Halimatus sadeeya

Yaya tace to malam insha Allahu Babu matsala se alheri in Zan Bari abatawa yaran da na haifa tarbiya to Zan Bari abata na sadiya ai da ban yarda da mutananba da bazan zo nace sadiya tafara aiki agidanba jibi zanzo na tafi da ita yanzu in nabar Nan wajan hajiya zamu da aminu muyi
Mata bayani ansamu Wanda zata kula da yaran na Kuma Bata amanar sadiya da kaina se
Nazo nadau sadiya jibi kafin Nazo tahada kayanta da du wani abinda zata nema Ina zuwa se tafiya
Umma da malam sukace to Allah yakaimu
malam yafito ze koma wajan sanaarsa yaga su lami an nutsu abakin tagar umma ana kasa kunne so suke suji me malam da Yaya da umma suke mgn akai malam yace aifa haka kuka iya anan kukafi kauri wajan labe adau gulma akai gaba Kuma du abinku ba abinda zakuji yanzu nasan ko gaisawa da bakuwar Tata bakuyiba Amma kunzo Kuna Mata labe Dan munafurci ita Kuma Khadija Mara zuciya naku bakin nazuwa zatazo ta gaishesu wasuma Dakar zasu amsa Mata wasuma ba amsa Mata sukeba Amma baiwar Allah Bata taba gajiyaba se tazo ta gaisa da su ammaku bakusan kuyi Mata karaba ku gaisa da nata bakin in da mutunci ai yayartace tazo uwa Daya uba Daya kamar Yar uwarku take in da mutunci zakuje ku gaisheta ko se naci mutuncinku ko Yaya wlh inanan har se kunje kun gaisheta Kan nafita naji wata Tama gaisuwar wulakancin kuga ikwan Allah gobema kukara labewa intai Baki bakunce Khadija asiri tai minba ta shanyeni yanzu kuka fara ganin aikin asirin Khadija wlh in Baku canza haliba canjima awajena yanzu kuka fara gani Ni da zata kaini wajan malamin da yai mata asirin ta shanyeni da na karamai kudi yayi fin Wanda tabiya kudi yai mata Ni sonake nazama mijin tace awajan Khadija Kuma kukoma irin halayanta kuga in ban Zama mijin taceba awajanku wlh kusani yanzu ba malam din da bane wannan malam din me zafine du Wanda tayi ba dedaiba itama zataji badedaiba awajena kushige kuje ku gaisa Zan fita inah jiranku
Bashiri suka tafi gai da Yaya suna kunkuni suka shiga badan sun soba suka gaisa Yaya cikin sakin fuska ta amsa musu Suka fito Rai abace su yanzu malam tsoroma yake Basu gashi yahanasu fito ko inah yasa masu zuba Masa Ido akansu du Wanda tafito zata unguwa Yan zaman banzan unguwarsu malam Yana dawowa zasu Gaya Masa abin yadamesu gashi sunaso suje awajan malamansu bahali malam yakasa yatsare
se da malam yaga du sun gaisa da Yaya sannan yatafi wajan sanaarsa
Yaya tana barin gidan takira sminu tafada Masa yanda sukayi da su umma yaji Dadi sosai Yaya tace gatanan zuwa gidan su ummi suhadu da aminu acan suwa ummi bayani Yaya na karasowa tasamu aminu na jiranta suka karasa cikin gidan afalo suka samu ummi da murna ummi tatari Yaya tasa aka cika Mata gabanta da Kayan marmari sannan suka gaisa Yaya taiwa ummi bayani
Tace to hajiya ga amanar yatanan nabaki yarinyar na da hankali da nutsuwa ga tarbiya Kuma tayi sauka har sau biyu yanzu tana ajin hadda yarinyar tasamu matsala kwanannan Bata da lfy baaso tasa damuwa aranta
Nan yaya Tai Mata bayanin rashin lfyar sadiya da matsalar da take da munta Kuma tafada Mata yanda suke da mahaifiyar sadiya
Ummi har da hawaye tace Allah sarki bansan me yake damun mutanan muba in yarinya Batyi aure da wuriba se kiga ta zama abar kyama acikin mutane kowa na gudunta watama har da iyayanta da Yan uwanta da Yan unguwa se kiga kawaye du sun gujeta in Banda bakar mgn da Gori Babu abinda ake gayawa yarinya kamar ita tabawa kanta jinkirin Kuma Basu San komai na Allah bane komai na da lokaci Kuma irin wayannan yaran in sun tashi aure se auransu yabawa kowa mamaki Kuma se ya doke kaf na danginta Allah yabata miji nagari Allah sarki kowa da tasa matsalar aliyu inajin tausayinshi Sega wata ita,kuma Tata matsalar da ban nayarda zata kula da su Amira sosai Dan zuciyata ta yarda da ita tinkan na ganta in naga malika zata shiga hakkinta wlh zanyi gaggawar taka Mata burki tinkan naganta naji Ina kaunarta naji inajin tausayinta sadiya kikace sunanta ko Allah yakaimu jibin nawa zaana biyanta kunyanke ke da iyayan yarinyar
Yaya tace ai ba Yar haka tsakaninmu hajiya kifada konawa zana Bata
