AUREN GADO Page 1 to 10

“OK zanturo tunda mommy ta Amince dake and my brother too yanzu kije gida zanturo. Tsalle ta buga tareda Dane shi ta rungume shi kam” don Allah da gaske zaka tura? Oh my god khaleel zanyi suman dadi yau. Tafada tana share hawaye, ban bare ta yayi a jikin shi ya ce “oh come on a gidan surukai kike fa behave yourself.
“Farin ciki ne yamun yawa baby muje mota indakko wa momy tsarabar ta please, Tafada tana riko hannun shi, jinta takeyi kamar anyi mata bushara da gidan Aljannah……. ????
*Matar Soja*
???????? *AUREN GADO* ????????
*Matar soja ce*
Daga marubuciyar
KUSKURE NA
BARIKI AUREN SOJA
MUK’ADDARI
WANAKE AURE
ZANYI BIYAYYA
And now AUREN GADO,
???? page
5⃣&6⃣
..,………. Kaya na kece raini ta kawowa momy tsaraba Wanda tayi ta godiya kamar zata goyata, bayan tafiyar ta bata da wani zance sai na “Ibrahim khaleel bikin ka zamu gwan gwaje ba karya kaga Abun Arzikin da ta kawomin tun ba ayi Aure ba? Wucewa yayi cikin dakin shi domin shi yanzu daya sani yake mara iyaka daya Amince mata tazo gidan su har Mommy ta ganta, yanzu ya boni shikam………
Wasa wasa Saida aka kwashe kusan sati daya bai kuma daukar wayar taba ta Kira ta turo msg yafi hamsin Yana shareta, momy tayi nacin zancen turawa gaisuwa Yana ja baya, domin shidai bai shirya ba infact baya ra’ayin zama da fauzy she is not his choice zai cutar da itane kawai, bazata taba samun kanshi yanda take soba. Bikin Ahmed da Naziya ya matso gefen gidan su shikadai ke shirin shi da Abokan shi Yana cikin tsananin farin ciki, momy tace bazata wahala akan Y’ar talaka ba, yan uwan tane dai suka fara cika gidan, musamman Aunty zarah, Wanda itace kanwar ta da sukazo hali daya, komai na Aunty zarah sai a hankali tana son gayu da babbar harka.
Duk akwatunan da Ahmed ya hada momy ta sa anrage duk wani gold tasa ancire ansa passion wai basu san darajar su ba talakawa ne. Baida yanda zaiyi saidai farin cikin shi daya Khaleel ya hadomai Nagani na fada a bangkok, don haka sunkai sun boye sai in ta tare, duk wani event mommy ta soke wai yarinyar da ba wayayya ba yaja musu Abun fada bada itaba, don haka ya hakura domin Albarkar Aure yake nema in Allah ya mallaka mai ita burin shi ya gama cika, sannan farin cikin shi daya itama tace bata son wani bidi’a walima ta isheta da za ayi a gidan su,.
Khaleel yana gefe baya cewa komai he just feel boring baiga Abun burgewa a yin Auren ba ba wani Abu da ya bashi sha’awa da har zaiji yanason yayi Auren ma, fauzy sarkin naci tazo tun Ana jibi Bikin ta tare duk inda Aunty zarah ta shiga suna tare gaba daya yabi d’an uwan nashi sun kauracewa gidan suna part din Ahmed saboda jama’ar da suka cika na momy, yaki ko Yarda su hadu da ita, ta d’an ji sanyi ganin tana cikin gidan su kuma no matter what sai sun hadu kafin ta koma gida, ita da ta samu daurin gindi a wurin uwar miji ma, ita kanta tasan mommy batason Auren Ahmed domin ta gama bata labarin ta tas.
Rana bata karya inji bahaushe, Alkawari ya cika, inda Aka daura Auren Ahmed da Naziya akan sadaki mafi daraja, sai muyi fatan Allah ya kade fitina, tunda aka daura Auren ya baro taron ya dawo gidan tareda kulle kanshi cikin dakin su, zazzabi yakeji mara dalili tareda jin wani irin bakon Al amari a tattare dashi, Ahmed nata neman shi, Saida ya kirashi ya dauka yafada mai cewa yana gida, dawowa yayi shima tareda barin Abokan shi ya same shi a dukun kune cikin bargo,
Cire babbar rigar shi yayi ya zauna gefen gadon tareda cewa “bakada lafiya ne? “Fever ke son kamani, “sorry namiji, kasan me? Yafada yana gyara zama, tashi Khaleel yayi ya jingina a jikin gadon yace what my brother? “Burina yacika khaleel, today Naziya is legally mine, but am worried me zata fuskanta a cikin gidan nan, how is she going to react after she find out about everything? “Like what brother? Like our wealth, this big mansion, and mommy. Yafada yana rage murya cikeda tausaya wa kanshi, kamar yarone yaga alawa Ana mai kwalelenta haka yakeji yanzu, yasamu farin cikin shi Amma baya cikin farin ciki.
