Halimatus sadeeya

gakuma daddy shima da yadage kudi yake kashewa shine yadau nauyin yiwa sadiya Kayan daki komai na gidan aliyu se da yasa aka canjawa sadiya Dan daddy cewa yayi sadiya bazatayi anfani da Kayan da malika Tai anfani da suba Dan Kar sadiya takoyi bakin Hali kudin da yakashewa sadiya akayan daki ko yarshi malika be kashe Mata hakaba
Biki yayi biki abin baa mgn gidan su sadiya yakacame da Baki harta mustafa soja yayan sadiya yazo yaiyanta maza biyu da suke da aure Suma du sunzo Daman matansu sun rigasu yin gaba Yan uwan malam nakusa da na nesa du sunzo dangin umma na nesa da na kusa Suma du sunzo hidima umma take da Baki Babu hutu girke girke ake tayi kala kala anabawa Baki
sadiya amarya gyara takesha bana wasaba Dan hadin da Yar shuwa take Mata mezafine tinda komai akuranran lokaci aka Fara canji sosai sadiya takeji ajikinta ga wani kyau da tayi kamar ba sadiyaba kafin ta karaso waje kamshinta yayi sallama yarigata karasowa in kaganta kaga amarya
Amma Dan tsabar rashin hankali irin na su tala Basu gane auran sadiya zaayiba sunyi du wani biccike sun kasa gane komai Akan Taran da sukaga anayi abincin da suke na siyarwama gagara yayi suyishi saboda mutane babuma wajan da zasu sake su Dora nasu se hakura sukayi kansu yakulke sun rasa taranme akeyi dagasu har Yan unguwa sun kasa gane komai Kuma Yan unguwa Basu fasa shigowa ayi aiki da suba tinda suna samu komai Basu ake in andafa agidan zaman tsakar gida yagagari su habi Dole suka hakura su da Yan matansu suka koma zaman daki Dan Dole tala Dan bakin ciki har zazzabine yarufeta Dan bakin cikin takasa gane me akeyi abangaran umma Dan Daman ita tafi daukan tsanasu umma tafi su habi kishi da bakinciki
Ummi ranar jumaa da yamma tabawa Yan HALIMATUS SADIYA FANS GROUP nasu Kayan anko Tai tabasu hakuri telane be Dinka da wuriba kalar ankwansu daban da na Yan biki leshine me tsada da atanfa tayi musu masu kyau taba,su kowa yasamu Tasha godiya sosai
sannan tashige DAWEESU NOVEL GROUP Suma tabasu nasu Kayan anko din masu kyau da tsada Suma leshine da atanfa kalar nasu suma daban tasha godiya sosai
Rana Bata karya Allah yakawomu yau ake gobe se labari yau asabar yau ake daura auran sadiya Musa da alhaji aliyu idiris me azurfa Akan sadaki nera dubu dari biyar da sisin gwal inda dunbin mutane suka sheda augo aliyu yasha kyau baa mgn maroka kirari suke makada nakade Kade har da masu busa algaita unguwar su sadiya tacika da mutane motoci tindaga farkwan layi har bakin titi motocine manyan masu kudi da manyan Yan kasuwa sunzo
su tala sunfito tsegumi su da yaransu tsakar gida sunji Kade kadan da akeyi da hayaniyar mutane yayi yawa sosai Babu zato Babu tsammani sukaji maroki na cewa Allah yayarda Allah yakawomu bikin Yan gata bikin hajiya sadiya da alhaji aliyu idiris me azurfa aure yadauru Akan sadaki nera dubu dari biyar da sisin gwal bikine ake na Dan gata da Yar gata hajiya sadiya amarya albarkacinki alhaji aliyu me azurfa yabani kyautar kujerar hajji uban amarya uban augo alhaji idiris yabani kyautar gida Daya uban augo da amarya alhaji ahabubakar yabani kyautar katuwar mota Allah yasanya Albarka awanan sure bazan manta da Shiba shine silar arzikina jamaa kusheda aurefa yadauro ga kyauta anmin Babu kyarya aciki
Kamar hadin Baki daga tala habi lami asiya hauwa farida mutane se gani sukayi sun Fadi sun Suma salati Yan biki suka Fara sukayo kansu da gudu ana yaiyafa musu ruwa
