba bazai mike
ba!!!”
Ta mike da sauri tayi hanyar kofa.
Hajiya sai ta sa kuka ta kamota ta rungume ta, tana tofa mata duk addu’ar da ta zo bakinta. A wannan gabar,,
tana gujewa Mairo haduwa da psychological problem kowanne iri, wanda damuwa ke yin sanadin sa.
A daren ta yi asibiti da ita, aka soma ba ta treatment din da ya dace.
Ko da Daddy ya dawo tare da Hajiyar Dutsinma a can asibitin suka isko su, sun ba ta gado sun ce za su yi
‘treating’ dinta tsayin sati biyu. In banda surutai ba abin da ta ke kwana tana yi, duk akan Amiru da
damuwarta kan halin da yake ciki, sosai Daddyn Dina ya yiwa Hajiya fada kan abinda tayi. Wani zubin kuma
sai ta sa kuka, tayi-ta-yi ba kakkautawa. Likita yana zuwa har gida yana duba Hajiyar Dutsinma don bata yarda
tazo asibiti cikin sati biyu ta warware.
Daddy Ya yiwa Habibu waya ya sanar da shi halin da Mairo ke ciki. Bayan kwanaki biyu ya iso. Tana ganinshi ta
fizgo daga gado ta rungume shi tana hararar Hajiya, ta ce.
“Ba ga shi ba Amirun kika ce ya mutu! Allah Ya isa tsakanina da ke!!” Sai ta sa kuka.
Ma’aikatan jinyar asibitin suka zo suka yi mata allura, nan da nan ta kama barci. Habibu ya yi ajiyar zuciya ya
dubi Daddy. Suka zauna a kujeru masu fuskantar Mairon suna kallonta cikin tausayi. Habibu ya kebe da
babban likita ya kara yi mishi bayanin komi.
Ya ce kada su damu, bacin rai ne da damuwa kawai ya hargitsa ta, amma da ta kare shan maganin da suka
dorata a kai zata dawo dai-dai insha Allahu.
Tsayin watanni biyu Alh. Abdurrahman na jinyar tilon dansa, ya na kwantar masa da hankali ta hanyar bashi
misalai da al’amuran rayuwa kala-kala. Don ya yaye wa kanshi damuwar daya sanyawa zuciyar shi. Yana kuma
karantar abubuwanda ke faruwa a cikin gidanshi musamman Hajiya A’isha daya digawa gundumemiyar ayar
tambaya. Sabida yadda ta fita hayyacinta da rashin lafiyar Amiru, sai surutai take mai tonawa kai asiri, wani
zubin ta hada da su Nina tace su suka angizata, ta zazzagesu tayi musu mugun kalami tana cewa sun cuce ta.
Bai tambayeta komai ba, kuma bai tambayi Amiru mai yasa ya saki Mairo ba. Wanda rayuwar sa ke hannun
Allah. Dr. Fred yana zuwa gida akai-akai yana kula dashi. Ya ki yarda a maida shi New-York. Yace da Daddy in
ma mutuwarce, to yafi so ta dauke shi a dakin da yayi rayuwa da Mairo.
A yau Ambasadan Malaysia yazo ganin sa, ta dalilin Habibu da Amiru Daddyn Dina da Alhaji Abdurrahman
suka kulla abota. Alh. Abdurrahman yayi masa kyakkyawar tarba, shikansa saida ya zubda hawaye ganin halin
da Amirun ke ciki. Ya koma Malaysia cike da alhini inda ya tarar da Mairo da tata sabuwar matsalar har yau ba
sauyi.
A wannan satin da surutan Hajiya suka ishi Alh. Abdurrahman, yayiwa ‘ya’yan shi mata gabadaya waya, na ciki
dana waje, yace yana so su hallara a ‘family meeting’ ranar asabar mai zuwa. Sannan ya kira Alh. Abdulwahab
Baban Hanan shima yace yana so Hanan tazo ranar asabar. Alhaji Abdulwahab wanda ke cike taf da fushin
sakin da Amiru yayiwa Hanan sati daya da aure ya gintse fuska yace
“ince ko lafiya? Bayan an riga an saketa?”
