HAUSA NOVEL

FATU A BIRNI COMPLETE HAUSA NOVEL

 

Maman Fateey????????

[12:06PM, 8/1/2016] Mum Fateey: ????????????????????????????????????????????

????????????FATU A BIRNI???????? ????????????????????????????????????????????

Na Mrs Aslam Haidar✍

3⃣7⃣

 

Basu sha wahalan gane gidan ba duk da dan sauyin da aka samu kusan shekara da rabi, yau ma a kofar gida suka samu mal Ameenu yana zaune da wani mutum suna magana. Tun dosowar motar mal Ameenu yake kallonta duk da bashi sultan ya taba zuwa da ita ba amma yana kyautata zaton yau fatu tazo da mijinta. Nesa dasu kadan suka parking yayinda suka fito kowa da dan murmushi a fuskarsa, ganinsu yasa mal Ameenu fadada fara’arsa kaman an mishi bushara, yana leqen bayansu yaga ta inda zaiga *FATUN BIRNI* Kawu muntari da yake gefen mal Aminu yace “baba, ko dai maigidan fatu ne yazo? Gyada masa kai yayi saboda sun iso, sallama sukayi aka amsa musu suka sami guri akan babban tabarman suka zauna, kaka yace “muntari shiga gida ka samo musu ruwa” kawu muntari ya tashi da sauri ya shiga gida. Gaggaisawa sukayi cikin mutunci kaka bakinshi yaqi rufuwa sai hamdala yakeyi yace “ai na aza da ita zaku zo, ashe ku kadai ne” Jameel yace “na’am baba” don bai fahimci maganar ba sultan ma haka. Kaka ya cigaba da cewa “bbu abunda zance maka sultanu sai Allah ya maka albarka, yasa ka gama da duniya lafiya, wato naji dadin wasiqarka, shekara da auranku baka zo ba, nayi tsammanin ko baka son hadin da aka maka ne, har na fara maganan raba auren ganin yanda aka fara surutu a kauyen nan, mutane sunyi gaskia da suka ce ‘mai hakuri shi kan dafa dutse har yasha romonsa’ nan din ma hakan ya faru, ranar da kayi aika ta hadu da mal usman a hanya ya bata saqon kamar kullum” kallonsu kaka yayi da fara’ar da har ynzu bata bar fuskarsa ba, daga jameel har sultan sun zuba mishi ido, ya cigaba “wasiqan da na gani a ciki yasa na dauka ko ka sauwaqe mata ne, data karanta muka gane” daria kaka yayi amma babu wanda ya tayashi don gabadaya kansu ya daure, sun rasa inda maganarshi ya dosa, fitowan muntari yasa jameel cewa “me ya rubuta” muntari yace “rubutawa sultanun yayi cewa fatu ta bishi gombe zai yiwa mamarsa bazata, ko ba haka kace min ba baba? Kaka ya amshe “ehh” muntari yace “ai naso inje aga gurin da kuke din saboda ziyara, amma fatun tace ita kadai kace taje” tari ne ya sarqe sultan yanayi ba kakkautawa ruwa aka miqa mishi yasha sannan ya tsaya idonshi har yayi jaa, Jameel ne yayi qarfin halin qaqaro murmushi yace “haka fa, abun zai kai wata nawa ma? Daga kanshi yayi kamar mai son tunowa muntari yayi caraf yace “wata takwas ai ko” kiran sallah azahar da aka fara yasa sukayi shiru kowa da abunda yake saqawa a ransa, sai da aka idar mal Ameenu yace bari a kawo muku buta kuyi alwala, shiga gidan kaka yayi da kawu muntari aka barsu su kadai, a sannan ne sultan ya dubi jameel da tsananin damuwa a fuskarsa don a yanzu sun gane komai daya faru yace “ina cikin duhu jameel” girgiza kai jameel yayi yace “ita ta rubuta wasiqa kace taje, tun wata takwas da suka wuce kuma da alama har yau bata dawo ba, sultan, fatu ta bata” shiru sukayi sultan ji yakeyi kamar ya kurma ihu ko zaiji sassauci a zuciyarsa, _FATU TA BATA! IDAN MAL AMEENU YA GANE BATA TARE DASHI YA ZAIYI? IDAN MAHAIFIYARSHI TAJI ABUNDA YA AIKATA HAR HAKAN YA JANYO BACEWAR YAR QANWARTA YA ZAIYI? SHIN FATU TANA RAYE? IDAN TANA RAYE TA INA ZAI FARA NEMANTA? TA INA?_  Tambayoyin da suka cika brain din sultan wanda  babu wanda zai iya amsa mishi, ji yayi zuciyarshi na zafi yana ganin duhu duhu, hakan yayi daidai da fitowan kaka da muntari suka ajiye buta miqewan da sultan zaiyi yaji kanshi yayi nauyi ya zube a qasa.

 

Maman Fateey????????

[6:48PM, 8/1/2016] Mum Fateey: ????????????????????????????????????????????

????????????FATU A BIRNI???????? ????????????????????????????????????????????

