HAUSA NOVEL

GAMO DA KATAR Complete Hausa Novel

*M j pravet hospital baban hospital ne na manyan masu kud’i duk wani wanda yake ji da kanshi a gatin legos to wannan hospital d’in yake zuwa*
domin hospital ne in ka shige shi kamar a turai

ga ma ai kata kwarari na gida da na waje maza da mata

leabour room d’akin yan haihuwa

macce biyu ce a ciki kowacce da gadonta suna fesin din juna ba tazara so sai tsakani wannan gado d wannan na quda suke ba qaqqautawa kai dagani kasan suna shan wuya duk da ga likito cinan suna bakin qoqarin su to Aman da man ita haihuwa ta Allah ce

sai Adu.a suke Allah ya sauke su lafiya yayin da ita dayar na Adu.ane da hausa dayar kuma da larabci sai zufa su duk da sanyi A C da na fanka ga kuma sanyi gari saboda ba a dade da gama ruwan sma ba hakan bai hanasu zufa ba saboda ciwo da zafi dake da na quda

ciwon haihuwa ba qaramin ciwo bane dolle inka ga mai na quda k tausaya mata ;

cikin hukuncin Allah dayar ta sauka lafiya ta haifi yarta macce kyakyawa da yar kuma jikinta dug yamace

ya yi sanyi ta wahala aman hai huwar bata zoba ta juya kanta da qyala ta dubi wadda ta haihu saboda taji kukan jarir da qyala ta buda bakinta a hankali tana murmushin qarfin hali cikin hausarta da bata goge bace mashannu Alla shirya tace mata Ameen kema sannu Allah shi saukeki lafiya ta motsa labbanta Alamar Ammen hawayen nabin fuskar ta nursing sun gyara bby suka miqa mta ita bayan itamata sun gyara ta zasu kaita dakin hutu kafin ta tafi sao ta matso kuda da wannan ruqe da bbyn ta tai mata adu.a ta to famata itama cikin qarfin hali ta amshi bbyn tai mata adu.a sun dan jima ahaka sannan ta tafi dan hutawa bata jima da ta fiya ba na quda ta taso mata gadan gadan antaru kanta zuwa can Allah ya bata sa a ta haihu itama macce maishegen kyau ga gashi wanda ya rife mata fuska dan ko ganin fuskarta ba a yi sai da nursing din tasa hannuta ta maida gashin bayanta gashin kwance da tsawan shi kamar kayi parking dinshi

bbyn ba fara bace dan bata kai hasken babyn da aka haifaba gata da dan karan kyau na wuce misali sai daukar ta suke wannan ya dauka wannan ya dauka sunatai mata photonuna

Acewarsu ba,a ta6a haihuwar kyakyawa irin taba mai kayu da gashi

sun miqata ga mahaifiyar ta wadda tunda ta haihu take kuka ta amsheta ta jima tana kallon ta tare da yimata Adu.a sannan tai murmishi tace da likitan da ke gabanta da ta kira mata wadda ta haihi likitan tace to ta fita

 

more comments more typing

 

takuce mai son farin cikinku da nushadinku

 

 

*GOLDEN GIRL*

*GAMO DA KATAR*
(yar makahi)

*Na*

 

Yar mutan jibiy
*(Ammyn khairat)*

 

(¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)

 

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя’s αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/

TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09

*page 9⃣*

 

*Labari mai ta6a zuciya*

“*BISMILLAHI-RAHMANI-RAHIM*

 

Bayan likitar tafita kira mata wadda suka haihu tare sai ta juya tana kallon yar da ta haifa mai shegen kyau tana kuma kuka tare da yimata Adu,a Cikin kuka take cewa yata Allah shi maki Albarka ya kuma yara manke Abisa sunnan Annabin mu Allag shikare manke daga sharrin masu sharri Allah ya baki ilimi mai Albarka kiyi haquri da qaddaraki ki rungumeta hannu biyu kiyi imani da ita kijajirce kijure da hanlin da zaki tsinci kanki dan na son banmaki Adalci ba hadai tai ta sabbatu ita kade ”