Daddy yace lafiya kalau, ‘meeting’ zasu yi tare da ita. Ya gaya mishi bai san abubuwanda suke faruwa a gidan
ba, yana so ya sani ne, inda halin gyara ayi gyara. Yace Hanan zata zo albarkacin ka, amma babu batun gyara.
Don dama Hanan tana da mai sonta tuni, mutunci da ‘yan uwantaka aka diba aka bawa Amiru. Tunda kuma
yace baiyi, to Allah ya hada kowa da rabonsa na ALHERI.
Jikin Daddy a masifar sanyaye, da mamakin wai itama Hanan an saketa. To shi yana ina aka yi duk wannan
kazamin aiki? Lallai Hajiya ta bashi mamaki. Ya kuma soma zargin koma menene itace ummul-haba’isi, haka
kawai za’a kashe masa Da a banza.
Habibu bai bar jinyar Amiru ba, duk da tabbacinsa na sakin Mairo da yayi. Duk da zafin hakan dake ranshi.
Duk wai wata kusan tafi wata kusan. A wurinshi ba Mairo ce ta hada shi da Amiru ba balle ta zamo silar
rabuwarsu. Allah ne ya hada su, ya sanya kaunar juna da soyayya a tsakaninsu, ba kuma zasu rabu a dalilin ta
ba. Ko ba komai Amiru ya wanke mishi zuciya da baiyi mummunan saki ba wanda Allah baya so. Yayi kokari ya
karanta hargitsatstsen rubutun ya ga saki daya ne. Kullum kafin ya fita ofis zai zo, haka in ya tashi yana nan
tare dashi har goman dare.
Amiru yana shaida kowa, amma baya magana. Sai bin kowa da ido. A ganin shi rayuwar bata cancanci a
cigaba da itaba, ba tare da abinda zuciya da gangar jiki ke so ba. In za’a bashi zabi gara mutuwa da rayuwa
babu Mairo.
Kasancewar Daddy da Habibu na kula da shan magungunan sa akan lokaci, ya sanya kullum sauki na kara
samuwa.
Daddy ya shigo falon da ‘ya’yan sa, Hajiya da Hanan ke zaune, kowanne kai a kasa. Jiki yayi la’asar babu laka.
Ita kanta Hanan ta tsorata da ganin yadda Amiru ya koma cikin dan lokaci kalilan. Sau daya ta shiga part
dinshi, tausayi bai barta ta kara komawa ba. Ko babu soyayya Amiru dan uwanta ne wanda take ji har cikin
kashi da bTa kuma alkawartawa ranta fadiwa Daddy gaskiyar duk abinda ya tambayeta ba tareda shayin
Hajiya ba, don Yaya Amiru ya samu lafiya, ya samu abinda yake so, ita tayi hakuri, ta auri Ramadan wanda ke
son ta kamar ya kashe kan shi.
Amina kadai ake jira a falon wadda bata karaso daga Switzerland ba har yanzu. Don haka ganin ana batawa
‘majority’ lokaci, akan mutum daya, Daddy ya yanke hukuncin ayi taron bada ita ba.
Ya bude taron da cewa kowa yayiwa Annabi salati goma. Ya ja doguwar addu’a suka shafa. Yasa gilashi ya
soma duban ‘ya’yanshi mata su goma sha daya da fuska mara walwala. Ya maida dubanshi ga Hajiya A’isha
yace
“Hajiya, keda Hanan kune a gidannan sanda abin ya faru, don haka ku zan fara tambaya. Yaya aka yi Amir ya
saki matansa biyu duk a lokacin daya?”
Hajiya tayi shiru, ta soma share ido da gefen mayafinta, abinda ya riga ya zame mata jiki tun ranar da aka
dawo da Amiru wai yana fama da ciwon zuciyar data yi tsammanin yayi hannun riga da shi. Tararradinta shine
idan ta rasa Amiru ina zata tsoma ranta? Mutumin da ke yi mata biyayyar da duk cikin ‘ya’yan ta babu mai yi
mata kwatankwacinta?
