Halimatus sadeeya

Kai ta sunkuyar tace ba komai umma Babu abinda yake da muna
Umma tace Allah yasa haka sadiya na sankifa karki manta Ni nahaifeki kome yake da munki ko Baki fadaba Zan iya sani nasanki da hakuri da Mika lamuranki ga Allah kicigaba Allah na tsare da ke komai me shigewane ko zuwan da kannanki su zilai sukayi jiya maganar da suka dinga yadawa da zuwa yimusu sannu da zuwa da kikayi kikace abaki yaransu da suka Haifa ki dauka aka hanaki shine yatsaye Miki arai yake da munki ki mance da su kema kamar yaune zakiga kinyi aure kinzo Mana da naki baby su kalifa na tafada wajan dauka insha Allahu ranar zatazo kinji
Kunyace takamata tarufe fuska tana dariya tatashi da sauri tafice daga dakin zuwa bandaki se murmashi take
Umma tace sadiya sarkin kunya Allah yanuna Mana wannan ranar har gobe ban finda ran Bazaki aureba sadiya inaji ajikina mijinki yakusa zuwa kwanannan insha Allahu
Sallama ake ta rangadawa tindaga tsakar gida matan gidan su habi naji bawance ta amsa ummace tafito daga dakin tana amsa sallamar
tace Yaya kece yau agidan namu sannu da zuwa karaso ciki
Sadiya fitowarta kenan daga bayi tana ganin bakuwar tasu tahau murna tace lah babarmu sannu da zuwa
Taamsa tarike hannu sadiya suka karasa dakin umma bayan sun zauna suka gaisa
yaya tace sadiya yajiki
Tace da sauki babarmu
Yaya tace tafiya nayi ta musamman sadiya saboda ke yau tafiyar takice har malam se najira yazo munyi mgnar da shi Dan yardarsa
mukafi so in yayarda komai zezo da sauki kin kusa hutawa da bakin cikin matan gidannan ba se sun ganki bama zasuyi Miki
Umma tace hm ai ita da hutawa da kananun Maganganu se Allah yakawo Mata miji tayi aure Dan ma malam yakwatar Mata yanci wannan Karan yadau mataki abin ya Dan ragu sosai
Yaya tace Allah yakyauta wata mgnce take tafe da Ni Akan sadiya Ni da aminu muka yanke shawara nasan kema Zaki yarda kinsan aminu na aiki gidan wani me kudi Yana tare da megidan ba inda basa zuwa tare da alhaji Kuma du wani aike in har na kudi me yawane ko wanda yadace yaran gidanne zasu suyo to du aminu ake aikawa yaje aminu yazama kamar Dan gidan Dan yanda suka rikemin aminu da Amana ba kowana gidan masu kudi bane zasuyi hakaba to yanda sukaji dadin aiki da aminu shine suka cewa aminu yasamo musu me kula da yaran Dan megidan yaran suna da wayo sunama zuwa makaranta abinda zatana musu wanka dafa musu abinci shiryasu kula dasu dai tayanda yadace kusan dai zata koma kamar uwarsu Kuma gidan iyayan yaran zata koma da Zama acan zatana kwana sedai tazo gaisheku lokaci zuwa lokaci wata irin uwa Allah yabawa yaran nasan ko kune kukaji yanda rayuwar yaran take tafiya zaku tausaya musu wlh
Nan tabasu labarin irin rayuwar Malika da yanda take yiwa yaran lokaci guda sadiya sarkin tausayi tafara kuka umma ma jikinta yamutu sun Bata tausayi sosai yaran
tinda aminu yabani labari jikina yamutu naji tausayin yaran yakamani naga Babu Wanda yadace taje ta temaka musu irin sadiya nasan zata kula da su kamar kannanta ko yaran da ta Haifa har zuwa lokacin da Allah ze Bata miji se tabar aiki agidan Tai auranta Ni shawara nazo nabaki Khadija ki yarda sadiya taje ta Fara aikinnan Bakisan me Allah yake nufi da hakaba Kuma Ni nayi hakane Dan sadiya tasamu saukin irin bakin cikin da take kunsa acikin gidannan Kinga yanzu base sun gantaba zasuyi Mata se suci kansu har Yan unguwama da suka saka Mata Ido du tahuta da gulmarta da nunatan da akeyi Kuma nice Zan kaita gurin hajiyar da kaina Zan Bata amanar sadiya kuma Zan nemi alfarmar itama abarta ko isilamiyace asata a unguwar taci gaba da zuwa tarage kadaici Dan Allah Khadija in na Isa dake kiyarda da mgnata in malam yazo muhadu mushawo kansa bani da matsala tawajan sadiya tinda nabaku labarin irin kadaicin da yaran suke ciki da kunci sadiya na da tausayi zata yarda bazata kiba amsarki nake jira Khadija Kuma wlh kinsan sadiya na da kamun Kai Babu abinda ze faru se alheri insha Allahu
