GAMO DA KATAR Complete Hausa Novel

Hajiya tace bbyn nan ta ma 6ata pompas dinta bara Acire A gyara mata Inna tace” to ruwan zafi tad’ebo ta wanke mata gaba d’aya tai mata wanka ta kuma dama madara ta bata Inna na zaune tana jinsu Hajiya tace ma Amar ya kira mata d’aya daga cikin yaron dake masu Aiki ta Aike shi Amar yafita zuw can sai gasu tare pompos tasa ya siyo mata mai kwara Arba’in da kayan jarire da man jarire mintina kad’an ya dawo kafin lokacin maman maryam ta kawo mata kokonta sai Hajiya tace”
ta tafi Amar ya rakata tace to
bayan ta shafa mata mai tasa mata pampos da sabin kaya harda turare sai qamshi take ta ji dadin jikinta sai bude idanunta take tana kalle kalle
sosai Hajiya ke son Narim jinta take har’cikin 6argonta shi kansho Amar yana sonta dan sai wasa yake mata ita kuma sai dariya take to Inna gata naga kin’gaji da zaman gashi ko Abincin da na kawo maki baki ciba kin san’ni da san yara bama kamar Narim
dan Hajiya ta tambayi sunan bbyn Inna tace mata Fatima Narim ni kuma Inna sunana
Ah Ah Hajiya ba haka bane baqinci nayi ba waida da shi zan tai cinda da man bara nafito sai Allah ya hadani da maman maryam mijin na chan na’jirana da shi zan tai muci
oky hakan yayi bara sai Aqaramaku Hajiya tace da Inna to mun’gode Hajiya Allah ya qara budi Bayan Hajiya ta qara mata Abinci sai ta bata Narim tace to Inna yanzu Anzama daya ina so yar’ki zan runqa tura Amar yana kar6o’man ita to shikenan Hajiya Ai kema yar’kice Narim takice to Na gode Inna bakomai sai Hajiya tace Inna maganar Bara nan ki dai na zuwa komai zammaki dan kin zama yar uwa zan sa Akawo maku komai Insha Allahu to shikenan mungode Allah yasa kufi haka Amar ya daukar mata kular Abinci ita kuma ta dauki kofin koko bayan ta goya Narim har haraba Hajiya tai mata raki inda take fadin Amar bita sannu ka mamata sandar yace to hannushi yasa ya kamama sandar yai mata jagora suka fita zuwa gida malam ya gaji dajira ya dan shgingi’da duk da hankalin shi na garesi sallama sukayi ya Amsa yace naji shuru da ina niyar tashi nabiku ina kika shiga haka
kai dai bari malam na Allah bai qarewa tafe nake da yaro ka ganshi dan gidan mutumci nan tafada malam ko mai da haduwarta da maman maryam harya zuwa gidan su Amar dakuma Yanda sukayi da Hajiya
malam yace Allah yabiya su ta sauke goyonta ta shifar da Narim kan ta barma shikuma Amar ya koma wajan Narim yana mata wasa su Inana sukaci gaba da cin Abincin su
Amar yace Inna ga katifar ta kin Ajeta qasa katifa Ina katifa ni ban masan da ita ba gatako Inna Amar ya jawo katifa yabata katifa ce’ko babba ta jarire sai lau shi Inna tace bara A maida ta sama ta mai data saman katifar tace malam ni wallahi ban san da wata katifa ba ma ko kai kasani ina nake sani cinda ba gani nake ba balle na ganta Aman Ai ba Abin mamaki bane Abinda da yafi haka ma zaki gani
Inna tace hakanev Amar ta kira sunan shi ya Amsa mata da Na,am Inna sai Inna tace mashi Bayan katifa dami dami ke cikin dakin Amar ya duba yace kayane masu yawa ina tace to kawo man sunan ka gwada mani Amar yace to ya tashi yai ta jido kayan yana Ajewa ga ban’su
Sai da ya kwaso kayan duka sannan yace mata suke nan tace to bud’a kai man bayani yanda kayan suke ya bud’a wata leda kayane na jarire da wanduna ya ciro yana basu ga hannu su yana masu Bayani
Leda d’a ya kuma kayan mayi kane da sabulai Suma na jarire ga pampos
Sai kudi masu yawan gaskye bai san yawan kud’in ba ya dai ce masu ga kud’i dake ciki ya bata ga hannun ta ta laluba kud’ini masu yawa
Amar sai da yaga Narim ta yi barci sanna yai masu salama ya tafi gida