Mutumin da ya sadaukar da farin-cikinshi akanta. Bama wannan ba, ina zata kai hakkin Mairon da bata ci
mata ba, bata sha mata ba, biyayya take yi mata tamkar tayi mata sujjada, kawai don Allah As-samadu bai
bata haihuwar da bata isa ta baiwa kanta ba? Ta tabbatar ba komai ya kai ta yin umarnin data yi ba, bacin ran
sakin da yayiwa Hanan ne. Wadda ita bata damu ba, kamar dama jira take, yana sakinta ta hada ya-nata-yanata tayi tafiyar ta, babu ko cikakkiyar sallama. Sai yau ta ganta cikin taron da bata zata ba.
Amma ko waya Hanan bata kara yi mata ba. Gatanan da ranta da lafiyar ta ba abinda ya dameta. Sai nata dan
data jefa cikin halin ha’u’la’i. zaiyi-ba zaiyi- ba Allah masani.
Ta dubi Nina, kamar ta tsinka mata mari, domin dai ita ta kaita ga abinda bata taba tsammanin yi a rayuwarta
ba. Wato bin malaman tsafi Yarbawan Lagos, haka-kawai zasu fidda ita a imanin ta. Kukanta ya tsananta ta
kasa baiwa Daddy amsa.
Don haka ya juya akalar tambayarsa ga Hanan. Ta sunkuyar da kai ta soma fada masa duk abinda ya faru, tun
ranar da Hajiya ta aika ta zo, abubuwanda ta rinka bata wai tayiwa Amiru amfani dasu, har zuwa ranar daya
saketa, da tirkeshi data yi ya saki Mairo. Daddy ya jinjina kai cikin al’ajabi da mamaki, yaushe Hajiya ta koma
haka?
Ya ce da Hanan ya gama da ita, kuma ya gode. Kuma menene ra’ayinta kan zama da Amiru? Tana so idan
Allah Ya bashi lafiya zata dawo dakinta ne ko a’ah?
Ta sunkuyar da kai tace “ka fahimce ni Daddy. Ba wai bana son Yaya Amiru ba, amma shi wallahi-wallahi baya
so na. Matarshi kadai yake so Daddy. Kuyi kokari ku dawo mishi da abarshi cikin gaggawa in har kuna son
lafiyar shi fakat. Nikam har ga Allah na hakura, zan auri mai so na. Daman kuma babu iddarshi a kaina”.
Daddy ya sake jinjina kalamanta, yayi mata godiya ya sallameta ta fita ta koma wurin Amiru. Inda aka baro su
shida Habibu. Daddy ya dubi Hajiya cikin wani irin fushi da ‘anger’ da bata taba gani daga gareshi ba. Fuskar
shi tayi jawur abinki da bafulatani, jijiyoyin kansa sun fito rada-rada, idanunshi sun canza launi daga farare sol
zuwa jajaye. Jikinshi na tsuma, tsigar jikinshi na tashi yace
“A’isha! Hanan gaskiya ta fadi ko karya ne?”
Ta juya kai cikin tsoro da tashin hankali, nadama da yin kaico da kai, don bata taba ganin shi cikin wannan
halin ba. Tace
“batayi karya ba anyi haka. Sai dai kuskure ne da ajizanci irin na kowanne dan adam. Na tuba Alhaji na bi
Allah na bika. Sai dai komai ya faru ne da zuga da taimakon wadannan……….” Tana nuna Nina, Ni’ima da
Khalisa.
“Su suke karbo komi a Lagos wallahi ban taba zuwa ba. Don nasan zuwa wajen irin wadannan mutanen
haramun ne. Na roke ka, kada ka bari Habibu yaji wannan magana don GIRMA NA ZAI FADI A IDANUN SA don
ba iyakarta kenan ba…….”
Cikin nishi Alh. Abdurrahman yace “sai kuma me?”
Ta yarfe hawaye da majina tace
“Na sanya shi ya janye hannun jarinsa daga bankinsu shida Habibu……duk takardun dukiyar shi suna hannu
na yanzu, bari inje in dauko…”.
