Halimatus sadeeya

Malam yace shikenan ya Isa Zan Mata mgn batun sadiya Kuma me ta tsare muku Dan Allah yarinyar da ko mgn be dametaba Kuma batun tayi kwantai komai na Allahne Ni ba zan yiwa yarana auran doleba na fada na kuma fada Babu auran Dole atsarina Wanda yarinya ta kawo da kanta tace tanaso shi Zan aura Mata banwa yayanku auran doleba itama bazan Mata
Barinsu yayi anan suna ta mgangununshi narashin mutunci yashige dakin umma da sallama samunta yayi tana zaune da bahon awara danya gabanta tana yanyakawa zata cika ta da magi Kan sadiya ta dawo daga isilamiya karfe hudu sannu da zuwa Tai Masa yaamsa yazauna bakin gado yace Khadija meyahada ki da Yan uwanki haka ke da nake yabanki sallah Zaki kasa alwala Dan Allah karna karajin irin haka tafaru kiringa hakuri wataran see labari kinji
Tace to malam bazaa Kumaba yauma bango suka kaini namayar musu nagajine
Nan takwashe yanda akayi tamayar Masa ransa yamugun baci da yaji me suka Gaya mata Amma bayanda zeyi Dan Matan NASA sunfi karfinshi koya musu fada baji zasuyiba Kuma tsoransuma yake bakome sukai yake mgnba ko yaransu sunfi karfinshi Dan koyasa musu doka ko yai musu fada baji zasuyiba yayan ummune kadai suke Mai biyaiya tawajan umma da yaranta ne kadai yake Jin Dadi Amma Banda sauran matansa da yayansu du da wani lokaci tsoran.yi musu mgn yake koyabude Baki zeyi myn baya iyawa ba lefinshi bane an mallakeshine ta malamai danma Yana da karfin ibada ko sun banko Masa basosai asirin yake tasiri akan saba hakuri ya dada bawa umma yafice warsa masallaci ko taken sauran matansa bebiba
shararran Dan boko Kuma banban Dan kasuwa meji da kansa kuma da kudi alhaji aliyu me azurfa kenan zaune ababban falanshi Wanda yagaji da haduwa Dan kimanin shekara arbain da biyar aduniya fuskarshi tagaji da kyau da kwarjini kana ganin yananinsa kasan ransa abace yake hannu yasa yadafe kansa yarufe Ido yajingina da kujera wata bakar Mata nagani kakkaura gajera kannan dam da garin gashi farcannan yasha janfarce kamar ba Yar musulamaiba kana ganinta kasan Yar duniyace ta banko kofa tashigo Rai abace ko sallama Babu ta tsaya kansa tana jinjiga
tace wlh baby bazan yardaba innanan Kan bakata Sena zubar da cikinnan da wanne zanji haba haihuwa ta ukufa zanyi se kace wata karya sarkin Yaya Ni da Daya nai niyar Haifa aduni tin haihuwar walit nace ayankemin mahaifa kaki yarda kaimin dadin Baki har nazo nakuma haihuwar Amira Shima babu fadan da bamuyi da kaiba akan kasa ayankemin mahaifa kaki Kuma kayimin alkarin bazaka Kuma min wani cikinba Amma gashi yanzu saboda jarabarka kakuma bankamin wani cikin wlh wanna zubar da shi zanyi Kuma ko kaso ko kaki zansa ayankemin mahaifa nagaji da haihuwa haka kawai da aikin bankin da nake zuwa zanji ko da ciki du kawayena haihuwarsu daidai seni me gaban haihuwa du nafisu yawan yara da kuruciyata duniya na yayina naje na ratantake na kwararrabe na fatantake inaji Ina gani Kai kanasan Yara nikuma bama nasan Yara da haihuwa kwatakwata bana sansu na tsanesu kaga tafiyata asibiti Sena kawoma jinin danka aleda adaure
Jitayi yafuncukota yajuyo da ita cikin fishi ya wanketa da Mari kwarara har uku ko mgn be mataba yakama hannunta yai hanyar dakinta da ita bude dakinta yayi yajefata Kan tafkeken gadan da ke dakin yajuya yacire mukullin dakin yafita yakulleta tawaje yanaji tana ihu tana gaya masa bakaken maga Amma ko uffan bece mataba cikin sauri yai hanyar waje inda motocin gidan suke yaransa naganinsa suka biyoshi da gudu daya daga ciki yabude Masa kofar mota yashiga direba yaja yaransa suka shiga nasu motocin suka biyo bayan motarsa megadi yabude musu suka fice jingina yayi da kujerar motar yarufe Ido jiyayi direban
