MAKAUNIYAR KADDARA 46

 

*Page 46*

………Koda akazo yin breakfast yau gaba ɗaya gidan aka haɗu harsu 

Momie domin nuna murnar dawowar Hajiya iya. Aiko taji matuƙar jin daɗi 

dan bakinta yaƙi rufuwa. Little na jikinta tana bashi da kanta. Ita 

Zinneerah ma har mamakin yanda ya saki jiki da kowa takeyi, gashi yanzu 

ta fahimci dai yana neman zama ɗan gidan. Har ranta tanajin daɗin yanda 

kowa bai taɓa gano alaƙarta da little ɗinba. Amma idan ta tuna randa 

zasu iya sanin abin na damunta da sakata a fargaba.

        Tunda ta zauna bata yarda ta kalli inda AK yake ba, dan ta samu 

ta ɗan maƙale ne jikin aunty Safiyya ba sosai ake iya ganinta kamar kowa 

ba. Garama Huzaifa da yazo zai zauna sai da ya tsokaneta. Murmushi kawai 

tayi dan ita kam ba iya irin wannan wasan tayiba saboda miskilancin ta. 

Shima dai ya fahimci miskilarce, hakan ya sashi faɗin, “Like Husband 

like wife”.

     Murmushi su Baffah duk sukayi, yaran kuwa kowa yay ƙasa da kai yana 

gumtse dariya. Ita dai Zinneerah ba sanin inda ya dosa tai ba. AK kuwa 

yi yayi kamarma baiji mi Huzaifa ya faɗaba, ya maida hankali gacin 

abincinsa kawai dan hajiya iya ta riga tai musu sabon idan suka zauna 

gaban abinci shi kaɗai suke bama dukan nutsuwarsu har sai sun kammala.

      Shine farkon tashi, kamar an tsikari little shima ya miƙe daga 

jikin hajiya iya yana faɗin, “Abbana zanje”.

      Yanda yay zaram ɗin ya miƙe da maganar tasa data fita raɗam ya 

saka kowa yin dariya, banda Zinneerah da aranta take raya (kajimin yaro 

da shegen ɗafa, wai Abbana).

     AK kam dawowa yay da baya yasa hannu ya ɗaukesa yana murmushi, ba 

komai kesa little na ƙara manne masaba sai yawon da yake fita da shi, 

shiko yaro dama akwai son yawo shiyyasa duk inda sukaga maza koda basu 

da wayo suke maƙale musu. Balle little dake da wayo masha ALLAH.

       “Sweetheart kaima fa ka iya yawo na lura”. AK ya faɗa lokacin da 

suke nufar ɗakinsa shi da little. 

      Mommy dake binsu da kallo ita da Baffah tace, “Ƙuruciyar little 

tamkar Adnan, har wayon tsiyar ya kwaso bai rageba. Wani irin bugawa 

ƙirjin Zinneerah yayi a take, har takai ta ɗago ta kalli Mommy batare 

data saniba. Haɗa ido sukai da Hajiya iya dake kallonta cike da nazari 

ita, tai saurin maida kanta ƙasa. Harga ALLAH maganar ta daketa shiyyasa 

duk abincinma ya fita mata a rai. 

       Ganin yanda taketa faman juya cokali a cikin abincin Hajiya iya 

tace, “Inno kin ƙoshi ko?”. Da sauri tako ɗaga kanta jin ta samu mafita, 

kafinma Hajiya iya ta sake cewa wani abu ta miƙe da sauri. Sauran da duk 

basu san mike faruwaba basu fahimci komaiba. Da wannan damar Zinneerah 

ta samu ta silale daga wajen ta koma ɗaki.

     Tayi zurfi a tunani sosai Hajiya iya ta shigo, harta zauna 

Zinneerah batasan da zuwantaba, sai da ta gama mata kallon nazari tsaf 

sannan ta taɓata. Nufashi Zinneerah ta kawo a zabure, sai dai ganin 

hajiya iya ya sakata sauke ajiyar zuciya da ɗan ƙaƙaro murmushi. 

      “Granny ashe kin shigo? Bara na ɗauka miki maganinki kisha”. Tai 

maganar tana ƙoƙarin tashi. Kamo hannunta Granny tayi ta maida ta ta 

zaunar. Hakan yasa Zinneerah ɗan kallonta. Amma ganin itama kallonta 

Granny keyi saita maida kanta ƙasa dan kallon ya banbanta da wanda ta 

sani. “Kamannin Abdul-Mutallab da Moddibo na ruɗaki ko? Muma haka suke 

ruɗamu a koda yaushe. Sai dai nasan jinine kawai yasa Hauwa’u haifo mai 

kama da Moddibo”.

