Halimatus sadeeya

Bako yaushe zakuna jinaba se ranar da naji jikina da sauki yauma Allah ne yabaku natashi alhamdulillah jikina da sauki ngd da adduarku
Maman yaseer saura kice wani Abu na sanki da tsokana bakomai bane yake da muna tsufane????
New writer’s
Hakan take
*Husba’ahfama* ????????????
*Yar* *kwaliya* ???? ????????
????????????????????????
????????????????????
????????????????
????????????????
????????????
????????????????????????
????????????????????
????????????????
????????????
????????????????
????????????
????????????
???????? *HALEEMATUS* *SADEEYA* ????????
Written by *HUSBA’AHFAMA*
IG **officiall_husba’ahfama*
Facebook *Real* *husba’ahfama*
Follow me on Wattpad @ *Real* *husba’ahfama*
*Bismillahir* *Rahamanir* *Rahim*
19-20
Malam ne yashigo gida yaji mitar da su habi keyi Wai umma ta gaya,musu mgn ta zagesu
Yace metace muku Kuma me kuka Fara cemata Dan nasan Khadija bazata Fara tsokanarkuba hakakawai se dai kune kufara
Kame kame suka Fara
umma tafito tagaya Masa abinda yahadasu da mgnar da tamayar musu
Malam yace haka akayi ku bani amsa
Kasa mgn sukayi
Malam yace Daman hakane inbaki yasan mezefada besan abinda zaamayar masaba gobema kukara Gaya Mata mgn karku fasa kuji da kashin da yake jikinku kafin ku kalli nawasu sadiya Kuma se dai kuji alheri munafukan banza ku kunsan me naku ya’Yan sukeyi awaje in sunfita ko binsu kukeyi du inda zasu yaja tsaki yashige dakinsa
Yabarsu da kunan Rai azuciya da tsinewa umma
Umma kuwa dariya tahau musu tace wahalanlu tashige daki
Sadiya ita da su Walid shakuwace me tsanani tashiga tsakaninsu gashi sunajin mgnarta sosai ko tawajan tarbiyarsu tacanja sosai ko gaisuwa da basayi in sunga babba Amma yanzu suna ganin Wanda yagirmesu zasu gaisheshi kullin da safe se sunje sungai da aliyu sungai da sadiya intace suje su gaishe da malika se sufara kuka duyanda zatai da su bazasuba sedai suyi tamata kuka aliyu dakansa yace Mata karta Kara matsa musu kansuje su gai da mahaifiyarsu Dole tahakura ta barsu badan tasoba ita kokarinta ta gyara tsakanin malika da yaranta taga abin yafi karfinta Dole ta hakura tazuba Ido lokacin Sallah nayi zasuje suyi Wanda adah Basu damu dayin sallah ba Walid dakansa yake zuwa yacewa aliyu yazo suje masallaci tare abin har mamaki yakeba aliyu canjawar yaransa lokaci guda gakaratu da sukeyi sosai Wanda Ada Basu iyaba ga hadisai da Qur,ani da Sadiya take koya musu yashayin zuwan bazata bangaransu yaga ko dawata matsala Amma Babu wani Abu da be daceba da yake gani inyaje se daima yadawo da farinciki Dan hankalinshi yakuma kwanciya har CC,TV yasa abangaran su Amira du Sadiya Bata saniba Dan yaga abinda yake faruwa da yaransa sosai in yakunna yanda yaga tana kula da yaran tana musu wasa har goyasu takeyi in suna wasa bakaramin Dadi yakejiba in karatune shima in tana koya musu abin na burgeshi ko amakaranta akabasu Homework ita take Zama takoya musu hakan bakaramin Dadi yakewa aliyuba hamdalah yakeyi akullin Yana godewa Allah da su ummi da suka samo me hankali take kula da yaransa wani lokacinma in Yana kallan abinda sukeyi ta CC,TV yai tadawo da wajan baya Yana dada kallah Yana murmushi akace meda Wawa lokaci guda sadiya tashiga ran aliyu yake ganin girmanta da kimarta baya gajiya da kallanta ko wajan aikinshi yaje yai ta,tunaninta Kennan inkuwa yadawo beje yagansuba bayajin Dadi aransa ko siyaiya zewa su Amira da sadiya yake hadawa sukuma da sukaga haka Ko kayan wasa in yasiyo musu in besiyo da sadiya ba basa karba su Walid sun tafishi da shi kenan har seyaje yasiyo Mata sadiya tamusu fada su dena cewa asiyo Kayan was da ita in babansu yasiyo musu ita ta girma sunki suji sufa yanzu tsakaninsu da Allah gani suke sadiya mamansuce ita ta haifesu ba malika bace ta haifesu yanzu tsoran Malika suke sosai ko hanya basaso suhada da malika basama yarda ko haduwa suyi sunma manta da shafinta agidan daga aliyu se sadiya sune wayanda suka sani agidan Kuma suka damu dasu suka Zama farincikinsu
