DR KHALEEL, Complete Hausa Novel.

~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar116…….Ashfah ta kusa awa daya a xaune gefen yaran tayi tagumi tana kallonsu, mikewa tayi a hnkli daga karshe ganin sun fara bacci, ta gyara masu kwanciya snn ta cire kayan jikinta ta canxa xuwa gown na bacci, ledan da ya ajiye mata ta dauka ta bude fridge ta ajiye, snn ta dauki hijab ta sa tayi kwanciyarta gefen yaran. Can cikin dare Sultan me sunan Abbansu Ashfah ya farka ya fara kuka, lkci daya ya tada dan uwansa Sudais me sunan dad, suka hadu suka dinga kuka, Khaleel na xaune kan darduma ya idar da sllhn Nafila ya ji kukansu, sun fi minti goma suna kukan, Khaleel ya mike jin kukan nasu sae karuwa yake yana kallon agogo ya ga Karfe biyu saura, kofa ya nufa ya bude ya fita ya nufi dakin Ashfah, ya dde tsaye bakin kofar daga karshe yyi sallama yana tsaye bae shiga ba, sallama ya kuma yi, jin bata amsa ba yasa ya tura kofar a hnkli ya shiga dakin, ga mmkinsa kwance yasameta tana bacci ga yaran gefenta sae rusa kuka suke har da shure shure, kasa daina kallonta yyi yana ganin ta kmr Ashnaahr sa gashi exactly irin kwanciyar Ashnaah tayi, ya karaso gadon a sanyayeba tare da ya san lkcn da yyi hkn ba har lkcn idonsa a kanta, hawaye ne suka cika idonsa lkci daya xuciyarsa ta raya masa ba fa fateemarsa bace wnn wata ce daban kawae kama suka yi, juyawa yyi da sauri hawaye na sakko masa ya nufi kofa xae fita jinkukan yaransa ya sa ya dakata a bakin kofar ya juyaa hnkli yana kallonsu, share fuskarsa yyi ya karasa gadon ya dauki sultan dake kusa da ita, sae a snn Ashfah ta farka a dan firgice ta mike xaune da sauri tana gyara hijab dinta ta koma baya tana mitsika ido, Khaleel dae bae ce mata komae ba ya dauki duk yaran yana lallashinsu, Ashfah tayi mmkin irin baccin da tayi don rabonta da bacci irin hka tun kafin Abba yace xae hadata da Khaleel, kullum cikindare bata da aiki sae na kuka da tunane tunane, mikewa tayi da sauri ba tare da ta kallesa ba tace”in hada masu madara ne?” Shi ma bae kalleta ba yace “eh” ta fita da sauri daga dakin ta shiga neman kitchen don samo ruwan xafi, Eva water ta daura a gas ya dan yi xafi snn ta dawo dakin ta shiga hada masu madaran cikin feedern su, tana gamawa ta mika masa daya feedern tace “kawo dayan in basa” ya mika mata sudais ta karbe shi ta xauna gefen gadon ta shiga basa feedern, Khaleel kam bae xauna ba daga tsayen da yake ya shiga ba Sultan dake rungume jikinsa, lkci daya yaran suka koma bacci, Ashfah ta kwantar da Sudais da ke hannunta a hnkli, shi ma ya kwantar da Sultan gefen Sudais ba tare da ya kalleta ba yyi mata sae da safe ya fita.Washegari da safe Ashfah ta rasa ta ynda xa tayi ma yaran wanka, ga dae ruwan xafi ta sirka a bayi amma bata san ta ina xa ta fara wankan ba don gunMomyn Meenah yaran suke tun suna jarirai, ta fito daga bayin a sanyaye ta xauna gefen gado tana kallon yaran da ke ta wasa abunsu, a hnkli ta shiga cire masu kayan jikinsu gaba daya har ta gama snn ta dauki Sultan ta nufi bayin da shi tana kallon ruwan dake sirke cikin bahon wankansu kmr xata yi kuka, ga sabulu da soso ta ajiye gefe, Muryar Khaleel ta ji a bayanta ta juya da sauri ta rungume yaron a jikinta don har lkcn nyt gown ne jikinta, ya kauda kai yace “xa ki iya masu wankan ne” ta juya masa baya tayi shiru, a hnkli tace “ni ban iya ba” yace “OK kawo in masu” juyawa tayi ta mika masa yaron hannunta ta fice da sauri ta je ta sa hijab dinta, shi yyi masu wankan gaba daya ya shirya su, ita kuma ta hada masu abincin su ya ba daya ita mata ba daya. Hka Ashfah ta wuni ranan daga ita sae twins a daki gashi basu da rigima ko kadan