Labarai

faston da ya yi wuff da zuka-zukan ‘yam mata 4 a rana daya, matansa 5 yanzu

Zagabe Chiluza, mutumin daya fito da ga gabashin Kongo, ya bar mutane da dama da sakin baki inda ya auri mata dai dai har 4 a lokaci daya. Faston wanda ya kasance yanada wata mata ya gwangwaje kansa da zuka zukan ‘yan mata har 4 inda aka yi shagalin biki mai kayatarwa.

A cewar AfriMax,Faston ya kasance kullum yana bada wa’azi akan auren fiye da mace daya inda yake cewa auren mace fiye da ɗaya ba laifi ba ne. “Ina da mata daya, kuma yau zan kara auren ‘yan mata har hudu, ya bayyana haka a ranar shagalin auren.

Auren mace fiye da daya abune da addinin sa ya yarda dashi.

Ya yi iƙirarin Cewa auren mace fiye da daya ya samo asaline daga Littafi Mai Tsarki .Yakubu ya ce, “Ni,jacob Allah ya azurtani da mata hudu Leah,Racheal,Bilha, Zilfa…ina matukar farin ciki da Allah ya azurtani da mata biyar.”

Wasu mabiya cocin Zagabe sun yi na’am da wannan ra’ayi nasa inda suka bayyana cewa addini ya yarda da auren mata fiye da ɗaya a cikin Littafi Mai Tsarki. AfriMax ta yi kokarin ziyartarwannan faston wanda yanzu shekara daya kenan da rabi da ya angwace da matansa a gidansa, kuma suna cikin farin ciki da kwanciyan hankali.

Daga LabarunHausa

               

[ad_2]

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button