Matsowa yayi sosai kusa da d’an uwan shi yace “Yaya this is the time da zakayi fighting back, ka tsaya akan ra’ayin ka, you have to talk brother, fight for your love, and Aunty Naziya will be happy bazaka samu Matsala da itaba, in tace zata sama yayana hawan jini bazan raga mata ba cos batasan irin fighting da kakeyi akan soyayyar taba. “Hmmm you known, nafison momy ta barni in zauna a gefen mu, bana son Naziya ta shiga cikin damuwa nasan zata sha wahala Idan akace zata zauna cikin gidan, she can’t handle it, bata saba da irin wannan rayuwar ba. And mommy is our mother dole mubi Abinda takeso Auren Naziya da A hannu na yake Dana hakura for mommy happiness, but Allah kadai yasan mai ya boye a cikin Al’ amarin,
Yafada cikeda damuwa, Dariya khaleel yayi mai d’an sauti wadda ta Kara bayyana kyanshi sosai, “Yaya this my Aunty is very lucky, tasamu miji mai sonta sosai Anya zaka kuma Aure nan gaba like the way mommy is planning? ” no Khaleel bana son Naziyata ta zauna da kishiya Ina so tayi rayuwar y’anci ne, Ina son inganta cikin hutu da walwala, khaleel na gama tsara irin yanda nakeso rayuwar Naziya ta kasance, I love her beyond your imagination, ka tayani son Naziya kaima kamar yanda nake sonta.
Sundauki dogon lokaci yana daukewa yayan nashi damuwa ta hanyar k’arfa famai guiwa, Saida friends suka fara kiranshi ya Fita tareda barin khaleel cikin damuwa, Alwashi ya dauka mai girma akan zai taya yayan shi fighting akan duk Abinda zai daga mai hankali bazai so yaganshi cikin damuwa ba,.
Bai kuma Fita a gidan ba ko sallah a part din yakeyi ya koma ya kwanta, yarasa abunda duk ya Cire mai walwala da natsuwa bayajin dadin jiki da zuciyar shi baki daya, he just fee like going back to bangkok, baisan mai ke hana shi sukuni ba. Sai Karfe Tara Ahmed ya kuma shigowa dakin ya tsaya a kan shi tareda cewa “brother what is wrong? You look very dull. “I don’t know Yaya kawai bana jina cikin natsuwa. “relax nima haka nakeji tundazu but now am fine, your Aunty is here khaleel, finally Naziya is here. Zama yayi tareda rungume Khaleel din yana fitarda hawayen da yarasa na menene ke fitowa daga idanun shi.
Saida ya d’an natsu yace let go and welcome your sister in law. Mikewa yayi ba musu, ya bishi sanye cikin kana nan guntayen kayan da ya canja tundazu.
Gefen Naziya kuwa tunda suka sako kai cikin wannan tafkeken gidan gaban ta ke faduwa gashi gwaggonnin tane suka rakota su uku bisa ga umarnin malam domin baison gayyar tsegumi, kanta a duke yake tunda motar da ta dakko su ta shigo, cikin Y’ar rakiyar ta daya tace “t’irk’ashi wannan gidan mutum daya ne ko dai gidan y’an yankan kai? Sauran suka fara salati, shikenan malam saida Y’ar nan yayi, irin wannan gidan saikace wata unguwar? Saurin daga kanta tayi ta saki baki tareda dafe kirjin ta tana karanto Addu’ar tsari a cikin zuciyar ta, jikin ta shegen rawa yafarayi. Har motar ta tsaya Abokin da ya dakko su yace “Hajiya kufito mu shiga ciki ko? Kamar way’enda kwai ya fashewa a ciki haka suka fito ji sukeyi kamar ace ar su ruga, shi ya musu jagora kowaccen su Addu’ar da duk tazo bakin ta takeyi, rike take da tsintsiyar hannu irin wainda ake rikewa na share dattin daki a wurin sabuwar Amarya bisa ga Al Ada, nasan wasu sun san wannan Al Ada akan ce ta share duk fitinar d’akin kafin ta zauna cikin dakin ta.