Ummi tace to ko nawa muka yanke da uban yaran Zan kiraki awaya nafada Miki ko na gayawa aminu ngd sosai naji Dadi da samomin yarinyarnan da kikayi
Sallama Yaya tayi da ummi tatafi gida cikin farinciki sadiya zata huta da bacin ran su tala
Ummi Kiran aliyu tayi awaya in yagama abinda yakeyi yazo tana san ganinshi yace zezo da dandare
Dare nayi aliyu yazo umma da abbah sukai Masa bayani ansamu me kula da su walid
Yace to anan zata zauna ko tare da ku da yaran
Abbah yace yamukayi da Kai banace nagama mgn ba Yara zasu komai gidanka su zauna tare da mahaifiyarsu aliyu komai yai zafi maganinshi Allah Kuma Yana tare da Kai kayi hakuri akwai ranar da zakayi farinciki arayuwarka zaka manta komai in ranar tazo zaka gane Mata ba duka suka taru suka Zama dayaba hakurin,Nan da kowa yake cewa kayi to kacigaba dayi akwai ranar cin riba wannan yarinyar me kula da su amira insha Allahu karshan wahalar su Amira yazo zata kula da su sosai muna da namu dalilin na cewa yaran se sun koma gun mahaifiyarsu ko Bazata daga Ido ta kallesuba Kai dai kaci gaba da Jan yaranka ajiki kakara Akan Wanda kakeyi Dan su shaku da Kai sosai Kuma munaso kasawa wannan yarinyar Ido sosai Akan su Amira zakaga abinda mukace akanta gaskiyane anyi dacan me kula da su Kuma wannan tafiye tafiyan ka,ragesu saboda yaranka Dan kana ganin wace kalar tarbiya take Basu in kayarda da ita gaba daya se kacigaba da tafiye tafiyanka kuma ko kayi tafiya kadinga zuwan bazata saboda kana ganin wana Hali gidanka yake ciki daga Yan aikinka zuwa ita kanta matarka kaji ko
Yace to abbah insha Allahu du naji abinda kace Kuma zanbi Zan muku biyaiya akoyaushe Allah yakara girma Ni Zan koma gida da aikin da nake nafito zanje na karasa Allah yakaimu jibin
Aliyu na komawa gida yasamu malika afalo se kaiwa take tana dawowa tana kallan agogo Kai yadauke kamar besan da mutunba yashige ze tafi shashinsa gabanshi taje Tasha da gudu
Tace Kama rainamin hankali kaifa nake jira tin dazu daga inah kake yanzu kaga karfe nawa kuwa shadaya saurafa azamanka na megida se shadayan dare zaka dawo gida Ni bawannan bama inah yarana nayi kawaici nazuba Ido naji shuru naduba har yau Banga sun dawoba hakurina yakare Wai me Kai da danginka kuke nufi da ni wlh in Baku dawomin da yaranaba Zan kaiku Kara kotu takarbar,min yarana Dan haka,ni bana sakarwa danginka fuska Dan bakaunata sukeba Ni Kai kafi bani mamaki kasa nabar ciki ajikina kana ta wulakan,tani kalli yanda cikin yake dada turowa se Muni yake karamin daman abinda nake gudu kenan Kar nafiya haihuwa kana wulakan,tani Ashe yaran da kake cewa kanaso na karyane tinda gashi nasamu kana wulakan,tani baka kula Dani Ina ganin yanda maza ke kula da matansu in suna da ciki Amma Banda Kai solobiyo namijin kawai
Wani kallo aliyu yawatsa Mata yace mahaukaciya shashasha kawai ke Wai Dan Baki da kunya kece me tareni da wannan Maganganun wlh kifita a idona nakai bango ke Dan Baki da kunya kece me tsareni ki tambayeni daga inah nake yanzu ke waya tsareki yake Miki tambaya in kin dawo daga yawan shashancinki yanzu har Karin girma Kika samu har kwana kike awaje namiki mgn ke har Yara gareki ai Baki da Yara Baki haifaba bakuma Zaki haifaba yarana zakice ko kice yaran mamansu da zatazo jibi ta zauna agidannan yaran da Baki da lokacinsu yaran da ko haduwa dake basaso su tsoranki suke basaso su ganki yaran da har takai da bakinsu suke cewa ke ba mahaifiyarsu bace Basu da uwa Dan Allah ke bakya,jin komai azuciyaki Kan irin abinda kikewa yaranki da mijinki yanzu ki fadamin yaushe raban da kibani hakkina yaushe raban da mu hada Koda wajan kwanane da ke naji dumin jikinki kiji nawa yaushe raban da mu,zauna muyi Hira irin ta ma aurata ko nace masoya yaushe raban da kisan Yaya rayuwar gidanki take tafiya da ta mijinki wlh yanzu nadena daukan wannan rainin da kike min wlh wlh da ba ciki jikinki se kinsha mamakina karki Kuma kara tarata da wata mgn ko wace irice muci gaba da Zama haka kowa yai harkar gabansa irin rayuwar da Kika zabar Mana Kennan Dan haka Babu ruwan wani daga ga cikinmu Kar Wanda yakara sawa wani Ido