Tare da likitar suka shigo hannu ta guda sa6e da yarta an gyarata ansa mata kayan sanyi sai wani kyakyawan yaro kamar dan turawa shekarun shi basu wuce 8 ya sha t shat din shi mai dogon hannu da wanda jus blue rigar kuma reat da a gogon hannun shi na yara kyakyawane sosai yaro

Masha Allahu tace yar uwa kin sauka ke ma ta Aje yar tata kan daya daga cikin gadajen dake wajan ta zo ta amshi bby cikin farin ciki tace sannu da qoqari ina can ina maki Adu,a tace na gode tace kikoga bby nan mai kyau da ita sai tai murmushi tace na gode shikuma yaron da ta shigo shi cewa yake momy bani ita na gani da ita da taki wacce tafi kyau duqowa tayi tanuna mashi tace boy ya ka ganta yace wwo momy so beutifull momy cute girl

Ina sota sosai ya matsa kusada mahaifiyar ta dake kwance kan gado tana kallon su tana dariyar qarfin hali yace momy zaki bani cute ta shafa kan shi tace na baka ita dana kana dai son ta ko yace eh so sai tace to na baka ita kariqeta amana yace insha Allahu yaron ya bigeta so sai kuma ya kwanta mata a rai sai ya juya ya ce momy kinga ta bani ita nasamu mata inason ta so sai bani itanan tace boy ka cika shime to gata riqe kware hannu biyu yasa ya Amsheta ya rungume harda lumshe ido tare da ajiyar zuciya jiyai yafi sonta abisa qanwar shi da momy dinshi ta haifa momy ta matsa bakin gadon tace yar uwa kin aika kirana da fatan lafiya cikin cije lipe dinta tace lafiya lau tare da ruqo hannuta sai boy ya matso kusa da su yace momy itama matata zan iya yi mata suna kamar yanda naima qanwata momy tace kajika da rigima bara momyn ta tai mata suna sai tace qyaleshi da yi mata suna mikake so kasa mata momy tace yar uwa kar ke biye shirman *Nuraim* tace bakomai qyalaishi sa mata suna kaji dana yace to cinda ni sunana *Nuraim* qanwata kuma Nasa mata *Narima*

To mata ta” kuma zan sa mata *Narim* ko matata ita kuma bbyn ta buda ido ta kalle shi tare da wasa da yan hanuwanta tana cilla qafaunta yace yauwa matata kunga ta kalleni ko sunan baiyiba momy tace eh baiyi ba Na Na din tayi yawa sai tace qyaleshi ni sunan yai man dadi *Narim* suna ya yi sai A runqa kiranta da Fatima *Narim* yace momy sunan wanene fatima tace sunan kakar tane yace to shikenan Allah shiraya fatima *Narim*
Ya koma can inda aka aje qanwarshi yana tai masu wasa

Ta dubi momy tace yaronki ya man akwai wayo momy tace indai Nuraim ne ai inkina tare da shi sai kingaji da surutun sa ta juya ta kalleshi sai wasa yake ma fatima Narim farin ciki ya kamata da kuma tausayin yarta

