Halimatus sadeeya

Su tala se gani sukayi ana ta shigowa da Kaya ancika tsakar gida da su mutuwar tsaye sukayi Babu Wanda yakulasu har aka Gama kwaso Kayan
da Kar lami Baki na rawa tace Wai malam meyake faruwane ko kudi kayi lokaci daya bamu saniba ko acikin sirikanmu wani yayomaka wannan siyaiyar ainasan se dai sirikai tinda du masu kudine
Kala bece mataba yashigeta yashiga dakin umma
Habi tace mudai bamugane munafurcin me ake kullawa agidannanba da nuna bambanci adai dingayin komai tsakani da Allah du kanmu auranmu kake ko Dan wata taje yawan duniya tadawo har da Yara biyu aka dawo da su gida da akaboyesu tinda bamusan da suba dayake duniya tazo karshe anrufe mutun da ruwan kudi ko akansa be damuba sema Nan,Nan da ake da yaran da uwar yaran
Tala tace ki rufawa kanki asiri kinsan baataba yargwal da Yar mulki karki jawa kanki kina zaman zamanki muzuba mugani in tusa zata hura wuta
Malam da umma da ummi suna jinsu daga daki Babu Wanda yakulasu tantauna yanda tsarin biki ze tafi sukeyi godiya sosai su malam suke taiwa ummi har seda tace Dan Allah suyi shuru sunfi karfin haka
Ummi tadade gidan su sadiya sannan Tai musu sallama tatafi su Amira Basu damuba Dan tatafi tinda suna tare da sadiya
Malam fitowa yayi yatafi masallaci su habi na tamasa mgn yaki kulasu haka suka hakura suka kyaleshi abin yayi mugun batamusu Rai suka haukace se zage zage sukeyi idansu yarufe Dan jikinsu yabasu da abinda ake kullawa agidan baaso su sani Kuma koma meye umma yashafa ko sadiya
Umma taffto ita da sadiya suna duba Kayan
Ai su tala kamar su,rufesu da duka Dan bakinciki mgn suka Fara cikin daga murwa Dan su tinzira umma Ta kulasu Dan sunshirya in Tai mgn rufeta zasuyi da duka sukace munafinci in abin yine ayi mugani asiri ze tonu komai daran dadewa se asiri yatonu Ashe Daman andade ana yawan duniya anhaifi Yara anboye awani gidan du bamu saniba se yanzu aka fito da yaran duniya tagani kowa yagani aka dawo gida da abin arsiki Dan atoshewa tsohu da tsohuwa Baki sukasa mgn dayake tsoho da tsohuwa kwadayaiyune masu San abin duniya idansu yarufe sunga arziki ankawo musu sun,kasa biccike su dau mataki lokaci yayi da ake kwalliya da abin kunya
Umma da sadiya ko akansu Babu Wanda yatankasu sallamar Yan uwan umma sukaji Mata da matan yaiyun sadiya biyu Buda yayar umma tasaki Babar aminu sauran da suka shigo tare suka Kama Suma suka cika gidan da Buda kamar lokacin ake taro rawa Yaya tafara tana Waka
Tane cewa Komai lokacine kowana bawa da ranarsa da samunsa Allah kenan babu abinda be iyaba da wani farin jinin gara jinkirin alheri Allah mungode maka yarmu tayi goshi sadiya baiwar Allah damo sarkin hakuri Allah mungode maka lokaci yayi Amma ba na mutuwaba mu ai mundena fada mun Dena fishi muna cikin farinciki sadiya tazama darasi awajanmu da wajan jamaa Baki Daya kubani Aran hanci Yan uwana biki ake na farar kaza
Buda suka,hau saki sosai har mutanan unguwa naji yaran unguwa suka cika gidan suna kallan me akeyi wasuma iyayansune suka turosu Dan su gane musu abinda ke faruwa
Yaya ta Ciro Yan nera hamsin hamsin sababbi tahau rabawa yaran tana cemusu ku gayawa iyayanku biki yayi biki muna gaiyatarsu abin arzigi daga yanzu du suzo inji umma Babar sadiya akwai aiki zaa Fara yanzu du su shigo muyi tare
Dagudu Yara suka tafi suna murna suna zuwa suna fadawa iyayansu wasu yaranma ana Basu labari ana raba kudi gidan su sadiya dagudu suke shiga suma su karbi nasu
Yan uwan umma sun cika gidan se Buda ake ana ta aiki su tala Baki yamutu Babu bakin mgn se dai Ido Kuma anki Gaya musu kome akeyi gashi Babu damar suyi habaice habaican da suka Saba saboda Yan uwan umma da suka cika gidan sunayi Dangin umma zasu tarar musu Zama su iya rufesu da duka tinda sun fisu yawa Dole ko wacce taja jikinta takoma daki Dan habaicin da su Yaya suke sakar musuma ya ishesu bakin cikine fal zuciyar su tala Babu bakin magantuwa