Tana shirin mikewa ya daga mata hannu “bayan Nina, Ni’ima da Khalisa sai kuma wa?” tace “sai mutanen
Gaya. Su suke cewa “juya” ce. Don haka ne na kulla auren shi da Hanan don ya samu ‘ya’ya kawai wallahi,
amma ba don in raba shi da matarsa ba….. kai shaida ne akan cewa tsakani da Allah ina son Mairo”.
Ya kalli Nina da Khalisa da suka yi tsuru-tsuru, jikinsu sai kyarma yake. Don sun gigice da ganin ‘tension’ din
mahaifinsu mai son su da gudun bacin ransu, tareda kyautatawa rayuwarsu tun daga yarinta har girma.
Rayyah tace “wallahi babu ruwana……” Sabah tace “wallahi babu hannu na…..” Mami tace.
“ni Daddy da ba a kasar nake ba, wallahi bani da masaniyar komai…….”.
Juyawa yayi gefensa ya fizgo wayar talbijin. Ya soma binsu yana tsula musu. Duka na tashin hankali. Da masu
ruwan, da wadanda suka ce babu ruwan su. Yana hawaye yana tafkarsu, yace
“Kun yi asara! Kun kashe auren mutumci da amana da soyayya ta gaskiya!!
Bazan yi muku baki ba. Amma kuji tsoron hakki. Kuje duniya kadai ta isheku, tunda kuma mata ne kuma aure
kuke kamar yadda Mairo ke zaman aure.
Sannan abinda kuka yiwa Mairo, kuka sa aka yi mata, zai iya faruwa da kowaccenku. Dan uwanku kuma idan
yana da hakkinku Allah zai fitar masa, muddin ya mutu bai yafe muku ba.
Kuma sai kun maimaita wannan magana agaban Habibu, sai Habibu yaji wannan maganar.
Ke kuma Hajiya ki tattara ya-naki-ya-naki ki tafi Gaya, sai na nemeki…….bana bukatar ganin ki a cikin gidana
yanzu……”. Kowa a falon kuka yake, yana rokon gafara. Basu kara tsananta kukansu ba, saida suka ji wannan
danyen hukuncin da Daddy ya zartas akan Hajiya. Suka rirrike kafafun shi suna bashi hakuri yace
“ni baku yi min komai ba. Wadanda kuka yiwa su zaku nema gafara amma ba ni ba. Sannan bazan taba sanya
baki Mairo ta dawo gidan dan uwanku ba. Tunda bakwa son ta.
Ku aura mishi duk wadda kuke so tazo ta cika muku gida da ‘ya’ya. Ko ya mutu, ko yayi rai, na barwa ALLAH!
Ku bace min da gani dabbobin banza. Hajiya ina kara gaya miki, kada in dawo in ganki cikin gida na….”.
Ya yarda wayar ya fice, yana share hawayen da suka cika mishi ido.
***
Wasa-wasa sai da Mairo ta kwashe watanni uku cur cikin wannan halin, a lokacin cikin jikinta ya fito sosai,
domin ya shiga cikin watanni na biyar.
Rannan daga ita sai Hajiyar Dutsinma a dakin, ta farka daga barci, ta kurawa silin ido, al’amuran suka soma
dawo mata tar-tar.
Ta tuna wai Amiru ya sake ta, ba tareda ta yi mishi laifin komi ba, alhalin suna tsaka da son junansu. Bayan ta
mallaka mishi duk wata soyayyarta.
Sannan ya auro Hanan, ba ta fita daga wannan bacin ran ba, ya dankara mata saki, ta tabbatar bisa
tursasawar Hajiya ne, amma Amirun ba zai taba yi mata haka akan-kanshi ba, ko giyar wake ya sha.
Tana mai sa ran bada jimawa ba za su dai-daita da mijinta ya maida ita ta zauna lafiya da Hajiya Aisha, tunda
abin da Hajiyar ta kwallafa rai, har ta tsane ta a kanshi, ga shi Allah Ya bayar.
Sai kuma ta tuno wai an fada mata ya kara kamuwa da ciwon zuciya irin wanda yayi a baya, aka samu
rayuwarshi da kyar da taimakon ta. Gashi yanzu basa tare. Kai ita ji tayi ma kamar ance ya rasu! Daga bakin
Hajiyar Dina da ba zai taba yi mata karya, ko zolaya ba.