Tace momy Abinda yasa na kiraki wata Alfarma nake naima duk da nason zaki so jin koni wacece to sai dai lokaci ya qure da zan baki labarina ni dai ba yar nan qasar bace kuma yata da ubanta sanan tunda na ganki naji kinkwanta man dan Allah ta kamo hanunta idanuta cike da hawaye tace yata fatima Narim na biki ita aman kiriqe tamkae kekika haifeta tajuya ta kalli yata hawaye nabin fuskarta tace wanna kwanciyar da kikaga nayi to bata tashi bace inso dan Allah ki riqe yata Amana Allah ya tayaki riqo ta kwance wani quli dake ga zananta sarqace ta gwal sai saiqi tace mai harafin f suma yan kunnan haka suke da wannan harafi sai dan haunu dukansu na yara ta zubasu kan hannu momy tace kisa mata su sannan in tayi tsawan rai gawa jikacan kibata tanuna ma momy jikar dake kusa da gadon ta tace kibata komai na dangance da tarihinta yana ci karkibata sai shekaeunta sunkai ta mallaki hankalinta dan Allah ke man wannan Alfama ina son ki hankina ya kwanta dake na son kuma zaki ruqe Amana da na baki sai yanzu momy tanisa dan tunda tafara mafana bace komai ba tace haba yar uwa ai cuta ba mutuwa bace ki daina irin haka insha Allahu zaki tashi tace kaiya baki son yanda nake jibane kedai inafatan ki ruqe aman da na baki sai tari ya sarqeta tari take ba qaqqautawa momy ta buda biki tace likita shuru da yake ba kowa sai su sai kuma Nuraim da hankalinshi kega matarshi kamar yanda yake cewa kafin momy ta ankar sai aman jini matar take momy hankalinta ya tashi sosai tace sannu insha Allahu bazaki mutuba zaki tashi harkiga auran Fatimarki ki daurw kinji bari naje nakira likita cinkin qarfin hali tace aha ha kokin kirasu ba Abinda zasu iyayi dan batashi zanyi ba idanuta suka juye baka gani bakin sai farin tajuya tana kallon yarta daketa cilla qafafu sama kan gado Nuraim na tai mata wasa tana so tayi magana aman ina bikinta ya mata nauyi harahe ya kare sai cire cirw take gado na jijigawa momy duk ta rude tana son zuwa jiran likita Aman ta ruqe hannuta gam yanda bata iya kwace wa ba abinda momy ke fadi sai kalmar sha hada inda itama Allah yabata ikon fadin Abinda momy kecewa momy na fada tana bi duk da maganar ba tafita so sai aman tana fada momy naji sai da sukayi sau ukku sannan momy taji shuru shurun ta keda wuya bbyn ta ta kwala kuka Nuraim na mata wasa Aman sai kuka take hankalin momy gaba daya tashe yake itama tata bbyn dake barci ta tashi kukan take momy tarasa yanda zatayi kawai itama ta fashe da kuka wanda ya jawo hankalin Nuraim wajant a sabkowa yayi daga kan gadon yazo wajanta yace momy bakijin ya yanki na kuka lafiya naga kema kina kuka miyafaru momy takasa cewa komai sai nuna mashi ita take ya kai duban shi inda ta nuna hannuta ya gatanan kwance idanunta sunyi sama farifet dasu ya matsa kusa da ita ya ruqo hannuta yace momy momy shuru ya matsa hannuta yaji jijiya bata motsi ya kara kunnan shi saitin zuciyarta yaji bata halbawa sai ya kai hannun shi kan fukarta ya shafa idanunta ya rufe matasu tare da tofa mata Addu,a yaja zane ya rufe ta idanunshi cike da kwalla yace momy bari kuka yi mata Adu,a bake kace man in mamaci ya mutu ba ai mashi kuka ba momy ta gyada kai yace to miyasa ke kike kuka Adu,a zamiyi mata duk da ba musan taba yaune Allah ya hadau muda ita naji inajinta cikin raina inajin mutuwarta so sai momy koke kika mutu iya Abinda zanji kenan baban qarin da muwata momy shine matana cewa da Fatima Narim momy ya zamu da ita gasu can suna kuka ki daure ki tashi kika masu momy ta goge hawayanta tace Allah shi maka Albarka boy yaro ne kai qarim aman a kwai kaifin basira likita ce ta shigo tace kai lafiya yara keta kuka kun qyale su momu tace dolle ce tasa haka bamu cinki kwanciyar hankali ta nuna mata gawar matarda bata masan sunan taba sai yar uwa da take cemata

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button