FATU A BIRNI COMPLETE HAUSA NOVEL

Dawowan farouq yasa fatu sauqowa kasa ta masa oyoyo, yace “bro sultan yace yana gaisheki” kallon mummy tayi taga hankalinta na kan tv don haka tace “yaushe” yace “yanzu na hadu dashi a bakin gate, kin ganeshi? Shine wanda nake baki labarin ya kawo min tsaraba zuwansa china, muje in qara nuna miki tsaraban” fatu tace “awww yanzu na tuna, kaje kayi wanka kayi sallah sai muci abinci, akwai labarin da zan baka” ya tafi dakinsa. Mal usman ne ya shigo ya gaishe da hajia ya tsaya a bakin kofa, hajia tace “sultan ya baka aika ne? Yace “ehh” tace “ka bawa fateema ta dubamin, miqa ma fatu yayi ta bude kudi ne dai har yanzu, har zata rufe taga wata karamar paper da dauka ta miqa wa hajia. Hajia tace “a’a letter dinki ne” rufe envelope din tayi ta bawa mal usman yasa a aljihu. Hajia tace wa fatu shikenan kije dakinki. Ta wuce. Hajia tace “mal usman kamar yadda na fada maka fateema tana nan amma kakanta bai sani ba, haka sultan, inaso a dauka a gidansu sultan take, kakanta kan iya tambayarka fatu, kace masa tana lafiya, kuma a baka takardun karatun ta duka, sultan zai saka ta a makaranta” da saurinsa yace “hajia an gama” kudi ta bashi ya karba yana godia kana ya fita.
Fatu kuwa tana shiga dakinta ta fada kan gado tana tariyo yanda sultan ya mata murmushi, karo na biyu kenan da taga smillin dinshi. Ya qara mata kyau da kwarjini, dazu tayi matuqar yin qoqarin ganin bata kwapsa ba balle ya ganota. Papern tayi saurin budewa, ta fara karantawa
Hii
“”Ki cewa mal Ameenu na gaishe shi, ki kuma bashi hakurin rashin ganina, may be bayan sallah zanzo””
Samun kanta tayi tana nanata wasiqar, duk da ba ita akayiwa ba amma taji dadin sa. Murmushi naga ya subuce a fuskarta can kuma ta fara hawaye, tana tausayin kanta, yanzu zata rabu da mijinta, duk da ba sonshi takeyi ba amma zata so ta zauna da dan’uwanta. Kuma taga yana mata murmushi. Wata zuciya tace fateema yake yiwa ba fatu ba. Kar ma kisa shi a ranki, a duk lokacin da ya gano kece fatu bazai qara kulaki ba. Wasu zafafan hawaye ne suka qara gangaro mata tayi saurin gogewa, farouq ne ya shigo dakinta wai ta sauko yin lunch, goge fuskarta tayi suka fita tare da yake tana fashin sallah.
Acan garin modibbo kuwa mal usman ya kai saqo kamar kullum. Mal aminu ke tambayarsa? Ina uwargidan nawa, da fatan tana lafiya? Mal usman yace “tana lafiya kalau, tace a gaisheka ma. Kuma a bata takardun makarantar ta zata cigaba da karatu. Cikin jin dadi kaka ya dauko komai da komai ya bashi, da yake duk takardun nata a gurin kaka yake.
Bayan mal usman ya dawo ya bawa hajia, nan da nan tasa a nema wa fatu admission a GSU cikin qanqanin lokaci aka sama mata, aka gama komai ta fara zuwa lectures.
Anan zamu tsaya a FATU A BIRNI insha Allah bayan sallah zamu cigaba.
Kuyi hakuri na rashin post da wuri hakan ya samo asaline na rashin charge.
FATU NA MUKU HAPPY RAMADAN????????????????????????
Allah ya bamu ladan dake cikin wannan wata ta Ramadan. Ameeen
[3:15PM, 7/11/2016] Mum Fateey: ????????????????????????????????????????????
????????????FATU A BIRNI???????? ????????????????????????????????????????????