Ta soma kuka a hankali, kukan sabo, soyayya, kauna da kewa. A tsayin zamansu na shekaru takwas, bai taba
bata mata ba, sai bisa kuskure. Soyayyar da ya wanzar da rayuwarshi a nuna mata, wani abu ne da ba zai taba
kankaruwa daga zuciyarta ba.
Tunda ya aure ta ya haramtawa kanshi sauran mata. Bai kara hada jiki da wata diya mace ba, bayan ita, har
inda yau ke motsi. Har kuwa wadda ya aura da auren sunnah. Taji wannan a bakin Hanan ba a bakinsa ba.
Duk da matakin rayuwa irin nashi, wannan bai shagaltar da shi daga rudin duniya ba.
Ta tabbata ta yi babban rashin da har abada ba zata mayar da makwafinsa ba.
Ta mika hannu ta shafi kasan mararta, inda babynshi ke kwance, yana wutsil-wutsil cikin koshin lafiya. Ta
lumshe ido a hankali, hawaye masu dumi suna zirara ta gefen idonta suna shiga cikin kunnuwanta. Ba ta
damu da ta share ba, haka zuciyarta ba ta daina kokawa ba.
A wannan halin Habibu ya tarar da ita. Ya ja kujera ya zauna yana fuskantarta. Ya ce.
“Mairo, Mairon Dina, Mairon Yaya Habibu…”
Ga mamakinshi sai ta fado jikinshi tana kuka mai tsuma zuciya. Ta ce.
“Yaya Habibu da gaske mun rasa AMEERU?”
Ya ce
“Mun rasa auren shi dai Mairo, da gaske mun rasa auren mai kaunarmu da gaskiya da amana. Amma Ameeru
yana nan a raye.
Duk wanda yace dake ya rasu, ya fada miki ne kawai don ya tayar da hankalinki. Ko kuma baki tsaya kin
saurara dai-dai ba. Amma yana gida, kwance a dakin ki. Akan gadon ki.
Kwanciyar shi ciwo da rabuwar auren ku ya barni da kewa, da katoton gibi a zuciyata. Wanda mayar da shi
wani abu ne da ba zai taba yiyuwa ba. Don haka ki dage da yi mishi addu’a. Allah ya bashi lafiya cikin
gaggawa.
To lose a friend like him, will be the GREATEST lose of all losses. To lose a husband like him, is another GREAT
loss. (rasa aboki kamar sa, ba karamar asara ba ce daga manyan asarori, kuma rasa miji kamar sa, shima
babbar asara ce.) Sai dai mu cigaba da yi mishi addu’a. Allah ya bashi lafiya.
Wannan ne kadai babbar sakayyar da zamu yi wa masoyi irinshi. Amma ba da son ranshi ya sake ki ba.
A matsayinmu na musulmi, ma’abota imani da yarda da kaddara, muna da tabbacin cewa, duk abinda ya faru
damu da sanin Allah. Shine mai sanya cuta, kuma shine mai yaye ta. Don haka muna da kyakkyawan zaton Zai
tashi kafadar Amiru, a lokacinda ya so. Ya cigaba da gudanar da al’amuran kyakkyawar rayuwarshi. Inda
rabon zaku komawa auren ku, to da yardar Allah zaku koma. Amir bai yi haka ba Mairo, sai bisa tirsasawa.
Ya kamo hannunta ya rike cikin nashi, ya ce.
“Mairo mun rasa Baba, mun rasa Inna, amma mun hakura kan ba yadda za mu yi. To haka da muka rasa auren
Amiru, zamu yi hobbasar yin tawakkali. Mu ci gaba da jure jarrabawoyin da Ubangiji ke yi mana a rayuwa, har
mu cinye jarrabawarmu.
Don haka ki yi hakuri kamar yadda na yi hakuri, iyayenshi da ‘yan uwanshi suka yi, kan halinda yake ciki. Kuma
Alhamdulillahi yana gane mutane yanzu saidai ya ki asibiti.
Hajiyar Amiru dasu Nina suna can suna ta nemanki, suna neman inda za su ganki su nemi gafarar ki sun rasa.
