AZIZA DA AZIMA COMPLETE HAUSA NOVEL

AZIZA DA AZIMA 41-50

“Wlh Mom tun da muka dawo inaji bayan mun gama hada abincin da za a fita da shi ban ƙara ganinta ba, dan tun sadda baki suka fara shigowa ban ganta ba” Mom ta ce

“Kin san Aziza bata son mutane kamar ma kunyarsu takeji yanzu haka to ba mamaki tana daki”

“Wlh kam Mom kunyar mutane takeji,ko mu a gida Aziza bata gama sabo damu ba bare kuma yau ta ga mutane ai ba zata fito ba,amma bari naje na fito da ita dan yau yawon sallah zamu je a ga yan uwa da abokan arziki” Mom ta ce “dubota to, sai ku shirya ku fita nima zanje gidan Hajiya Hauwa(gidan sirkan Sultana, Hajiya Hauwa ita ce Mamansu Khalil wanda zai auri Sultana) dan yau muma zamuje ziyara ne”

“To Mom” Sultana ta faɗa tana tashi da sauri ta yi dakin Aziza a lokacin ta gama kukanta tana tunanin wan can sallar tana gida tare da Hajjanta da Baffanta, Sultana tana shigowa Aziza na fitowa daga toilet ta wanke fuskarta, Sultana ta ce

“Ohh Allah Aziza, sabida kinji gidan a cike shine kika boya a daki? To maza ki shirya, zamuje yawon sallah”

“A’a Anty Sultana bana son fita,bazan je ba”

“Wlh sai kinje, Mom ma fita zata yi,yau ranar zumunci ce, yau fa ranar farin ciki ne amma ke na ga kamar ba baki farin ciki ko mun yi miki wani abu ne?”

Aziza ta girgiza kai, 

“To idan har ba mu miki komai ba ki shirya yanzu ki canza kaya ki saka atampa,bari nima naje na canza kaya” Aziza ta gya ɗa kai, Sultana ta fice.

      har Sultana ta shirya ta sha makeup ta kashe ɗauri ta yi pics ta turawa Khalil dinta, sannan ta fito dauke da handbag dinta ta shiga dakin Aziza ta sameta ta canza kaya amma tana zaune tana riƙe da ɗankwali a hannunta, Sultana ta ce

“Ba kiyi kwalliya ba?”

“A’a Anty Sultana ba zan yi ba”

“A yau sallan? Wlh baki isa ba” Sultana ta fada tana daukar powder ta hau gogawa Aziza a fuska, sannan ta shafa mata red lipstick, duk da fuskarta taki bari ya fito sosai amma ta yi kyau, sannan Sultana ta kashe mata ɗauri, Subhanallahi! Aziza ta yi kyau sosai, nan Sultana ta daukesu hoto, duk da Aziza bata ɗago fuskarta sosai ba, sannan bata ɗaga idonta ba.

Bayan sun fito parlour suka sake yi da Mom, sannan suka fice a gidan, a mota Sultana ta turawa Nawaz pics din tare da rubuta masa HAPPY SALLAH BRO NAWAZ.

    Ko da Nawaz ya buɗe ya ga hotunan yan uwa da abokan arziki, Allah Sarki gida dadi,ya fada yana murmushi a ransa, wani hoto ya bude ya ga Mom sai da ya sumbaci hoton, sannan ya sake buɗe wani ya ga Sultana ta yi kyau sosai ya ce “nice sis” ya sake bude wani ya ga da Mom da Sultana ya yi murmushi yana faɗin

“My world” wani hoton ya sake buɗewa ya ga Sultana da Aziza amma bai ganeta ba, sai da ya kara buɗe wani ya ga tana dukar da kai kamar amarya kafin ya ganeta, sun sha lalle kuwa, wani hoton ya sake buɗewa Aziza na zaune a mota bata ma san sultana ta dauketa ba, lumshe ido Nawaz ya yi yana karanto adduar masifa dan Aziza ji yake yi ta zamo masa masifa, kansa ne ya hau sara masa sai da ya ɗan ji dai-dai kafin ya fita dan yaje ya samu amininsa su ɗan fita suma.

      ????????????

Kwana hudu su Sultana suna yawo,kullum kuma idan suka yi wanka sai Sultana ta musu hoto ta turawa Nawaz, tun yana buɗewa har ya daina buɗewa,dan ganin hoton shike kara masa mafarkai a nasa ganin kenan.