sae in sun ji yunwa, Rukayya ce ta kawo masu abinci throughout ranan, Khaleel kam na dakinsa tun bayan da ya taimaka ma Ashfah ya shirya yaran bae kuma fitowa ba yana aikinsa da ya saba kullum na tunanin Ashnaah, bbu ranan Allahn da baxae wuce ba da baxae bata awa biyu xuwa uku cikin lkcn sa ba yana tunanin irin rayuwar da suka yi tun daga farkon haduwarsu da Ashnaah har xuwa rananda xata bar duniya, hkn kan sa shi kwalla ba kadan ba, kullum Addu’arsa bae wuce na Allah ya rahama mata ba ya bata gidan aljanna, Da daddare Rukayyana komawa gida bayan ta taimaka ma Ashfah ta yi ma yaran wanka Khaleel ya shigo dakin da sallama ya tsaya daga bakin kofa yace “bbu matsala ko?” Ashfah ta gyada masa kai ya juya ya fita tare da yi mata sae da safe ya rufe masu kofar.Satin Ashfah biyu knn gidan Khaleel amma ko gaisuwa baya hadata da shi in ka ga sun yi magana to ya shigo daki taimaka mata ya basu abinci in ya jisun hade mata kae suna kuka ne ko kuma ya taimaka mata ya wankesu da safe don sun ma daina tashi cikin dare in har suka koshi da daddare, shknn iyakar abinda ke hadasu knn, kwata kwata ya daina yini a gida ynxu, ita dae bata san inda yake xuwa ba amma da Karfe shidda yyi xae dawo gida da yan kayan ciye ciye ya ajiye mata, tuni ta fara girki a gidan kuma duk girkin da xata yi xata xuba masa nasa ta ajiye kan dinnin kuma yana ci ba laifi idan ya dawo, wani lkcn yace mata “thank yhu” in yashigo taimaka mata da twinz, ita dae bata cewa komae. Yau da daddare Ashfah na gama shirya su sultan da daddare ta basu abincin su suka yi bacci lkci daya ta kwantar da su, ynxu kam ta fara sabawada iya rainansu ita kadae ba sae an taimaketa ba, sae dae tana shan wahala ssae don rainon yan biyu ba abu me sauki bane da daya ya fara kuka daya zae amshe ko wasa yake su hadu suyi tayi duk su rikitata wataran ma ita ma ta sa masu kukan, ssae take son yaran kmr xata hadiyesu, tana kwantar da su ita ma ta kwanta nn da nn bacci ya dauketa, can cikin dare suka tashi gaba daya suka fara kuka, ta mike xaune da kyar tana kallonsu don da wuya ka ga sun tashi cikin dare ynxu gashi ba su barta tayi baccin rana ba ranan, kan fridge ta nufa ta dauko Goran ruwansu don tasan ba yunwa a tare da su saedae kila kishin ruwa amma kmr ta kuma sa su kuka da ta basu ruwan, ta shiga hada masu madara da sauri, ta daukesu a tare tana basu nn ma suka ki karba kmr sun hada baki, sae kuka suke, ita ma ta fashe da kuka tana kallonsu tace “toh me ku ke so?” Tura kofar da taji anyi tare da sallama yasa ta dauki hijab dinta da sauri ta sa, ya karaso cikin dakin yanakallon twins din ya duka ya dauki sultan snn Sudais duk ya rungumesu yana lallashi, jin basu yi shiru ba yasa ya xauna gefen gadon ya dauki feeder yana basu, nn ma dae ba su wani karba ba, ya gane to kila basu da lfya ne, yan dubaru yyi masu ya basu magunguna, yana ta lallaba su har dae ya samu duksuka koma bacci, daya a kafarsa, yana rungume da daya kuma, juyawa yyi yana kallon Ashfah ya ganta xaune can karshen gadon wae don ya xauna gefen gadon, ta jinginar da kanta jikin gadon tana bacci daga xaunen da take, duk lkcn da ya kalleta sae gabansa yyi mugun faduwa lkci daya kuma Ashnaah ta fado masa gashi yana ddewa kafin ya daina tunaninta, meyasa xa a basa mata me kama da fateemarsa hka, juyawa yyi ya kuma kallonta jikinsa a sanyaye yace “ki kwanta” bae ga alamar ta san yana yi ba don da gani tayi nisa da baccinta, ya mike a hnkli ya nufi dakinsa da yaran gudun kar su tashi duk ya kwantar da su a dakin snn ya dawo dakin Ashfah ya kuma ce mata ta kwanta daga bakin kofar da yake tsaye amma shiru, yw fi minti biyar a tsaye snn ya