     Ɗan murmushin yaƙe kawai Zinneerah tayi kanta a ƙasa har yanzu, 

Hajiya iya taci gaba da magana batare da ta damu da yanayin Zinneerah 

ɗin ba. “Ki shirya zuwa anjima da yamma hajiya Zulai zatazo ku wuce 

katsina akwai wani aike da zaku kaimin amma ke da ita kawai zakuje”.

      Saurin ɗagowa Zinneerah tai ta kalli Hajiya iyan a karo na farko, 

dan itafa tama kanta alƙawarin bazata ƙara taka ƙafarta katsina ba 

saboda tsoron karsu Hajiya su ganta. Duk da a yanzu tafi ƙarfin a ƙara 

kaita inda aka kaitan, kuma tasan ba gidan yankan kai baneba kamar yanda 

ƙuruciya ta sata kiran wajen a baya.

    Cike da basarwa Hajiya iya tai ɗan dariya, “Oh wai kokin taɓa zuwa 

Katsina ne Inno?”.

      Murya a raunane Zinneerah tace, “Sau ɗaya Granny”.

      “Kai, duk da kasancewarki bakatsina? A to karma ki faɗa gaban su 

Jamal sumiki dariyar Danya kawai kika sani”. 

     Ƴar dariya tayi saboda yanda hajiya iya tai maganar cike da raha. 

Batare da tunanin komaiba tace, “Granny ai shima aiki Inna tasa wata 

mata taje dani nayi bama yawo naje ba”.

       “Aiki kuma? Kina nufin aikatau fa kenan?”.

      A take damuwa ta bayyana akan fuskar Zinneerah, ƙwalla suka ciko 

mata idanu, murya a raunane tace, “Eh aikatau Granny, ni bansan miyasa 

Inna bata sonaba. Dagafa wata ƙawarta tazo ta bata labarin kuɗin da ake 

samu shikenan tasa na bita ko baba bai saniba. Amma tsabar sharri dana 

dawo sai tace wai yawon banza naje, wlhy kuma ba yawo najeba”.

        “Toke miyasa baki faɗama Babanki gaskiyar abinda ya faruba?”.

     “Haka kawai naji inajin tsoro Granny, koma nayi niyyar faɗa masa 

saina kasa dan Baba tsoron Inna yakeji saboda masifarta wlhy, bama shi 

kaɗaiba ƴan garinmu da yawa tsoronta sukeji dan jarababbiyace sosai”.

      “Kai wannan mata ALLAH ya wadaran halinta, ina daɗi ace miji na 

tsoronka. To amma ke miya faru har tasa aka tafi dake aikatau babu wanda 

ya sani, harma ta samu damar miki sharri kinje yawo?”.

    Hannu Zinneerah tasa ta share hawayenta daketa sakkowa saboda tuna a 

yanda tabar Danya wancan lokacin, babu wani tunanin wayon manya Hajiya 

iya ke mata ta fara zayyana mata yanda abin ya kasance.

      “Hajja lanti ƙawar inna ce sosai, dan nidai tare na sansu tunda na 

fara wayo, dan Hajja Lanti dillaliyace a garinmu, tana kuma saida 

abubuwa iri-iri. Daga baya kuma ta koma ɗaukar yara tana kaiwa aikatau a 

birni. Hajja lanti ba sona takeba itama, shiyyasa bana murna da zuwanta 

gidanmu, dan duk randa tazo da wahala kaga harta tafi Inna bata dakeniba 

saboda tsaban iya haɗa gulmanta. A wata ranar asabar na dawo daga tallan 

gyaɗa da riɗi a gajiye na iskesu zaune a tsakar gidanmu suna magana da 

ban san kota micece ba. Ni dai na gaidasu na bama Inna kuɗin tallar na 

shige ɗaki dan tace karna sake zama a tsakar gida idan tayi baƙi. Ban 

jima da shiga ba ta ƙwalamin kira. Koda na fito sai da suka gama min 

kallo na wani lokaci ne naji hajja Lantin na cewa “Ai wannan ma itace 

dai-dai a yanzu. Dan za’a jima ana samu tattare da ita”. Bansan ina 

zancen nasu ya dosaba. Ni dai Inna tacemin naje na canja kaya nawuce can 

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button