GAMO DA KATAR Complete Hausa Novel

Momy ta duba tace” kai kai kai gaskya da yayi Narim ce gatanan harda hannu cikin baki boy ya yi kyau ina ka ko yi zane nima dai momy naga na zanata
To yanzu ina ka barota tana d’akina tayi barci to da ta tashi ka kawota ta sha madara yace to ya”fita momy ta jinjina kai.
Da dadare momy taje ga mijinta daman haka takeyi idan taje ta ba mujinta haqqin shi sai ta dawo saboda Narim cinda bai so Ajeda ita d’akin shi yasa take komawa nata d’akin tunda ta haihu
Tabar su Nuraim da Narim kwance d’akinta Aman da ta dawo sai bata gansu ba koda ta shiga d’akin Nuraim sai ta ganusu kwance ya rungume ta kamar zai maidata cikin ciki sai barcin su suke ga madara nan gefansu inta farka ya bata momy har’ zata ta da shi sai ta qyaleshi ta matsa da niyar daukan Narim taji rungume yake da ita sai kace wani zai qwaceta.
Nuraim sarki rigima inji momy Nuraim na Narim yau kuma nan Akadawo hijira a kai mani Adu,a ta tofa masu sannan tafita tai nata d’akin duk da dai duk waje daya suke. Babban porlour ne mai dauke da kichine da da kuna guda ukku kowanne da toilet din shi to Nuraim nada d’aki guda yana kallon yana kallon d’akin momy .
Tunda momy tabaro d’akin Alhj isah yake tunani wacce hanya zaibi yau ya fitar da yarinyar nan daga gidan shi dan shifa wallahi bai rugon dan kowa balle tsintarciyar mage wadda bai san Asalinta ba.
Sai tufka da warwara yake shin gidan marayu zai kaita to inya kaita gidan marayu cikin wannan daran sai sun tuhumeshi daga ina yake da ita?”
Kuma shi bai son kowa yasan shi ya dauke ta.
Haka dai ya yanke shawara guda shine ya dauketa ya jefa cikin ruwa kifi ko kada su hadeta Ahuta ko kuma ruwa su tai da ita dan inba haka yayo ba to ko ina zai kaita momy zata iya samunta dan za Abaza a kafafan yada labari”
Sai da yabari dare ya yi sosao wajan qarfe biyu na dare sannan ya tashi yasa jallabiyar shi ya dauki kye din motarshi yasa Aljihu yafita zuwa d’akin momy sadaf sadaf take tafiya Ahankali ya tura door din d’akin dan kartaji qara kuma batajiba saboda qofar batada qara shiga ya yi yasamu sunata barcin su to ina Nuraim ya laiqa fuskar diyar dake gaban momy dayake Akwai hasken fitila irin wannan fitilar mara haske sosai ga mamakinshi sai yaga Narima ce gaban ta .
wani dadi yaji ya lullu6eshi kenann Nuraim na tare da ita dan haka cinki hanzari ya fita jikin shi har’rawa yake yana shiga ya gansi kwance suna barci Aman shi Nuraim ya juya mata baya duk da haka ta bayan shi saida ya Azamata hannu dan yarinqa jinta Allah sarki Nuraim kana son Narim sosai gashi za,a rabaka da ita????????
cikinn’sanda yasa hannun shi Ahankali ya dauke hannu Nuraim dake bisa jikinta dayake barci yayi Awan gaba da shi dan bai dade da tashi ba yabata madara da ta farlka shiyasa da ta koma barci shima ya juya kwanci sai barci yai gaba dashi barci baka kyauta ????
daukarta ya yi tare da zananta ya fita zuwa waje motar shi ya bud’a baya ya Ajeta sai ya ciro wayar shi yaje yaga mai gadi na barci wayar qarya yake kasan cewar akwai yan sanda sai yai bige yana cewa oky oky bani minta goma ganinnan zan tafo kayan sun iso kenan?
Yan sadan yace su bude mashi get zaije kayansu suka iso suka bude mashi get ya tada motar shi yafita kan titi sai tunani yake ina zai kai ta .
sai ya tanke shawar kai ta bakin ruwa ya aje ruwa sugaba da ita haka kau akayi can ya nufa ya kashe motar shi ya bud’a ya fito da ita rungume da ita Allah sarki Narim jin sanyi wajan da kuma isaka shi yasata bude ido tana kallon shi shima ita yake kallo ko tau sai bata bashi ba
haka ya matsa da ita bakin teku ya aje dayake akwai hasken farin wata kamar rana sai kalle kalle take zuwa chan ruwan teku sukayi’qugi wanda ya tsora ta ta ta fashe da kuka shi kan shi sai da ya tsorata yai tsalle ya matsa gefe domin ruwanne suka tafo cikin hukuncin Allah sai basu kawo inda Narim ke kwance ba
ko tau santa bai jiba haka ya yajuya ya komawar shi cikin mota bai ko wai wayotaba zuciyar shi wasai Narim sai kuka take yanajin kukanta haka yatada motar shi ta tafi….