Umma tace to Yaya du abinda kikaga yadace da sadiya wlh Ni bazance Miki aah ba ai yarkice kunfi kusa nasan Bazaki zaba Mata aikin da ze cutar da itaba Ni adduace tawa Allah yasa haka shi yafi alheri Allah yasa karshan bakin cikin sadiya yazo malam yakusa dawowa se ki Masa mgnar in yaki Zan tayaki sa Baki har yayarda Allah yasanya Albarka alamarin
Yaya tace Ameeen to sadiya saura ke Dan se da yardarki zamuyiwa mahaifinki mgn kin yarda zakiyi aikin Kuma Zaki koma can gidan da Zama in Kinga da takura zamu shiga hakkinki abar mgnar asamo musu wata kinji
Sadiya tace aah Babu wata takura in umma da da babanmu sun yarda se nayi ba komai Zan iya yaran sun bani tausayi daga Jin labarinsu naji inah kaunar yaran baa temako Nima wani bawan Allah yatemake,Ni ku samin Albarka ku tayimin addua Allah yabani saa
Sallamar malam sukaji daga tsakar gida
Umma tace yauwa gashinan ma yadawo
Masu yimin comments Ina sane da ku ban manta da kuba
bana turawa ta pc du meso daga farko ta tambaya agrp zatasamu
New writer’s
Hakan Take
*Husba’ahfama* ????????????
*’Yar kwalliya* ????????????
????????????????????????
????????????????????
????????????????
????????????????
????????????
????????????????????????
????????????????????
????????????????
????????????
????????????????
????????????
????????????
???????? *HALEEMATUS SADEEYA*????????
Written by *HUSBA’AHFAMA*
IG *officiall_husba’ahfama*
Facebook *Real Husba’ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba’ahfama*
*Bismillahir Rahamanir Rahim*
13-14
Malam karasa shiga dakin umma yayi saboda yau kwanannan,tane da sallama yaga yayace tazo yace yau manyan Baki muke da su agidan namu Khadija yabaki aika ankirani ba nazo mungaisa yanzu da ban shigoba shikenan bazamu haduba
Yaya tace ai yau ko baka shigoba dakainama Zan tura akiraka Dan tafiyar takace ko nace takuce ku uku Allah yasa ka fahimceni in nama bayani
Malam gaisawa yayi da Yaya sadiya da umma sukai Masa sannu da zuwa Zama yayi
Yace to Yaya Allah yasa dai lfy kince tafiyar tamuce tinda nashigo aimin bayani
Yaya taiwa malam bayanin abinda yake tafe da ita tace tawa sadiya da umma bayani Kan yashigo taba shi lanarin yaran da sadiya zatana kula da su ta fadamasa sunan unguwar da zataje Tai aikin takuma ce bawata matsala yatemake yabari ko Dan irin zaman bacin ran da sadiya take agidansu da Yan unguwa tasamu sauki sosai ko Dan yanayin jikinta tarage damuwa in taga tayi nesa da gida da du wani Wanda ze Bata Mata Rai Kuma yaran bawasu yaran da zatana goyawa bane ko Tasha wahalar rainansu komai zezo da sauki umma ma zata,samu sauki tawani wajan Dan indai anbatawa sadiya Rai in Taji Dole nata ran itama ze baci tace tawajannan daga umma har sadiya sun samun sauki
Dakyar akashawo Kan malam yayarda Dan shi cewa yayi bayaso sadiya takuma samun wata matsalar ga wannan ko dadewa batayi da dawowaba daga asibitiba Kuma shi talaucinshi bekai yatura yaran sa aikatauba gidan masu kudi se da umma tasa Baki yayarda yakuma tambayi sadiya tanaso zata iya tace Masa eh zata iya sannan yayarda yasawa abin Albarka
Yace to Yaya yanzu yaushe zata Fara zuwa kifa tambatar Kinga kalar gidan da zaakaita in Kinga da matsala zaabata tarbiyar sadiya Dan Allah karki barima tafara aikin kidawo Mana da ita