Ta yi nadama/sunyi nadamar abin da suka yi mana.
Yafiyarki su ke nema Mairo. Afuwata suke nema da hawayensu. Sun gurfana kan gwiwoyin su a gabana don
na yafe musu. Sannan sun samu Daddy sun bayyana mishi duk abinda suka yi mana, yayi mamaki nima nayi
mamaki, ya saba musu sosai kuma sunyi nadama ta gaskiya akan ki Mairo. Yace dasu ai ga sakayya nan sun
soma gani tun a duniya, tunda Amirun na neman rasa ransa a kanki. Wallahi Mairo tun bayan tafiyar ki ko
kofar gida Amiru bai kara takawa ba, yana gidan ki, daga dakin ki sai falon ki.
Hajiya in kin ganta a halin yanzu dole ki tausaya mata, watanta daya a Gaya ya koreta, kiris ya rage ya saketa
saida nasa baki tukunna ya hakura.
Ta ce ki yi wa Allah ki kula mata da abin da ke cikinki. Sabida na gayawa Daddy kina da ciki shikuma ya gaya
musu.
Sabida haka ki kwantar da hankalinki, don a samu daidaituwar B.P dinki, don hawan jini hatsari ne ga mai juna
biyu, kuma jininki ya hau, don haka ki taimake ni Mairo, kada kema na rasa ki………bani da Uwa, bani da Uba,
sai ke da abinda zaki haifa….”
Hawaye sharrr! Suka zubo daga idonsa.
Ta kai hannu tana share masa, ita ma nata suna zuba. Cikin rishin kuka ta ce.
“Ka daina kuka Yaya Habibu, na yi maka alkawarin zan kwantar da hankalina tunda yana raye”.
Ya ce,
“To tashi ki ci abinci, ko dan cikinki ya samu. Bai kamata ki dinga zama da yunwa ba, plzzz… Mairona!”.
Ta ce
“To ba ni in ci”.
Ya bude kular da ke gabanta, ya zuba mata faten dankalin Turawa, wanda ya ji tsokar naman kaji ya yi lugub.
Ya mika mata a faranti, ya cika tambulan da (fresh milk) mai sanyi ya mika mata. Ta karba ta soma ci sosai har
tana taune harshenta sabida yunwa.
Dina ta shigo rike da kwandon kayan abinci, suka zauna akan kilishi suna ci ita da Habibu. Mairo na kallonsu
tana raya abubuwa a ranta, wato ranar da aka kaita gidan Amiru ya takura mata sai ta ci abinci akan idonsa.
Ta kai hannu da sauri ta goge hawayen da suka kara shimfido mata, don ba ta son Yaya Habibu ya gani, ranshi
ya baci. Amma ta riga ta san kuka ta dinga yinshi kenan, har karshen rayuwarta. Tunda yanzu itada Amiru sai
dai a TUNA BAYA……Yaya zatayi da dimbin soyayyar shi data kankanewa zuciyarta????
An sallami Mairo ranar wata asabar bayan likitocinta sun tabbatar komi nata ya koma dai-dai. A lokacin
cikinta ya cika watanni shidda cif, wanda ya yi dai-dai da cikar Amiru watanni hudu yana jinya.
Suka dawo gidan su Dina, inda a washegari Habibu da Dina suka yi shirin tahowa gida Najeriya. Gidan ya rage
daga Mairon sai Hajiya da masu aiki, don Abban Dina bai cika zama ba sai a weekend, kullum yana ofis.
Bata tashi daga inda ta yi sallolin farilla guda biyar, ba tareda ta yiwa Amiru addu’ar neman lafiya daga
Ubangiji ba.
Hajiyar Dina na kula da ita yadda ya kamata, ko Innarta iyakacin kulawar da zata yi mata kenan.
Watan Hajiyar Dutsinma biyu tare da su jikinta ya yi kyau ta koma gida.