Koda yaje gida Ammy tace sai yanzu yace ei sai Anjima kaje ka kai masu Abinci rana yanzu nasa Asiyo masu sayaya kan da zasu buqata yace Ammy kayan su ma qasa suke ba Akwatin sawa basuda gado balle katifa kan ta barma su gasu dakaya ba wajan sawa tace komai za,a kai masu Amar jeka kira man maman maryam in an kawo kayan sai ta tai maka ta gyara masu cinda su basu iya gyarawa
Amar yace” to ya fita Lagos Hospital
Momy zaune ta buga uban ta gume Abin duniya duk ya ishe ta
Ta zura ma dan’ta ido tana kallon shi ita ba ciwon shi yafi da munta ba illa batan yarta wandda ya zuwa yanzu har ta dai na kuka da hawaye sai kukan zuci wanda ya haddasa mata ciwon zuciya zuciyar ta ta mata nauyi kamar an Aza mata dutsi Allah ka kawo man dauki
Alhaji Isah ne ya shigo yace mata ya mai jikin tace jiki da sauqi gashinan haryanzu dai ko motsawa bai’yi ba
To Allah ya bashi lpya Ameen tace yanzu ya Ake ciki sai yace har yanzu dai bawani labari Hajiya Batan yarinyat nan na da muna”
Nakasa ci nakasa sha na kasa barci saboda tunaninta ko tana raye ko ta mutu Allah kade ya sani tanama raye insha Allah cikin qoshi lpy ,
Yace Allah yasa Bari naje S..p ya kirani yanzu yace man yanazuwa to Allah ya kiyaye Allah yasa Adace Ameen
*PAGE 1⃣3⃣*
Alhaji Bello tafe yake cikin motar’shi yana tunani dada’nasani na salwantar da Narim,gashi ya salwantar da ita Aman bai’da natsuwa koka’dan dan tunjiya dadad’dare Rabon’shi da Abinci,
Yana driven yake wanna’nan tunani wayar shi’ce tayi qara ya dauka difi’o ne ya kirashi ya shai’da mashi gasunan qofar gidan shi suna jiran’shi yace”masu shi’ma gashinan zuwa, suba shi yan muntuna kad’an.
Tunda ya isa unguwar yaga motar yan sanda kusan ukku duk sunfito suna jiran shi waje yai parking din motar shi.ya fito yabasu hannu suka. Gaisa.
Suka sake tatauna’wa Akan kyes din su inda dai har’yanzu bawani issues.
Mutane da dama sai jajanta mashi suke harda kuka yake tausayin shi duk yakama jama,a suna ta kwantar mashi da hankali Akan ya,Yi haquri isha Allahu za,a dace.
Suma jame,in yan sanda ya haquri suka bashi suka,Ce ya kwnatar da hankalin shi zasuyi iya bakin qoqarin’su wajan gani Anga yarinya sun shaida mashi cewa zasu tsane’ta bincike. Bayan sun tafi ya shiga gida magana ta gaskiya yanzu ya Yi dana’sani Abinda ya Aikata dan haka yanzu zuciyar shi Na raya mashi ya Yi wanka yakoma bakin teku yaga ko yasamu wani Labari Akan Narim
Yaji ko Ansamu wadanda suka ganta qila Ruwa basu tai da ita ba.
Dawanna’n tunani ya shiga wanna
Alhaji Bello haifafen garin Lagos ne dan kasuwane sosai yana kasuwanici sifiri yanada manyan kanfanoni.
Na. Shaddodi da turame
Mutumin kirki ne sosai yanada kirki yanada halin kware
Kowa na yabani shi musamman Ma,aikatan shi bai tauye masu hakkinsu yanabiyansu Hakkinsu in lokaci ya Yi
Yanada halin kware dan duk Wanda zaka tambaya Alhji Bello zaice maka mutum kirki ne ba boyeyye ne A lagos dan haraka kasuwancin shi yasa ya Yi suna Afadin garin Lagos
Matar shi hajiya Asama,u itama Yar Lagos. Ce mahaifanta nanan cikin Lagos Auran sauryi da budurwa sukayi
Makwabta ne su ita da Bello da gidan iyayanta da nashi banisa unguwarsu daya mahaifiyarta kawar mahaifiyarshi Ce so su suka kulla wannan Aure da yake suna,San junan su Said Aure ya kullu .
Asama,u Maccece mai kirki ga Addini tanada halin kware ga San Mutane kowa NATA ne bata, da qyamar tallaka duk da kirkin Alhji BELLO yana da wuyar Sha,ani inba shi ya,Yi niyar Abuba to bawanda ya isa ya sashi Abinda bai Yi niya ba.
Ba shida Aibun komai inba wannan halin na shi ba na bawanda zai sashi yin Abinda bai Yi niyaba .
Shiya ba Wanda ya yi zarginshi Akan batan Narim