yace yallabai Ina zamu
Kamar baze bashi amsaba can Kuma yace gidan su Malika zamu tsaki yaja mekarfi yafesar da iskar bakinsa ahankali yace malika zancen zuci yafara shi kadai yace tun Ina Dubai yarinyar Nan ta dameni da Kira tana da ciki zata zubar in banzoba zubarwa zatai Dan nasan halinta tasaba zubarmin da ciki gani take du ban saniba Dan haka ban Gama abinda yakainiba Dole nabari nataho in bahakaba Shima zubar da shi zatayi daga isowata ko hutawa banyiba tarufeni da Bala,I Babu sannu da zuwan kirki bare tarba me Dadi har abani abincin da zanci azaune jiya na kwana ko nace muka kwana saboda masifarta ko auran kiyaiya mukayi da Malika see dai haka tin da mukai aure bani da kwanciyar hankali in dai haka aure yake wlh danani ban yishiba da na zauna haka tawajan bani hakkina Malika batasan wannanba tawajan kula da yaranta da gida du Bata da wannan lokacin see dai Yan aiki suyi in anyi mgn tace aikine yaimata yawa se kace Kanta akafara aiki Matan da suke da aure suke aiki Kuma suke kula da yaransu da megidansu Amma ita narasa me yake damunta gashi ta tsani haihuwa Ni Kuma Allah yadoramin San Yara Kullin burina da addua ta Naga gidana cika da Yara Amma inah ita bahakane burintaba natsani Mata du Mata kallan da nake musu kenan awaje zasu soka suyi maka biyaiya sunana maka farincikinka sukeso Amma in kashigo da su ba haka abin yakeba Mata Mata na tsaneku uwata kadai nakeso ko kannena Mata kallan haka nake musu du gani nake halinsu Daya da malika
Motarce takawo gidan da zasu zo Amma besan sun kawoba Yana zancan zuci
Direban yace yallabai munkawo
shuru be amsaba se da yada maimaita Masa sannan yabude idansa ahankali da sukai jajawur bude Masa kofar akayi yasa kafa yafito ahankali cikin izza yafara tafiya kana ganinsa kasan namijin duniyane yashiga cikin gidan masu gadi na tazubewa suna kwasar gaisuwa hannu yake daga musu kana ganin yananinsa kasan Yana cikin bacin Rai
shiga yai cikin falan gidan da sallama dauke abakinshi wani dantijone kishingide akan kafet yata da kai da irin tuntunnan da akesawa atsakiyar afalo amsawa tsohon yayi
Yace aliyu ka karaso zoka zauna kusa da Ni dana
Yace daddy barka da hutawa
Amsawa tsohun yayi cikin mutunci suka gaisa
Alhaji aliyu yace daddy Daman bawani Abu bane nace inasan ganinka Kan Malika ne tana da ciki har nawata hudu itama batasan tana da shiba se kwanannan saboda bebata wahalaba kamar sauran shine da tagano tana da ciki tatubure lanlai se ta zubur bazata haifeshiba Ina Dubai ban Gama abinda nakeba nataho sabada hankali na da ta tada jiya nadawo cikin dare Amma wlh ko bacci bamu samu munyiba har yanzu da nakema bayani saboda rigimar da take min seta zubar yanzu hakama kulleta nai adaki nafito Dan kartafita taje ta zubar bana gidan Dan Allah Kai Mata fada inasan cikina Kar ta zubarmin
Salati tsohun yakama yahau fada sosai yace lanlai bantaba sanin rashin mutuncin Malika da rashin hankali yakai hakaba ciki zata zubar abinda wasu suke nema Ido rufe Amma ita Allah yabata shine ta keso ta zubar dufa Rashi. Mutuncin da take shukawa agidanka nasani wlh zata hadu Dani tashi katafi gida yanzu zanzo da kaina karka budeta se na karaso
Yace to daddy ngd Allah yakara girma se ka karaso Amma Dan Allah daddy kabita ahankali
Yace kadai tafi aliyu se na karaso Allah yaimaka Albarka Allah yakarama hakurin Zama da Malika nasani wlh kana hakuri da ita
Fita alhaji aliyu yayi suka koma gida Yana fitowa daga mota Yan yaransa kanana suka taho yimasa sannu da zuwa namijin me suna walid Dan shekara biyar se macan Amira Yar shekara uku dagasu yayi Daya bayan Daya Yana musu wasa