karaso cikin dakin ya dan buga gado ko xata tashi nn ma bata tashi ba, but ko kadanAshnaah bata da nauyin bacci hka da ta ji motsi take farkawa, ya dan yi murmushi jikinsa a sanyaye ya dan dafata.117…..A tsorace Ashfah ta farka tana kkrin mikewa ya koma baya da sauri yace “No nace ki kwanta ne” mikewa tsaye tayi ta koma jikin gado kanta a kasa, ya juya da sauri ya nufi kofar xae fita, da sauri tace”yaran fa” ganin bata gansu kan gadon ba, ba tare daya kalleta ba yace “suna daki na” yana kai wa nn ya kulle mata kofarta. Washegari Ashfah ta gama shirin ta da safe ta gyara dakin ta snn ta sauka downstairs don hada break fst, ko da ta gama har tara yyi, ta haura sama don komawa dakinta taji kukan su sultan, kasa shiga dakinta tayi ta tsaya bakin kofa, don da taji kukansu hnklinta ke tashi ta rasa sukuni barin ynxu da tasan ba su ci abinci ba tun wayewar gari, can dae ta gaji da tsayuwa ta shiga dakinta, ta fi minti biyar da shiga amma har lkcn sae karuwa kukansu yake, ta kasa daurewa ta mike kmr xata yi kuka ta fita da sauri ta nufi dakin, tana shiga dai dai lkcn da Khaleel ke fitowa daga wanka knn daure towel a waist, da sauri ta juya masa baya a mugun tsorace sae kuma ta nufi kofa ta fice daga dakin da sauri har tana tuntube, Khaleelya dauki yaran yana lallashinsu har suka yi shiru snn ya xaunar da su tunda sun fara iyawa ynxu cikinkekunansu da fanz suka kawo masu as gift ranan da aka rada masu suna bayan rasuwar uwarsu duk da ba ayi wani taron suna ba, cikin minti sha biyar ya gama shirin sa ya kwashi yaran ya kai mata ba tare da ya kalleta ba yace “anjima xa mu fita, ki hada masu kayansu,” yana kai wa nn ya juya ya fita, Karfe sha daya suka bar gidan gaba daya da kayan sawansu da ta harhada masu da madaransu da feeder, bayan mota ta xauna da yaran a jikinta, ga mmkinta gidansu ta ga Khaleel ya nufa, yana gama parkin suka shiga a tare, sae murna take xata ga Abbanta da momy, momy tayi farincikin ganinta hkama Abba, inna ma na gidan ranan, inna ta rungume jikartata tana mata sannu da xuwa da daya daga yan biyun hannunta, sae da Ashnaah ta rasu da sati biyu aka sanar da inna da ke can katsina lkcn, ba sae na fadi tashin hnklin da ta shiga ba don dagewa tayi kan Abba ne ya kasheta ba kowa ba wllh, da kyar dae aka samo kanta don sae da ita ma tayi yankwanaki a gadon asibiti don ba karamin girgixa ta mutuwar tayi ba, Khaleel da ya biyo bayan Ashfah rike da Sudais a hannu ya duka har kasa ya gaida innar da ba wani sake masa take ba don a xaton ta shine sanadin faruwan komae, sae da duk suka bar falon ya rage shi da Abba snn yace “dama Abba sultan na kawo maka, na baka shi kmr ynda ka bukaci inyi hkn idan Allah ya yrda,” Abba yyi murmushi yace “Ma’sha Allah, Allah yyi maka albarka Khaleel na gode kwarae da gske” Khaleel yadukar da kansa yace “Ameen Abba, Sudais kuma xan kai sa can gidanmu gun Ummina” Abba yace”,Allah sarki, Allah dae ya raya su ya albarkaci rayuwarsu” Khaleel yace “Ameen Abba” Ashfah duk a tunaninta karatu xata koma shiyasa aka maido yaran gidansu amma har suka fara shirin tafiya bataji Abbanta yyi mata mgnr karatu ba, hkn yasa hnklinta ya tashi, Karfe biyu suka bar gidan, Khaleel ya kai Sudais can gidansu kmr ynda yace, dad dinsaya kira sa har bedroom dinsa yace “alfarma daya nake son ka min ynxu son” Khaleel ya daga kai yanakallonsa, Abba ya nisa yace “ko sati ba ayi ba da xuwan Alhaji Mukhtar wajena, so nake kayi hkuri ka mance duk abinda ya faru ka koma bakin aikin ka, shi ya nemi wnn alfarman daga gareni kan cewa in maka mgna xaka fi ji” Khaleel yyi shiru bae ce komae ba, ko kadan badan mahaifin sa ne yyi masamgna