       ????????????

Ta bangaren Azima ko kaɗan bata yi wankan sallah ba bare shigar sallah, haka ranar sallar ta wuni tana jin haushin kowa,kiris ya rage abincin sallar ma bata watsa masa dafi ba, dan haka kawai ta ga kowa na murna da farinciki ita kuma tana ji kamar zuciyarta ya fashe da baƙin ciki da takaici, haka aka gama cin sallah Azima bata yi shigar sallah ba illa kayan fulaninta da ta dinga yawo da shi har satin sallah.

        Bayan komai ya daidaita haka rayuwa ta ci gaba da tafiya, bayan sallah da sati biyu Aziza ta fara zuwa university din su Sultana, bata shiga hidimar kowa kasancewar tasan ita din ba mutum ba ce,haka zata je ta dawo,idan kuma Sultana na da paper su kan je tare su dawo tare, tana nan tana tara kuɗinta har ma da wa inda ta samu da sallah dan tace kwanan nan zata bar gidan.

????????????????????

“Innalillahi wa inna ilayhirrajiun! Dan Allah Jauro ka taimakawa ƴata kar mayyar nan ta kasheta!” ya faɗa yana mai riƙe kafar Jauro, Jauro ya ce

“Wlh Malam Halliru na kasa yiwa ‘yarka magani, wannan mayyar tana da taurin kai” Salti dan gidan Jauro ya ce

“Wlh Baffana baya da baiwa irinta Baffa Magaji, dama wajan Baffa Magaji kuka je da yanzu ta samu sauki, amma ku fara zuwa kuyi kamun kafa da Sarki Chubaɗo”

“Wlh zanci ubanka Salti! Zaka fita mini ka bani waje ko sai na bazar da kai da sanda?” Salti ya miƙe yana kunkuni yana fadin

“To dan na fadi gaskiya kuma Baffa” Salti na fita, Malam Halliru ya ce

“Hakika munyi kuskure, dole wajan Magaji zamu je neman taimako”

       ????????????

MOMYN AHLAN✍????

[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: ????????????????????????????????????????

    ????✨ *AZIMA DA AZIZA*????✨

    (???? _Macizai ne_????)

    MALLAKAR.

*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*

SAHIBAR KAINUWA.

Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din

0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.

Sanarwa.

Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*____________________________________*

*????KAINUWA WRITERS✍???? ASSOCIATION*????????

“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*????????

https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association

*____________________________________*

*MARUBUCIYAR.*

1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._

2- _GUDU A JEJI._

3- _SHUHADA._

4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._

5- _WA’YA KASHE ZAHRA’U?(#200)._

6- _COLONEL UBAIDULLAH._

7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._

8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._

9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._

10- _DA NA SANI NA._

  11- _BADAWIYYAH_

12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_

Now

13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE????)_

_Follow me on wattpad,@Fateemah’0_

   ????????????????????

*PAID.*

????️=4️⃣7️⃣↪️4️⃣8️⃣

Wajan Sarki Chubaɗo Malam Halliru yaje yana kuka yana ba wa Sarki yankin fulanin kwana hakuri a kan ya taimaka yasa baki ya yiwa Magaji Bawa magana ya taimaka ya duba masa ‘yarsa, Sarki Chubaɗo cikin tunzura ya ce

“Ayhoo!! Ashe ku kuna son yaranku, shi da ku ka kora masa nasa ya yi yaya kenan? har kwanan gobe Jumala bata magana bata um bata um-um,nan ku ka daure Aziza kuna shirin kasheta! anyi haka ko ba a yi ba?” cikin kukan nadama Malam Halliru ya ce

“Munyi kuskure ranka ya dade! Amma ba laifinmu bane Jauro ne ya zugamu ya sa mana tsoro da shakku, dan Allah a taimaka mini” Sarki Chubaɗo ya ce

“Idan Jauro ya ce ku faɗa wuta zaku faɗa ne? idan har Magaji zai taimaka maka a nasa ra’ayin farillahi hamdu! amma idan ya ƙi wlh daga nan fada babu wanda zai saka baki” Malam Halliru ya amsa da ya yarda shi dai ayi masa izini yaje gidan Baffa, Sarki Chubado ya daga masa hannu alamun yaje godiya sosai Malam Halliru ya yi ya tashi da gudu har yana tuntube, bayan Malam Halliru ya tashi Wazirin kwana ya ce

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button