Na Mrs Aslam Haidar✍
2⃣2⃣
Kwanaki sun shude yau watan fatu biyar da barin garinsu tayi nisa a karatunta kuma tana fahimta, qawarta daya sunanta itama ma fatima. Qawancen su ya samu asali ne ranan wata monday fatu tayi latti sosai gashi har an shiga lecture kuma lecturer baya barin a shiga, fatu sai safa da marwa takeyi a bakin hall din, fatima da take ciki ta hango ta sai ta bata tausayi, don tana lura da fatu, irin dodging lecture da students sukeyi ita sam bata yi ga kokari kamar me! Tana cikin tunaninta taji an jefe ta da abu; dumm gabanta ya fadi don tasan lalle yau zai korata waje, maimakon taji ance yi waje sai taji yace “Me kike kallo a waje? Bata san lokacin da tace “qawata ce” “u can join her” abunda ya fada kenan. Zare ido ta fara yi tace “sir bata da lafiya ne, ko dazu she called me tace bazata samu zuwa ba, so ganinta da nayi ne ya ban mamaki” sai da yayi dan jimm sannan ya mawa fatu hannu da take waje ta sake baki tana kallon ikon Allah. (Sana’ar ta ne dama sake baki????). Sai da ta shigo yace “get well dear” tana in ina tace “thank you sir” guri ta samu ta zauna aka cigaba da lecture. Bayan ya fita ne ta samu fatima ta miqa mata hannu hade da sallama ta amsa hade da shaking hannunta. Fatu tace “amma kin taimakeni nagode sosai, gashi ya bamu light akan abunda zai fito a exams. Fatima tayi murmushi tace “ai kuwa, me sunanki? Fatu ta amsa “Fateema Mahmud” tayi carab tace “sunan mu daya amma ana kira na xahra levels” fatu tace “I like it” xahra tace “tnks namesey”
Haka qawancen su ya cigaba cikin aminci. Suna ziyaran junansu lokaci lokaci, hajia ta yaba da hankalin xahra shiyasa take barin fatu tana ziyartar ta. Bangaren sultan kuma soyayyar fateema ta gama narkewa a zuciyansa, sukan gaisa amma daga nan yake tsayawa, dan gaisuwan da yake yawan shigowan ma ya rage, don akwai ranar da yazo fatu tana ganinshi ta haura sama, yazo ya zauna suka gaisa da mummy, hajia tace “nikam sai kora min ‘ya kakeyi, da ta ganka sai ta tafi” yayi murmushi yace “afuwa mummy” Haka suka cigaba da hiransu har yake tambayanta daddy tace yana Abuja, don shi bai cika zama a gida ba, lokacin zuwan fatu ma baya gida, da ya dawo hajia ta bashi labarin ta bai yi comment akai ba, illa cewa da yayi Allah ya taimaka. Yasa hajia ta kira masa ita ya mata questions akan rayuwarta ta bashi amsa, kana ya mata nasiha yace ta dauki gidan kamar gidansu, kuma ta maida hankali akan karatu.
Yau shirye shirye akeyi a gidan don tarban manyan baki, mahmud ne zai dawo daga cyprus sai jameel da matarsa suma zasu dawo daga south Africa. Hajia ta kasa zaune ko tsaye haka fatu, duk wani shiri da girke girke an kammala sai isowan su kadai ake jira, karfe 2 na rana sukayi waya sun sauqo, nan da nan hajia ta aika driver a dauko su, farouq yaso a je tarbansu hajia tace nooo. Bayan tafiyan driver fatu tace wa hajia zata je tayi wanka kafin su dawo, hajia tace to. Fatu ansha aiki, tana shiga daki tace bari ta dan miqe a gado kadan, bata san lokacin da bacci ya kwashe ta ba.
Jameel sun dawo cikin dokin ganin gida, hajia tayi murnan ganinsu harda kwallanta, farouq murna kamar ranar ne sallah. Bayan an gama gaishe gaishe aka nufi dinning cin abinci, amaryan jameel, lubna mai dauke da qaramin ciki tafi kowa kwasan girki, sai santi take zubawa, mahmud da yake qanin mijinta yana ta tsokananta kota kulashi, mummy dai dadi ya hanata magana. Can hajia tace “mahmud kai kuma maimakon kana gama karatunka kayo gida shine ka biya can south africa ko, wato ko missin din gida baka yi? Riqe hannunta yayi yace “wlh mummy jameel ne ya dameni wai in biya can tunda suma sun kusa dawowa wa, mummy 3 wiks kawai nayi a can din fa” ya qarasa maganarsa cikin shagwaba, daria sukayi lubna tace “ji shi kamar wani yaro” “yaro nake tunda ban kusa ajiye baby ba” mahmud ya bata amsan da ya saka ta kunya, don haka tayi shiru. Murmushi Jameel yace “mummy nafi son mu dawo rana daya ne thats why nace ya biya can, nd he enjoyed staying there” hajia tace “Alhamdulillah tunda kun dawo lafiya all, sai shirye shirye walima da party na taya murna, in da next 1 week” murmushin jindadi mahmud yayi yace “thanks mum, Allah ya biyaku dawainiyan da kukeyi akan mu” dukansu suka amsa da Ameen.