Kwanaki na mirginawa su zama watanni, har watan Aprilu ya kama, wanda shi ne EDD dinta. Sai dai Mairo ba
ta yarda anyi mata ‘scan’ ba. Ranar wata alhamis nakuda ta tashi cikin dare, haihuwa gadan-gadan. Don haka
ba da bata lokaci ba Hajiya ta tuka su da kanta suka nufi asibitin da ta ke awo, nan da nan aka karbe ta a
(labour ward), nakuda ta tsayin awanni uku cur, kan Hassan ya bullo, kamin likitocin su yi wani yunkuri, shi
ma Hussaini ya biyo dan uwansa.
Aka turota dakin hutu, Hajiya na rungume da jariran tana yi wa Allah sarkin halitta tazbihi, sabida kamar
Amiru ya yi kaki ya tofar. Sannan ‘identical twins’ irin wadanda banbacesu zai yi wuya.
Sai dai da alama Hassan kalar Babanshi ne, wato (choculate), yayin da Hussaini ya debo hasken fatar Mairo.
A take Hajiya ta yi waya ta sanar da Habibu, ya yi hamdala ya kuma nemi wayar Alh. Abdurrahman ya sanar
da shi, don haka a karshen satin suka dungumo har Hajiyar Amiru dasu Sabah suka iso Malaysia.
Farin ciki a wajen Hajiya Aisha da Alh. Abdurrahman abin ba’a cewa komi. Hajiya har da kukanta na nadama,
ga dai ‘ya’ya ba daya ba har biyu Mairo ta Haifa, duk kunyar Mairon ta isheta, ta kama ‘yan jikokin ta
rungume tana yi musu addu’a, ji take kamar Amirun ne ta rungume a ranar data haifeshi, sai dai dukkaninsu
babu mai ra’ayin a yi wani taro sai addu’a da kowa yake yi wa mahaifinsu, wanda har zuwa lokacin ke kwance
cikin halin jinya.
Yara sun ci sunan Habib da Amir, babu kuma wanda ya yarda da a sakaya. Ana kiransu da sunansu abinsu.
Bayan su Hajiya sun koma Mairo ta ci gaba da rainon ‘yan biyunta cikin koshin lafiya da taimakon (Nanny)
Bamaleshiya da Hajiya ta daukar mata.
Kamin watanni hudu sun cika sun yi kiba, sun yi bul kamar ‘yan watanni goma sabida samun kulawa da ruwan
nono isasshe. A lokacin ne kuma ‘addmission’ dinta na yin PhD ya fito a ‘university of Malaya’.
A satin da zata fara karatu, Yaya Habibu ya zo Malaysia. Yace tayi shiri suje Najeriya ta kaiwa Amiru ‘ya’yan shi
ya gansu. Don ya samu sauki har ya soma zuwa ofis. Daddy ya samo mishi aiki a CBN. Don shi Habibun bai
yarda su sake yin hadin gwiwar ba kamar yadda Daddy da Amirun suka bukata, yace saboda halin rai. Ya
kuma ce da Daddy akwai kudurin da yake dashi a kan bankin nan bada jimawa ba. Amma ba wai don yayi
fushi da abinda Hajiya tayi ba.
Mairo bata son wannan tafiyar sai don Yaya Habibu ya matsa mata. Amirun ne bata son gani, don bata son
duk wani abu da zai taba zuciyar ta a halin yanzu. Ta riga ta sanyawa zuciyarta YAKANAH (sunan littafin Takori
mai zuwa). Ta koya mata dangana, ta koya mata rayuwa ba AMIRU. Karatun ta kawai tasa a gaba, da rainon
‘ya’yan da Allah ya bata.
Lokacin da Daddy ya gayawa Amiru mairo ta haihu har ‘ya’ya biyu, bai nuna wani farin-ciki ba, don yana
kullace da Mairo, da bata taba zuwa ta dubashi ba har yayi ciwon sa da jinyarsa ya gama ya gaji ya mike. Bashi
da wani sauran buri a rayuwa, tunda ya rasa Mairo.
Sannan Daddy yace babu maganar biko, ba zancen kome, don bai yarda sun gama horuwa ba, Amirun yayi ta
zama a gwauro, ko su aura masa mai haihuwa. Ya kuma ce da Amiru in zai mike ya fuskanci sabuwar rayuwa
to ya mike, in bazai mike ba, yayi ta kwanciya soyayya ta kassara shi. Don shima yana da nasa laifin. Na kin
gaya masa duk abinda ke faruwa saboda tsoro da son Hajiyarsa. Har saida komai ya lalace. Daddy yace
“ita tana son ka ta lalata maka rayuwa?”
