ALLAH NE SHEDA HAUSA NOVEL

Wani wawan mari ta tsinka mata Wanda yasaka taslima ganin wasu stars na yawo, kunji wani sabon sanfarin sarrafa iskanci kuma Dan ubanki ni zakiyiwa zancen mahaukata a to ko mahaukaci wannan maganganun bazasuyi tasiri a xuciyarsa ba bare ni, koda yake ba hurumina bane bama yimiki wannan tambayar mazah’mazah ki hada kayan ki nanda 1hr kibarmin gida dama ai kwadayi ne yake kawoku burnin aiki inbanda haka, da kuma karuwanci ai duk laifin tauhida ne ta wani jawoki a jiki, ta dauke kamar wata kanwarta to Dan haka maza ki bar gidannan kin tsureni da idanu kamar mayyah, munafuka!
Fuuuu!!! Ta fita dakin nikuwa tsoro ya kamani Dan haka da sauri na fito Ina waiwaye harna fita gidan sautin kukana harya daina fita sai hawaye dake bin fuskata, napep na tsayar na fada masa inda zai kaini, kai tsaye gidan antyna na nufa na iske maigadi shine ya bude min nashiga kayana na tattara tsaf! Da kudin albashina wanda dama bana siyan komai tarawa nakeyi hotunan da mukai da antyna nadauko da wanda ita kadai tayi na fito nacewa” mai napep din kaini tasha inda xanhau motar jigawa! To yace’dan haka suka nufi tasha inda tahau motar jigawa tana ta tunanin halinda ummanta zata shiga idan taganta da wannan ciki! Tafiya sukai doguwa kafin isarsu jigawa motar kauyen su wato”roni” tahau tun a motar ta fara kuka gabda magruba ta isa kauyen duk wanda ta hadu dashi saiya bita da ido.
Jiki a mace tashiga gida da sallama” inna ce a bakin rijiya tana jan ruwa, kallon taslima tai a banzace’ sai a lokacin takalli cikin dake jikinta wurgi tayi da gugar, tayi wata shewa sannan ta cigaba da rangada guda ba kakkaftawa kankace meh mutane sun fara lekowa domin a tunanin su haihuwa ce akayi tunda al’adar garince insun haihu, wasu harta Katanga lekowa suke suga menene?
Ahayyeh! Nanayeh! ai mudai munsan rana dubu ta barawo rana daya take! tamai kaya ai cewa ake sharri mukeyi antafi aiki birni, mukau munsan yawon dandi aka tafi a birni to aifa ga aikatau nan andawo dashi, ai lallai ankuwa yo aiki wallahi babban aiki makuwa jama’ar gari kuzo kugani.
Umma dake daki tajiyo kwakwaxon inna hakan yasata fito taga meke faruwa, ai wani jiri taji na niyar dibarta domin abunda tagani gani takeyi kamar a mafarki, taslima ce da wani katon ciki innalillahi wa’inna ilaihi raji’un abunda tadinga mai-maitawa kenan cikin tashin hankali!
Baba dake bayi yayi saurin fitowa shima ido yabita dashi,
Inna tacigaba da cewa malan gashinan kana gani ankawo mama cikin shege a gidan nan nikam wallahi bazan zauna da dan zina a gida daya ba, dole inbar musu gidan,
Dasauri yace” kije ina ai sune dabarin gida bake ba, dama meh suke mana a gidan nan ai kece mata ta’ ita kuma wannan ya nuna umma(kinsan matar kanena ce shi kuma yabi duniya yabarta da lalata tar yarsu kuma kinga abunda ta kwaso Dan haka dole ne suma su shiga duniya Dan haka tabbas nabaku kankanen lokaci kafin inje masallaci indawo ku tabbatar kunbar gidan nan)
Daki ummana tashige saboda tashin hankali kukan ma takasa saina zuci datake yi,hada kayanta tashiga yi ni kuwa Ina gefe inata rusa kuka, ko kallon inda nake batayi ba,
Tabbas da baba(mijin Inna) da mahaifina ubansu daya kowa da uwarsa iyayensu duk sun rasu hakan yasa suke zaune gidan gadon su, baba da Inna sun tsani mahaifina da ummata basa kaunarsu ko kadan har aka haifeni nima abun yashafe ni, su kuwa basu taba, haihuwa ba, rana daya aka nemi mahaifina aka rasa, ummana tashiga tashin hankali matuka tun Ina karama, tun tana saka ran ganin shi harta fidda fiyeda shekara goma kenan anso tai aure takiya tace”zata cigaba da jiran mijinta har abada tunda tasan yana sonta kuma bai saketa ba, ita ta raine ni ci da sha sutura ta kuma sakani makarantar boko da arabi, dana fara girmane baba yaso ya aurar dani taki yarda shinefa suka bawa wata mata ni ta kaini aiki birni su kuma a basu kudin, ummana tayi bakin ciki da kuka sosai daga baya tacigaba damin addu’a da nasiha,
To shinefa Allah yasa aka kaini gidan anty tauhida wacce tamin gata,ta kuma mayarda ni school harna gama har xuwa yanxu da abunnan yafaru)!
Tsaf! Umma ta hada kayanta tayo waje na biyota baya, har muka fita gidan ai fitar mu keda wuya mutanen gari suka fara yimana ruwan duwatsu anata jifar mu, yara na ihu suna tayi cikin shege!
Ai tuni muka Kara sauri sukuwa suna binmu har bakin gari wani uban dutsi da aka jefo ai sai ga idanuwa na wani dum! Naji dif! Naga duhu ya ziyarci idanuwa na wani zugi da radadi nakeji har tsakar kaina da karfi nace” wayyo Allahna Umma! Umma kina Ina umma bana gani!
Allah sarki dah da mahaifi sai Allah cikin takaici ta juyo umman tana kallonta,Wanda yayi dai’dai da lokacin da akayowa ummar jefa a kunne! Wani dum! Taji kunnuwan nata’ tana kallon bakin taslima na magana amma batajin meh take cewa!
Ita kuwa kuka tasake Saki tace” wayyo Allahna ummana na makance umma idona a bude yake umma amma bana ganin ki umma duhu nake gani umma!!!!!!!!! Bana gani kitai makeni,
Matsowa tayi umman domin harga Allah batajin abunda taslimar ke fadi”kama hannunta tayi’tareda fadin taslima” Ina ganin bakin ki na magana amma kwata! Kwata banajin meh kike fadi banajin komai a kunnuwa na, sun jefe ni a kunne idan kina jina kizo mutafi karsu sake yimana lahani!!!
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un ummana bakyaji na sai dai kina iya magana nashiga ukku sun kashe miki kunne kenan sun mayarda ke kurma, ni kuma sun kashemin ido sun mayarda ni makauniya wayyo Allahna!
Shirun dataji umma tayi yakara tabbatar mata da batajin ta,Wayyo Allahna nashiga ukkuna, ya Allah Kai ne sheda ……………..
still am in love with you my fans thank you, follow me!!!!!Î Î Î Î Î Î Î Î
Sai munhadu a book2 wato ALLAH NE SHEDA 2 nagode masoya kucigaba da kasance Dani akoda yaushe taku har kullum”
ZAINAB ABUBAKAR SAFANA
xee’abu
Mrs’salihu Bamalli kaduna my luvly ustax.
GOLDEN’S WRITERS ASSOCIATION
Thank you for your shown love to me we are together fans.