ARNEHAUSA NOVEL

ARNE

Murmushin jin dadin dukansu uku sukayi
Inbanda Hajiya mariya da ta cika FAM saura kiris take jira

Sauka kasa yayi ya sake rusunawa gaban alhaji…
Nagode abba ,Allah ya saka maka da alkhairi…

Dagosa yayi yace no thanks my son, ka dauka nan kamar gidanku ne kaji? Yace toh abba na gode

Toh ku tashi ku je daki ,nan dukansu suka mike cikin farinciki suka nufi dakunansu

Murmushi alhaji ya yi yana cewa alhamdullhi,

Dogon tsaki yaji taja,tace hmmmmm
Allah sitiri bukwui inji kishiyar mai kusumbi

Kana bani mamaki wallhy

Dan dai daiita kallonsa yayi yace name fa?

Yadda kake buga kai akan Arne mana,wallhy wannan ba dabian musulmi bane

Dariya alhj yayi yace Mariya kenan,a naki sanin ba?
amma musulmi na kwarai ai baya walakanta dan wani

Arne ?haba alhaji yaron nan fa daga kazanta ya fito,mutanen da basu tsarki masu fitsari a tsaye?
wai meyasa ka rife idonka ne haka

ARNANCi Kazanta CE tabbas ,amma ai shi mutum ne ko? Kin manta da kissar fasikar karuwa da kare? Sanadiyar bashi ruwan Sha da tayi Aljanna ta shiga fa

Haba mariya,ko qurani ma cewa yayi ka zamo mai kywtata wa dukkanin mutane,..baice lallai sai musulmi ba…..meye laifin rikewa da taiimakon yaro karami kuma maraya ba uwa ba uba?kika sani ya samu kykkwan rabo ta sanadiyar mu ko ma mu mu rabauta sanadiyarsa?

Kifada min mariya….me asalin dalilinki na tsanan yaron nan

Shiru tayi batace komai ba
Hmmm ki nutsu fa, ni bana son yadda kike aibanta yaron nan

Tashi tayi shiru abunta ta wuce dakinta tana kukkuni…

Surayyahm.s????✍????
‬: ????????????????????????????????????????

 

????ARNE????

 

????????????????????????????????????????

????by????

 

Surayyahm.s????

 

*AM££NCI WRIT£R’S ASSOCIATION????✍????*

 

 

Page 19-20

Fitowar su alhji a masallaci bayan sallar asubahi da yaronsa zafar abayansa

dan ja da baya yayi yana kara dubawa

Raphael yagani zaune a kofar haraban duk hankalinsa na cikin wajen
Raphael? Alhaji ya kira
Em ummm ena kwana Abb..ah yafada da dan e,e nah
Me kakeyi anan ga sanyin asubahi

Ba komai ABBAH ,

Abba kullum yakan fito shima ai,kawae Baku taba haduwa bane zfaar yace

Dan murmurshi alhaji yayi yace raphael ai ba sallah kakeyi ba y not kayi baccin ka kar sanyi ya kama ka

No abba bana iya baccin ne kuma…..sai ya shiru ya rasa abunda zai CE

Toh shikenan ,muje ciki nan suka dunguma zuwa ciki su uku

Haka raphael ya cigaba da binsu yana zama a bakin haraba yanajin duk abunda akeyi

Hakama idan mallam mamman yazo weekend tun yana buya abayan window har ya fara zama tare dasu..anayi yanajin su a gefe…..

Musamman ma ranar waazi da tarihi ,domin kuwa raphael na matukar jin dadin kissoshi da tarbiyan da mallm mamman ke koyar da su zafar

 

Aransa kuwa wani bangaren na mamakin yadda agidan hajiya mariya CE kawae ba ruwanta da abunda ya shafi karatun Addinin yaranta….ko zuwa Inda suke bata yi

Hakan ne ma yabashi damar hllatar wajen ba tare da wani matsala ba

Ranar asabar bayan Malm mamman ya gama yan tambayoyin sa,

Alhaji ne ya taho ya iske su anata dariyar raphael da ya nace shi ma sai an masa tambaya shima.

Da murmushin sa ya mika wa Malm mamman hannu
Barka dai alhaji an fito lpya?