ba bbu abinda xae maida sa asibitin nn, but he vowed never to disobey his father till his lst day on earth, a sanyaye yace “to xan koma In’sha Allah dad, nagode” Dad yyi murmushi yace “toh Allah yi maka albarka, ya raya maka yaran ka ya albarkaci rayuwarsu, ya baku xan lfya da hkuri da matar ka” Khaleel yyi murmushi a sanyaye yace “Ameen Dad” snn ya mike yyi ma Dad dinsa sallama yace xa su tafi, dakin Ummi ya tarda Ashfah yace ta taso su tafi, Ashfah ta mike da kyar tana kkrin mayar da hawayen idonta ganin Sudais ma nn xa su bar shi, ita kuma abu kadan ke sa ta kuka ba kmr Ashnaah ba, sallama tayi ma Ummi, Ummi ta rakosu har downstairs Ashfah tayi ma dad ma sallama suka fita Khaleel na biye da ita a baya, rasa inda xata xauna a motar tayi, ta bude bayan motar a hnkli ta shiga, shi dae bae ce mata komae ba ya shiga driver seat ya tada motar suka bar gidan, Karfe goma saura suka isa gida, Ashfah ta nufi dakinta da sauri ta dinga rusa kukan rabata da su sultan da akayi, shknn ita kadae xa tayi ta xama kmr mayya a gidan bbu me debe mata kewaye, gajiya tayi da kukan ta mike xaune a sanyaye ta cire kayan jikinta ta daura xani ta shiga wanka, ko da ta fito gown din baccinta kawae ta xura ta kwanta ta ci gaba da kukanta, sha biyu saura Khaleel ya tura kofar dakin a hnkli tare da yin sallama ya shigo, Ashfah ta mike xaune da sauri tana share hawayen fuskarta lkci daya ta shiga dudduba inda hijab dinta yake amma ta kasa mikewa ta dauko don kayan baccin jikinta karami ne, bata taba tunanin shigowarsa dakin a lkcn ba, Khaleel ya karaso kusa da ita ya xauna gefen gado yana kallonta, sunkuyar da kai tayi da sauri gabanta na faduwa, ya dago kanta a hnkli yace”kukan me kike khadija” da ganinta kasan a tsorace take, ta saukar da idonta muryarta na rawa tace “su sultan….” Sae kuma ta fashe da kuka, Khaleel ya lumshe ido ya rungumeta murya can kasa yace “kiyihkuri xa su dinga xuwa maki hutu” Ashfah da ta gama tsorata don tun da take bata taba jin ta a kirjinNamiji ba ta shiga kkrin kwace kanta, ya saketa da sauri ya mike kmr wnda ya tuno abu juyawa yyi ya fice daga dakin yana kkrin mayar da hawayen idonsa.Washegari da safe Ashfah na gama hada break fst ta dawo dakin ta kwanta, Karfe goma saura ta ji fitarmotar Khaleel, sae da ya fita da kusan awa daya snn ta sauka downstairs, dinnin ta nufa don sae yyi break ita ma take yi, taga yyi ba laifi, ta ja kujera ta xauna ta shiga hada tean ta, Khaleel kam clinic ya nufa don amsa kiran da dad din Ameesha yyi da safe ba don ransa ya so ba sae dan darajar mahaifin sa. Da kyar ya iya shiga asibitin jikinsa a sanyaye tunowa da yyi a cikin nn wife dinsa ta rasu, tunanin hkn yasa kwalla taruwa cikin idonsa ya nufi office din boss din nasa bayan sun gaisa da nurses da ke reception, Da farko hkuri dad din Ameesha ya soma basa kan abubuwan da suka faru a baya snn ya bukaci da ya koma bakin aiki a ranan, Khaleel yace “Dad sae dae ko gobe, bn sanar da iyalina xan tafi gun aiki ba,” dad din Ameesha yace “toh bbu matsala, Allah ya kai mu goben” Khaleel ya mike yyimasa sallama ya fita, a haraban asibitin suka hadu da Ameesha, ta gaishesa da fara’arta ya amsa yana murmushi snn tace ya gaida mata Yara ta nufi cikin asibitin.118…..Sae da dad din Ameesha ya kuma kiran Khaleel snnya shirya ranan wani Monday ya tafi clinic, satin sa daya da komawa aiki ranan Najeeb ya samesa office dinsa, Najeeb ya ja kujera ya xauna don tun ranan ba su haduwa ba suka gaisa snn ya tambaye shi ya khadija, Khaleel yace “tana lfya qlau” duk da ya fi sati bae ma sa ta a ido ba, kallon abokin nasa Khaleel ya tsaya yi, yyi mugun mmkin rashin nuna