Kai jama,a wannan rashin tausai ne ko rashin imani?
shifa da nakowane kuma ba kasan wannada zai tai makekaba kuma kowanne dan Adm da irin baiwar da Allah yai mashi Allah shi kyauta Allah kasa mufi qardin zuqatanna Alhji isah kayi kuskure babba..
tun da yafito daga gida yake biye da shi har yazuwa yanzu da ya Aje Narim.
duk Abida ya faru akan idan shi kuma ya tur da halinshi ya so ya dau mataki akan Abida yayi Aman sai ya qyale shi duniya ta horashi.
wajan Nar din ya nufa wadda keta tsala kuka sanyi da iska sun isheta hannuwanshi yasa guda biyu ya dauke ta ya rungumeta aman still bata dana kuka ba dan haka sai yasa hannushi guda kan fuskarta ya shafa fukarta take barci ya dauketa ya yi tunani ya tai da ita wani waje daban aman sai yaga zamansu waje guda ba zai yuyuba.
shin waye wannan bara muji sanye yake da doguwar riga fara qal jallabiya mai dogon hannu tsayin rigar har qasa domin ko qafafun shi baka gani kanshi kuma qaton rawanine shima fari sai doguwa cabzaha wato cabci dogo shima manyan duwatsu shima fari.
ya jima dau da Narim bakin ruwa yana mata Adu o,i yana tofa mata daga qarshe ya yi murmushi yace” Alhji isah kayi kuskure..
wata hanya yanufa da ita bai zame ko ina ba sai wata rufar kwano mutanene kwance waja birjat sai yaja ya tsaya yana duban mutanan dake kwance wajan
yanan tsaye yaga wata mata tafito daga wani shago tana tafiya zuwa bayan shagon da yar buta ga hannu har ta kawo wajanshi ta wuceshi yana tsaye harta dawo zata wuce shi yai mata magana sallama yafara yimata
ba zato ba tsammani taji maganar shi duk da cewa sallamace yai mata sai da gabanta ya fadi jikinta na tarawa cikin karkarwa bakinta na rawa ta amsa mashi sallamar tace bawan Allah lafiya cikin darannan ?”
karka cutar dani ni makamniyace ban ko gani dan Allah kar kacuta man yace” inna kwantar da hankalinki ni ba mucuci bane kuma na san da make bagani kike ba shiyasa nazo wajanki
magana yake antar cikinta kadawa take jitake wani sanyi na shigar ta tace ti nida ba gani nake ba wanne tai mako zan iya yi maka kane mi masu ido yace bawani dogon zance tai mako nake so kuma ke zakiyi manshi ai naga masu idon na nufo ki to ina jinka fadi inji..
sai yace ” yauwa na gode inna kawo hannuki sai ta miqa mashi hannuta guda sai yace” biyu saki kawo ta miqa maahi hannuwanta biyu ya dora mata Narim bisa hannuwanta jikinta na tarawa yace” natsu kar kiyarda mana inna tototo haka take Ambata
tace bawan Allah ya naji kamar jariri yace” eh jinjira ce kuma kena ba Gatanan Amana to nida banida ido ya za ai nayi reno yace Allah da yabaki yafi ki sani yanda za ai kidai ruqe Amana dan na son zaki iya to ina uwarta batada uwa marainiya ce Allah sarki to bawan Allah yanzu dai bani kade nake ba ina tare da mijina dan haka mutai gani gaka gashi kai harda ma mutanan dake wajannan A tadasu ayi ga bansu suzama shaida ko ya kace yace hakane inna
karki damu dan yanzu zakubar garinnan yanzufa kace bawan Allah cikim darannan ina zamu samu mota kuma niko kudi bandasu yanzu yanzu ai sai Allah mubari dai har garin Allah ya waye yace inna mutai wajan malam tace to suka tafi ta shiga ta tado malam shima yaji Abin Al ajabi bayan inna tai mashi bayani sai malam Yace bakomashi Al amarin ubangiji sai kallo dan haka zamu Amsheta da hannu biyu kuma zamu ruqeta Amana