A fannin ita Hajiya, zaman Amirun haka babu iyali ya fara damun ta. Tana so tayi zancen biko a maida aure
tunda saki daya ne, babu fuska daga Habibu da Daddy. Don haka tasa ido, don ganin hukuncin da suke nufi.
Saidaifa rayuwar Amiru ta canza sosai. Ya zama babu murmushi babu far’a sai ‘dark-spaces’ kusan koyaushe
make a fuskarsa. Sai ayyukan dake gabansa. Ya kudire a ransa idan ba Daddy ne da kansa ya bude baki yace
ya maida Mairo ba da bakinsa, to ya hakura da ita har karshen rayuwarsa.
Yamma lis, suka iso filin jirgin saman Abuja. Dina dasu Muhammad sukaje tareda direba filin jirgin suka dauko
su. Suna zuwa gida Dina ta karbi yaran tayi musu wanka ta shiryasu da kaya na alfarma. Habibu ya dura su a
mota tareda su Muhamnmad da mai rainon su Esta da suka taho da ita daga Malaysia sai Asokoro.
Kasancewar ranar Lahadi ce, Daddy yana gida shida Amiru a karamin falonsa, suna aiki cikin takardu da
kwamfuta. Habibu ya yi sallama rike da mai sunan sa yayinda Muhammad ya biyo bayansa dauke da Amir. Ya
saki takardun hannunsa ya bisu da kallo. Ba zaka iya karantar halin da zuciyarshi ke ciki ba.
Suka yiwa kansu mazauni a falon Esta tana waje, Daddy sai murmushi yake yayinda Amiru ya zamo
mutummutumi, tsigar jikin shi na tashi cikin kauna da shauki. Ya matso ga Habib dake zaune a cinyar Habibu,
ya durkusa a gabansa ya mika mishi hannu, siraran lebbansa dauke da wani irin ni’imtaccen murmushi, da bai
taba yi a rayuwarsa ba.
Wata irin kauna ta da da mahaifi ke fizgar zuciyar shi. Amma sai Habib ya noke a kafadar Yaya Habibu wato,
bai san shi ba.
Yaji ba dadi, ya koma ga Amir yana karkada mishi ‘ya’yan mukullai, da wayo da dabara ya samu ya yarda ya
dauke shi. Ya rungumeshi sosai a kirjinshi yana sunsunar shi. Yana shakar kamshin turaren Mairo (Fahrenheit)
daya kama jikin yaron. Ganin dan uwanshi a hannun shi sai shima Habib ya miko hannu, ya hadasu su duka
biyun a kirjinsa, sai yaji kamar Mairo ce ya rungume. Amma don mazantaka, bai yarda ya zudda hawayen da
suke son bashi kunya ba.
Daddy da Habibu suka bisu da kallo cikin tausayi. Daddy yace “saukar yaushe?” Yace “dazunnan muka iso”.
Dai-dai lokacinda Hajiya ta shigo falon cikin kwalliya ta alfarma. Bakinta ya fadada da far’a da murmushi. Tace
“A’ah! Sababbin masu gidan sun zo, tsofaffi sai su zo su fice…” tana kallon Daddy tana dariya. Ya harareta don
yasan dashi take, yace “da tsohuwar zuma ake magani. In dai wadannan ne da ba mazauna ba ai gaki gasu, da
sun tafi zaki dawo min ne kina rara-gefe”.
Ba yadda bata yi ba don ta dauke su amma sun like jikin Ubansu. Ta fita ta kawo ‘teddy’ na ‘ya’yan Nina da
suka zo hutu sannan suka yarda da ita. Daddy yana son ya tambayi Habibu mai yasa Mairo bata zo ba? Yaga
babu dalilin da zai yi masa wannan tambayar sai yayi shiru. Shikuwa Amiru Allah kadai yasan abinda ke cin
zuciyar shi. Mairo ta daina son sa……! Mairo bata son ganin sa…..!!