Nusaiba tabawa malika shawara se aliyu yayi tafiya zasu shirya fatin da zaayi agidanta inda zasuyi fatin agidan su wulakanta sadiya Babu me kwatarta yanda har ayi agama aliyu baze San anyiba se dai yadawo yaga sadiya Bata gidan sun koreta sunsa sabuwar mekula da su Amira Malika Kuma tayarda da shawarar hannun binbiyu Dan haka tanuna batama damu da harkar sadiya ba agidan tin da ga ranar da abinda yafaru tsakaninsu Basu Kuma haduwaba itama Kuma sadiya taka tsantsan take agidan Dan karta shiga harkarta ko tayi abinda ze Bata Mata Rai aliyu yayi mamaki da malika Bata dau mataki Kan sadiyaba yagane babanza malika tashare abinda yafaru tsakaninsu rannan yasan halin malika sarar yasan da abinda take shiryawa Kan sadiya dashi kansa Dan haka yazuba Ido ta ko Ina Yana jiran me zefaru ko tafiya yakiyi zuwa kasar waje saboda gudun abinda zeje yazo
yau aliyu yashirya zeyi tafiya zuwa Dubai shigo da Kaya se da yashamci malika sannan yashirya tafiyar Daman shima ba haduwa yake da itaba yanzu gudunshi take Babu me shiga harkar kowa yashirya kayansa yafito cikin Shiri wata bugangiyar Shanda me tsada yasa Tasha aikin surfani takalmin kafarsa da agogwan hannunsa ma abin kallone yayi kyau ba kadanba ga kamshi yana tashi ta ko Inah ajikinsa in yamotsa du macan da takalleshi se ta dada kallah
sadiya da su Amira na falo suna wasa se guje guje suke suna boyewa sadiya ita Kuma tana nemosu Amira ta kwace Dan kwalin Kan sadiya ta gudu ga gashin sadiya yasha gyara yazubo har baya tana kwallawa Amira Kira tazo tabata Dan kwalinta tabiyo Amira da gudu zuwa waje Bata,zataba taji tayi Karo da mutun tayi baya luhhhhh zata Fadi cikin sauri aliyu yajanyota tafada kirjinshi Ido tarufe tana jiran tajita akasa taji anrukota tafada kirjin mutun ga wani fitinannan kamshi da yacika Mata hanci Ido ta runtse daga ita harshi wata duniyar suka tafi na Yan muntuna inda da kamshin turaranshi da nata yahadu yabada wani kalar kamshi medadi wani yanayi dukansu suka shiga gawata kasala da tasaukar musu lokaci guda ga jikinsu jisuke kamar sun hadawa juna shokin sun Dan Dade ahaka muryar Amira ta dawo da su da Walid suna dariya tace yauwa daddy ngd da ka rikemin ita tsokanarta nayi nagudu Dan kwalinta na dauka se lokacin suka dawo haiyacinsu dasauri yasaki sadiya
yace inkina tayi Kina kallan gabanki
yawani hade Rai kamar be taba dariyaba kunyace takama sadiya kamar tanutse kasa Dan kunya alokacin aliyu yazubawa sadiya Ido Yana Kare Mata kallo ahankali yace tubarkallah yakau da Kai gefe ga idansa yayi jajawur iskar bakinsa yafesar wajan Zama yanema Kan kujera yajingina da jikin kujerar Dan gaba Daya wata kasalace tarufeshi se Mai da numfashi ahankali yakeyi Ido yarufe su Amira sukaje kusa dashi suka zauna suna Masa surutu bajinsu yakeba Dan shiyasan abinda yake damunshi
Cikin kunya sadiya tadau dankwalinta tadaura jiki amace tashige zatabar wajan du a abinda takeyi takasan Ido yake kallanta ahankali yace dawo kizauna mgn zamuyi da ku
Komawa tayi ta zauna akasa nesa da shi kadan ta sunkuyar dakai kasa tahau gaisheshi cikin rawar murya
Amsa Mata yayi ahankali yace ke da yaranki Kuna jin Dadi kema kin koma yarinya kamarsu ko se guje guje kuke Baku da matsala gashi har faduwa kin kusayi Nima kinkusa kaini kasa Dana Sha kasa