Kafin kace me Yan unguwa matan aure sun cika gidan su sadiya Suma suna ta tambayar me akeyi haka agidan se acemusu lokacin fadawa mutane beyiba in lokaci yayi zaa sanar yanzu dai aki ake haka Yan uguwa sukasa hannu aka hau aiki da su gidafa yacika kamar lokacin aka Fara biki
Ummi na,barin gidan su sadiya asibiti tashige wajan aliyu ta,samu su abbah sunzo ita suke jira taji Dadi ganin aliyu jikin nashi da sauki abincima yake ci alokacin suna Hira da su abbah ummi na shiga da sallama suka gaisa tabasu labarin yanda sukayi da iyayan sadiya su daddy sunyi mamaki yanda iyayan sadiya Basu da kwadayi da wasu iyayanne idansu rufewa zeyi ganin an tila musu abin duniya Kuma murna zasuyi tayi yarinyarsu zata auri me arziki ammasu bahaka sukeba tsoran su abbah suke gani suke sayan sadiya zasuyi ahannunsu Kuma gani suke in sun yarda sun Basu auran sadiya wuya zasu Bata
Daddy yace alhamdulillah aliyu wannan lokacin kayi dace zaka samu kwanciyar hankali me dorewa arayuwarka
Shidai aliyu sun kulle Masa Kai yakasa gane me suke nufi
Abbah yace aliyu mgnar da mukace zamuyi da Kai zamu gayama yanzu shawara muka yanke Ni da sauran iyayanka azamanmu na iyayanka munyi maka Mata jibi zaa daura muku aure da ita arazane aliyu yadago Kai Yana kallan abbah Yar mutunci me tarbiya da sanin yakamata Yar manyan mutane masu tsoran Allah Sadiya me kula da yaranka ita muka yanke shawara zamu aura maka ita kaga se taci gaba da kula da yaranka Kuma kaga su Amira sun Saba da ita su gani sukeyima itace mahaifiyarsu kaima zakaji dadin Zama da ita kasan halin yarinyar Bata da matsala kaima kasha gwadata agidanka Amma baka taba kamata da lefiba ga amanar sadiya mun baka kariketa tsakani da Allah karka zalinci Yar mutane sadiya abar tausayice itama taga rayuwa kamar yanda kagani zamu baka labarinta Nan gaba in munga irin rikwan da kake mata ko baka Santa taci darajar yaranka da ta rike maka tsakani da Allah karka zalinci Yar mutane
Idan aliyu yakada yayi ja kana ganinshi kasan Yana cikin tashin hankali Dan shi ko amafarki be taba kawo wannan mgnarce ummi take rokwansa akai zasu gaya masa shi atsarinshi yacire babin aure har abada arayuwarshi yagama aure Dan gani yake aduniya bashi da raban yin aure yasamu kwanciyar hankali Dan haka yace ze karasa rayuwarsa haka yahakura da soyaiya bashi Babu wata mace da sunan so ko ya aureta
da kyar yabudi Baki yace abbah azamana na danku na yarda zanmuku biyaiya ko da banaso zan kuma zauna da ita tsakani da Allah bazan taba cutar da itaba nayi wannan alkawarin
Hamdalah su ummi suka hau yi suna godewa Allah Albarka suke ta shi Masa suna Masa adduar alheri
Tafiya gida sukayi kafin su tafi ummi se da Tai ta masa nasiha se da taga hankalinsa yakwanta sannan itama tabi su abbah suka tafi gida akabar aliyu da tinani kalkala azuciya
Kwanan aliyu Daya aka sallameshi ranar juma,a da yamma Yana komawa gida akahau shirye shiyan biki abbah wani babban abokin aliyu yadora akan har kar bikin aliyu me suna alhaji adamu shima Dan kasuwane meji da kansa yasashi yagaiyato abokansu nagida Dana kasar waje Suma sunyi mamaki gaiyatar biki ana saura kwana biyu ranar jumaa abokan aliyu na nesa suka Fara zuwa a Hotel suka sauka
Lefe nagani nafada ummi tasa aka hadawa sadiya musamman tasa akaje Dubai aka hado Mata tinkan su sanar da su zaa hadasu aure ummi tahada lefenta abbah yasan komai Dan shinema yaba da shawarar ahada lefen da wuri akwati ashirin da hudu akayiwa sadiya kayane anzubasu kamar baasan ciwan kudiba gwal kuwa inda Yana da Baki da yayi mgn akayan lefen sadiya me Abu da abinshi Daman sanaar aliyu kenan anzuba matasu da yawa fadarma irin yawan Kayan kudin da aka zubawa sadiya alefe Bata lokacine su ummi sunyi rawar gani kamar auran fari aliyu zeyi wanima inyaga hidimar da akeyi zece ummi Bata taba auran da dantaba se Akan aliyu daga abbah har ummi kowa hidima yake Akan bikin