Lu’u Lu’u 4

*4*

 

Bayan fitar Umad aka kira wayarshi, ganin mai kiran yasa hankalinshi ya tashi da sauri ya d’aga kiran yana fad’in “Hello yallab’ai.”

Daga can b’angaren wazirin sarki Musail yace “Yallab’ai Jacob, ya aiki?”

“Lafiya lau yallab’ai.”

Wazirin ne yace “Kaga na kiraka ko?”

Amsawa yayi da fad’in “E yallab’ai, fatan dai lafiya?”

Wani d’an murmushi yayi yace “Lafiya lau, gimbiya ce ta kirani yanzu take fad’a min sun samu matsala da wata ‘yar talakawa, ta fad’a min yarinyar ta ci mutumcinta sosai.”

Mik’ewa yayi tsaye yace “A nan makarantar? Wacece wannan?”

A gadarance yace “Sunanta Ayam.”

Zaro ido yayi dan har jikinshi saida ya amsa sunan, ba kasancewarta wacce gwamnati ta tsaya ma ba, shi kawai yarinyar tsoro take bashi, shiyasa ko kallon fuskarta baya son yi, yarinyar da zata maka yare kuma ta nuna bata son wane yare tayi ba. A ladabce yace “Yallab’ai ya kake so a yi yanzu?”

Kai tsaye ya furta “A koreta ko da kuwa k’arshen shekararta ce wannan, hakan zai zama izina ga yan baya.”

Da sauri ya cire hular kansa yace “Me?”

Da mamaki waziri yace “E, ko da matsala ne?”

A gigice yace “Yallab’ai *Khatar* akwai babbar matsala ma, dan yarinyar nan da kuke gani gwamnati ce ke d’aukar nauyin karatunta, yallab’ai Ayam bana jin ko a k’asar England za’a iya korarta a makaranta bare 脿 nan k’asar.”

Cike da tsiwa waziri Khatar yace “To shine me? Waye ubanta a k’asar nan?”

Girgiza kai yayi cike da tausayin kanshi dan har wata zufa ke tsatsafo masa yace “Yallab’ai Khatar ba ‘yar kowa bace, hasalima mahaifinta ba wani hamshak’i bane, amma kuma tasirin yarinyar yafi na democrad’iya.”

Wawan tsaki ya ja tare da fad’in “Kenan yanzu babu abinda zaka iya yi?”

A sanyaye yace “Gaskiya yallab’ai akan yarinyar nan zan iya rasa aikina had’e da tukuicin shiga babbar matsala, dan kad’an daga cikin ikon da gwamnati ta ba wa yarinyar nan, akwai lamunce mata ta ziyarci iyayenta duk sanda ta so, dan ma yarinyar na da lissafi ne take daidaita kanta da sauran d’aliban.”

A tsawace Khatar yace” Shiru malam, ni ba wannan na tambayeka ba.”

Cikin rarrashi yace” Kayi hak’uri yallab’ai, na maka alk’awarin zan ja mata kunne ta fita harkar gimbiya Zafreen.”

K’it! Ya kashe wayar hakan ya ba colonel d’in damar sauke numfashi mai nauyin gaske shi ma ya aje wayar.

K’aramin Sajan (sergent) d’inshi ya kira yace” Kira min Ayam *Utais*, izuwa yanzu suna aji tare da malam *Pedro*.”

Sara masa yayi ya amsa da” To yallab’ai.” Sannan ya fice.

Mintuna k’alilan suka shigo tare da ita, fita yayi bayan ya mata iso ta samu wuri ta zauna tana kallon major d’in, saida ya rufe musu k’ofar kafin ya kalli fuskarta saidai ba cikin idonta ba yana wani inda-inda yace “Am… Ayam Utais, dama nasa…a kirani ne naji dalilin samun sab’aninki da gimbiya Zafreen?”

K’uri ta masa da idonta hakan yasa shi mik’ewa tsaye yana dariyar rashin gaskiya kamar wacce tace kwab’e kayanka na zaneka, cikin duburburcewa ya ke fad’in “A’a, kin gane ko? Ba komai ma ba sa茂 kin fad’a ba, abinda nake so dake kawai ki rabu da ita, karki sake shiga sabgarta dan ke karatu ne ya kawoki nan, kin kusa kammala zangonki dan haka ki maida hankali kinji.”