Na Mrs Aslam Haidar✍

3⃣8⃣

 

“Innalillahi wa inna ilaihir rajiun” abunda kowannensu yake furtawa kenan sukayo kanshi, jameel ne ya shiga jijjiga shi yana “sultan, sultan ka tashi” yama manta cewa shi doctor ne, ruwan buta yasa aka miqo masa ya yayyafa masa, ajiyar zuciya mai qarfi ya sauqe kafin ya bude idonshi a hankali yace “ina fatu? Ganin zai qara magana yasa jameel saurin cewa “mu daga shi mu kaishi mota, dole sai an kaishi asibiti” mal Ameenu da yake da salallamai a gefe yace “muntari tayashi ku dauke shi, maza maza” hannayensa suka saka a kafadunsu suka kaishi mota kaka na “ashsha Allah ya bashi lafiya” yana girgiza kai. Suna sakashi a mota yana cewa “ina fatu? Ina fatu? Jameel yayi saurin shiga driver sit ya kunna motar, yana tunanin yanda zasu fara nemo fatu, tunawa da yayi cewa fateema ta yaga pic din fatu da suke dashi yasa yayi saurin fitowa daga motar ya samu kaka fuskar shi gwanin tausayi muntari na cewa “baba, sai cewa yakeyi ina fatu fa” alamar akwai matsala kenan, kaka na ganin jameel bai ko saurari muntari ba yace “jikin ne? Ko dai a qira madam nasi (nurse daya da suke dashi a qauyen) ta dubashi? Jameel yace “a’a nima doctor ne, fatu yake son gani, in akwai hotonta a bani” kaka cikin jimami yace “kayya wannan wani irin cuta ce? Fatu bata daukan hoto sai hoton ta daya da aka dauketa tana shekaru uku” da azama jameel yace “a bamu” kaka yayi saurin shiga gida muntari ya mara masa baya, shi kuma jameel ya koma gurin sultan a mota. Yana isa ya samu sultan ya fara dawowa hayyacinsa yace “yarinyar nan tana son kashe ni, tana jawomin matsala a rayuwata ta koyaushe, ina take? Bubbuga bayanshi jameel yakeyi yana cewa “be strong, be strong dude, zamu nemota insha Allah, I’m with u” jameel kaman ya fadawa kaka batan fatu amma yana hango tsananin tashin hankalin da zasu shiga in suka ji labari shiyasa ya shirya qaryan cewa sultan nason ganin hoton ta ne, fitowa kaka yayi muntari na binshi a baya kamar jela, da sauri jameel ya isa gurinsu ya karbi hoton tare da cewa “mungode, amma dole sai mun dangana da asibiti” muntari yace “to wani irin cuta ce wannan da zaisa mutum suma ya tashi da son kallon matarsa? Kaka ne ya harare shi kana ya maida kallonshi kan jameel yace “ai ya kamata ku hanzarta tafiya kafin wata matsala ta kunno” sallama sukayi jameel ya koma mota, ya samu sultan ya dafe kanshi yace “ka rage tunani sultan don kar ka jawowa kanka matsala, zamu nemota duk inda take” motar yaja suka tafi suka bar kaka cikin daurewan kai, meke faruwa ne?

 

Fatu na kwance kamar wacce aka tsikara ta tashi tace “xahra akwai matsala” xahra tasa pause ta juyo tace “a ina? “Yanzu idan suka je suka fadawa kaka bana tare dasu wallahi hankalinshi zai mugun tashi dama gashi da hawan jini, yanzu ya zanyi? Ido xahra ta qura mata tana tuna maganar fatu da take cewa rayuwarta kamar a film, wannan shine asalin film. Kafin xahra ta bude baki fatu ta sauqo daga kan gado ta dauki gyalen dogon rigan da yake jikinta ta yafa kawai tace “tashi muje gidan lubna, kaina ya daure, ban san me zanyi ba, zata fini sanin ya za’ayi” daukan gyalenta xahra ma tayi suka fito a palour suka tarar da mummy sukace zasu je gidan lubna, tace Allah ya kiyaye a gaisheta.

Suna fita daga garin sultan yace “taya zamu nemota bayan bamu san inda ta nufa ba, kuma ko hotonta bamu dashi” Jameel ya miqa mishi pic din da kaka ya bashi ya qurawa hoton ido kaman tana kama mishi da wata daya sani, tunawa da cewa ya taba ganin fatun yasa yabar tunanin, yace “wannan fa tana yarinya ce, ina wanda ka dauke mu? Jameel bai masa magana ba, tunowa da cewa fateema ta yaga yasa yayi zugum yana kallon dajin Allah. Suna shigowa gombe yace “jameel muyi gidanka” haka suka iso kowa da tunanin da yakeyi, ko gama parking jameel baiyi ba sultan ya bude ya fita da sauri jameel ya qarisa parking din ya biyo bayanshi “whats wrong sultan? Ina!! Already ya shige. Ko tsayawa kallon wadanda suke palourn baiyiba ya wuce gurin da dustbin yake ya juye a qasa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button