damuwarsa kan hada aurensu da aka yi da Ashfah don ya san yana sonta ssae, amma dae bae taba cemasa komae ba, Najeeb yace “Came to ask for yhurforgiveness frnd, Allah yasa xa ka iya yafe min” Khaleel yyi shiru yana kallonsa don bae gane inda xancensa ya dosa ba, Najeeb ya fiddo wata takarda daga aljihunsa ya mika masa, Khaleel ya karba yana warware takardan, idonsa ya sauka kan content din jikin takardar, Khaleel ya karanta ya fi sau biyar a xuciyarsa ga mmkinsa kuma rubutun Najeeb ne, Khaleel ya ce “wat about this, wats d meaning?” Najeeb yace “yhu remember dat day I forced yhu to birthday party of Maska?” Khaleel dae yyi shiru bae ce masa komae ba, Najeeb ya ci gaba”I got yhu drunk, yes I did! I made yhu recopy dis content to another paper while being drunk, yes I did! And that was hw everything started” kallonsa kawae Khaleel yake da mugun mmki, Najeeb ya ci gaba a sanyaye, “nasan idan ba proof din nn na kawo maka ba baxa ka taba yrda ni na rubuta takardan ba na baka kayi recopyn, frnd forgive me plss nd give me a second chance, I am vry happy dat sai da na roki gafara gun fateema a ranan da xata rasu, kuma tace ta yafe” Khaleel ya gyada kai ahnkli duk da irin tafarfasar da xuciyarsa take yace”And all dis happened as a result of???” Najeeb yyi shiru yana kallonsa , Khaleel yyi murmushin takaici yace “Shan giya! don hka duk wani mashayin giya yyi hasara I get dat, in my next life idan da akwae knn bbu abinda xae kuma hadani da giya, nayi da nasanin sanin giya da fara shan shi, its nt ur fault though Allah ne ya nuna min ishara” Khaleel na kai wa nn ya mike ya fice ya bar masa office din hawaye cike idonsa, sae da yyi kusan sati biyu yana avoidin din Najeeb, Najeeb na bin sa har daga karshe Khaleel ya gaji yace toh ya kai proof din ya nuna ma parent dinsa ya wanke xargin da ake masa, hka kuwa Najeeb yyi yaje ya sami dad din Khaleel yyi masa bayanin komae bbu shakka, dad din Khaleel ya tasa shi gaba suka je gun Abba yyi masa bayani da kansa, ssae jikin Abba yyi sanyi bbuabinda ya iya cewa sae Allah shi kyauta, dad ya kira Khaleel bayan ya koma gida yace “baya son kuma ganinsa da Najeeb” Khaleel ya amsa masa kawae ba don xae iya yin hka ba. Yau satin Khaleel biyu rabonsa da ya daura ido kan Ashfah kullum da safe yake fita baya kuma shigowa gidan sae bayan isha, sae dae kuma duk wani abun da yasan xa ta bukata yana siyo mata ya ajiye mata kan dinnin, yau ma kmr kullum sae bayan isha ya shigo gidan, yana haurawa sama ya ji shesshakar kukanta, har xae shiga dakinsa sae ya fasa don lkci daya hnklinsa ya tashi ya nufi kofar dakinta ya tura tare da sallama ya shiga, xaune ya sameta kasa ta hade kae da gwiwa tana kuka, tana jin an bude kofarta ta dago kai da sauri, kasa karasowa cikin dakin yyi jikinsa yyi sanyi ssae lkci daya Ashnaah ta fada masa in dae ya ji kukanta to a irin wnn yanayin yake shigowaya sameta, Ashfah ta shiga goge hawayen fuskarta ba tare da ta kallesa ba ya karaso cikin dakin yana kallonta ya duka gabanta a hnkli yace “Me ya faru khadija” shiru tayi bata ce komae ba ta sunkuyar da kanta, ya dago fuskarta yana kallon idonta da yyi ja ssae a sanyaye yace “ki gaya min plss, kina son wani abu ne” ta fashe da kuka bata ce komae ba, dagota yyi ya xaunar da ita gefen gadon ya xauna shi ma, taki Bari su hada ido, ya kuma dago fuskartayace “ki gaya min damuwarki don Allah” kin cewa komae tayi, ya gaji da tambayarta ya mike a sanyaye ya bar dakin. Kasa bacci khaleel yyi cikin dare, don duk ta daga masa hnkli tunda bae san me ke damunta ba, daya da kusan rabi ya mike da kyar ya fita daga dakinsa ya nufi nata.love yhu ol Fanz.