Turo baki tayi gaba kawai ta jinjina kai alamar gamsuwa tare da mik’ewa zata fita, da sauri yace” Kina ji Ayam.”

Tsayawa tayi ta juyo tana saurarenshi, d’orawa yayi da fad’in” Gobe mai horar daku malam Pedro zai koma k’asarshi, dan haka gobe da safe zaku ci gaba daga inda kuka tsaya tare da sabon mai horarswa.”

A sanyaye ta maimaita” Sabon mai horaswa?”

“E.” Ya fad’a yana komawa ya zauna, jinjina kai tayi ta fita a ofishin tana tab’e baki da maimaita sabon mai horaswa? Waye shi? Kuma da wane salo zai zo shi kuma? Ko shi ma irinsu malam *Elinio* ne da ya gama latse ‘yan mata kafin ya koma k’asarsa Brazil?

*Suna* zazzaune wajen cin abinci da dare Ayam ta kalli k’awayen na ta su uku tace “Kunsan me? D’azu colonel yake fad’a min wai gobe za’a kawo mana sabon mai horaswa.”

Duk k’ura mata ido sukayi sai Deeyam da tace “Sabon mai horaswa kuma? Gobe gobe kuma? To me ya samu Pedro d’in?”

Saida ta zura cokalin robar a bakinta tace “Yana nan, babu abinda ya sameshi, da alama wani aiki ya samu daya fi wannan.”

Jinjina kai sukayi kafin Ayam ta sake fad’in “Kunsan ni me nake so, ina tsoron kar a kawo mana irin malam Elinio, yana mana darasi yana tsaremu da ido yana kallar mana d’uwawu.”

Dariya Deeyam tayi tace “To ya zamuyi idan ma irinsa ne? Mu dai na mu bijire masa ne kawai.”

Kallon Deeyam d’in tayi tace “Ni kuma ba haka nake so ba, kunsan me zamuyi?”

Girgiza kai sukayi inda d’aya a cikinsu tace “Sai kin fad’a.”

Cikin rad’a tace “Mu kai ziyara b’angaren malaman, ta haka zamu san wane iri ne shi dan mu d’auki matakin kare kanmu.”

Zaro ido sukayi sai Deeyam da tace “Ta ya ya haka zai faru? Ko kin manta ba’a barin d’alibai zuwa b’angaren da malamai suke, haka su ma malaman basa zuwa inda d’alibai suke?”

Waina idonta tayi sannan ta k’urawa Deeyam su tana kallonta, kawar da kanta tayi murya k’asa k’asa tace “Ki daina kallona haka Ayam, na rantse miki saida gabana ya fad’i.”

Tab’e baki Ayam tayi ta d’auke idonta tace “To na d’auke, ni dai yanzu ku bar min komai a hannuna kawai, ku dai ku shirya zan tasheku a tsakiyar dare.”

Tana gama fad’a ta mik’e tare da juyawa ta bar wurin, da kallo suka bita da fari kafin d’aya 脿 cikinsu tace “Kamar kullum, yau ma mu zamu d’auke mata farantin abincinta.”

Deeyam dake cin abinci ce tace “Tunda kinsan da haka, me ye na bitar shi kuma?”

Wata a ciki ma murmushi tayi tace “Lokuta da dama Ayam tayi abu sai ka d’auka wata sarauniya ce.”

Dariya suka yi gaba d’ayansu haka har suka kammala suka mik’e suma da farantan a hannayensu suna ajewa wurin da aka keb’e dan ajesu kamar sauran d’alibai.

*01:43*

Tana daddab’a Deeyam ta bud’a ido tace mata “Tashi mu tafi.”

Tashi tayi zaune tana murza ido tace “Ayam, ina kuma zamu je?”

Cikin rad’a tace “Tashi mu tafi kedai.”

Sake bud’a idonta tayi ta kalli saura k’awayen dake bayan Ayam dukansu cikin kayan baccinsu, a hankali ta sulala ta sauka akan gadon.

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button