Lpya lau mamman ,enada ai ba wata matsala

Ahh bakomai masha Allahu

Yawwa kutashi ku shiga an gama na Yau..yafada yan dubansu

Ganin yadda raphael yayi fuskan tausayi yasa Malm mamman yace abokina kar ka damu zan tambayeka next week sai ka shirya

Da dariyarsu suka kalleshi, yana cewa toh oga mallam

Shima dariyar ya mayar musu

Toh alhaji ni zan wuce,Malm yace

Hannu yasa a aljihu ya Ciro kudi yabasa
Ka Sha ruwa a hanya an gode fa,

Godiya shima yayi ya fice_

Zafar,alhaji ya kirashi gefe yace ku shirya dukkan ku
zamu Fita kai da faryal da raphael

Murna yake ya Shiga dakin raphael yace masa kayi Saurii ka shirya abba zai fita damu yau

Minti 15 sai gasu sun fito, faryal tareda haj mariya kowa yayi kyw tubarkallah…

Nan shima Raphael ya fito cikin shigar Riga red da bakin wando jean ,ba karya shima ya fito

amma tsoro ne da fargaba cikin ransa yadda yaga hajiya na doka masa harara da gefen ido

Sunkuyar da kai kawae yayi ya wuce shima ya Shiga motar

Haka fir ta hanasa sakewa a motar duk da alhaji na nan shima aciki

Wata babban super market aka sauke su, kana ganin haduwar wajen kasan daga wane sai wane agarin abujan ma….

Duk su faryal sun sake abunsu amma Raphael jiyake kamar ya Shiga wata duniyar ta daban ba a Nigeria yake ba

Sai kalle kalle yakeyi

Dariya sukaji haj mariya takeyi kamar anbata kywtar wani abun

Subhanallh da Sauri alhaji ya karaso ganin Raphael ya makale akan stairs na zamani mai tafiya da Kansan nan

Bakauye an shigo birni,haj tafada tana dariya
zo nan mu wuce faryal.

Hannu zafar ya mika masa ya sauko kafin alhaji ya sa ya gwada masa yadda a ke yi

Kaga raphael ba takawa zaka nayi ba,tsayawa zakayi akan Wanda ka fara takawa shi zai kai ka har sama sai ka sauka

Zafar yafada yana gwada masa

Nan alhaj yace Toh ku je tare da Raphael zafar sai ka na gwada masa abunda bai gane ba

Toh abba,suka nufi sama su ma

Nan zafar ya fara deba musu kayan sakawa kala kala dayake designers ne ,tareda da expert artist suke wanda ke binsu yana basu opinion da zabi akan yanayin kowani kayan sawa da suka zaba

Duk da fargaban dake zuciyar raphael zafar bai barshi ba sanda ya jida masa kaya fiye da nashi ma.
Haka ma takalma turare, wristwatches da mayukan jiki, wanka, Dana wanke kai…

Cikin awowi 4 da rabi aka kammala komai suka kama hanya

Wani mugun kallo take masa
Wanda yasa jikinsa karkarwa duk hankalinsa baya jikinsa

Ji yayi ance raphael da karfi,a firgice yace naam Zafar

Abba na maka magana

Yace muje dakinsa mu same sa yanzu

Toh muje mana …….tare suka jera suka nufi dakin da sallamarsu

Surayyahm.s????✍????
‬: ????????????????????????????????????????

 

 

????ARNE????

 

????????????????????????????????????????

????by????

Surayyahm.s????

 

*AM££NCI WRIT£R’S ASSOCIATION????✍????*

Page17-18

Bayan wata biyu a gidan alhaji ,raphael ya warware
normal kamar bashi ba

Zaune yake a kofar masallacin gidan yana sauraron zafar dake karatun Qur’ani bayan sallar asubahi.

Nitsuwa yayi tamkar wanda yasan abunda ake cewa…….har cikin ransa abun na Sanya shi jin nitsuwa
Shyasa ma ya nace kullum sai ya biyosa ko a sace ne ya labe yana ji

Karfe 7.saura suka nufi gida tare ,asace raphael ya shiga dakinsa domin kuwa Hajiya ta hanasa hada hanya da su zafar

Shikuwa kullum yana like duk enda zasuje dashi
musamman ma zafar da ke sa’arsa ne,,,sai ya buya a gefe guda har ya gama harkokinsa kafin su dawo

Hajiya kuwa bata damu ba ma saboda a dakinsa tace yadinga zama kar ya fito mata cikin gida.

 

Alhaji abdullhi dan kimanin shekaru 45yrs bafulatani ne dan asali kauyar Adamawa a Nigeria

mahifinsa alhaji Muhammad ja’EH da
,mahaifiyarsa Hajiya salima ita kuma asalin yar Ethiopia cr…

a tsaye yake duk da shekaru tafara ja, kynwun halittarsa bata boyewa,

mutum ne mai ilimi sosai da sanin yanayin zaman takewa …..kafaffen mai kudi ne wanda ya samo asali ne tun daga mahaifinsa….ya mallaki kamfanoni a Nigeria da kasashe daba daban a waje.

Alhaji abdullhi da Hajiya mariya auren zumunta akai musu …ita kuma yar Ethiopia ce
ta wajen mahaifinta

,mariya dai yar dangin mahaifiyar su alhji abdullahi ne Hajiya salima

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button