Wata kanwar umma tace kutashi kutsahi wlh Baku isaba ayi Baku ai yanda kuka Fara ganin komai se Kun karasa gani kunji komai ai mu yanzu kuka Suma kukaki farfadowa Kun cucemu kubari inma zuciya zaku hadiya ku mutu kujira agama komai a idanku azamanku na iyayan amarya Yan farin gida ba Yan bakin gidaba kutashi ku tayamu murna Allah yayarda sadiya baiwar Allah tayi aure kwantai yau yayi anfani yazama kwantan alheri yau Allah yayarda andaura auran sadiya itama tashiga daga ciki tayi aure kamar yanda masu farin jinin yaranku sukayi kubude idanku da kunnanku kuji da kyau hidimar biki mukeyi na sadiya Yar Khadija da malam musu
Atare suka bude Ido suna tambayar me kunnansu yake jiye musu akace musu du abinda sukaji gaskiyane ba karba
Tala tace Wai mafarki nake ko bacci nakene dagaske auran sadiya aka daura akan wannan uban kudin du wannan Taran na auran sadiya ne du wannan uwar dukiyar da malam yanarka du akan Sadiya yakashe,su Daman malam na da kudi yake cewa Babu Daman da Wanda yaajjewa kudinshi ze kashe Mata Daman Yana sane yaki aurar da sadiya da wuri mu yacucemu yaaurar da namu yaran da wuri Ashe Daman da abinda yataka Akan sadiya da uwarta
Kafin su tala sugama warwarewa Yan kawo lefe suka shigo suna Buda zasu shige dakin umma da Kayan kawar umma me suna nafisa tace kuzo Nan gaban iyayansu ku jere musu akwatinan su Fara budewa su gani su yadace su Fara sa Albarka
Shigowa ake da akwatina ana jeresu gaban su tala se zare Ido suke suna Mai da numfashi da kyar gani sukayi akwatina sunki karewa har se da aka jere musu guda ashirin da hudu akahau bude musu ana nuna musu su habi sun kasa mgn kuka kawai suke tayi kamar kananan Yara wayanda basusan me yake faruwaba sun zata kukan firincikine Nan kuwa ba haka bane na bakincikine
Nafisa Dan ta guma musu bakinciki Dan karamin akwatin da aka zubo sarkokin gwal din tabude musu shi tana nuna musu se haske musu Ido yake wani mahaukacin kuka tala ta fashe da shi
Yankawo lefe sukace kiyi shuru uwar amarya kukan ya Isa haka addua Zaki musu wannan kuka haka
Tala tace kukan barinciki nake gara nayi kukan oh ni tala yau Naga Abu da idona sadiya aka hadawa wannan hidimar du akan Sadiya akeyi wannan uwar dukiyar du ta sadiyace
Habi tace Bari kedai yau munyi kallo sadiya sadiya tafashe da kuka waiyo malam kana Ina kazo nemanka muke
Lami tace Ni raban da Naga malam na manta malam yanuna bambanci atsakaninmu sadiya da Khadija hmm bakomai tadafe kirji tana Mai da numfashi itace tafara tashi tabar wajan takoma daki tadinga kuka burinta taga malam
Nafisa tace ayidai ahankali Kar zuciya ta buga baaja da ikwan Allah zakarar da Allah yanufa da tsara ko ana muzuru ana shaho se yayi Dan haka se hakuri Yan uwa sun Gama ganin Kayan mu kwashe mu Kai dakin uwar amarya baiwar Allah mu ajje Yan uwa Suma su gani su sa Albarka
Su tala nagani ana ta jidar akwatinan ana ta shiga da su dakin umma haka sukaja jiki ba kwari suka shige daki anwaresu Babu su aharkar bikin Babu abinda suka sani Akan harkar bikin sunma kasa sakewa gani suke du atakure suke Dan Suma sunsan sun fita daban acikin Yan bikin dakin
tala dukansu suka hadu
Lami tace kundaiga abinda yake faruwa da idanku Wai yau bikin sadiya akeyi da ranmu da lafiyarmu Anya kuwa sadiya da uwarta mutanene kuwa ko nace Khadija da yaranta mutanene kuwa kiga tinda muka shigo gidannan muke Abu Daya Amma burinmu yaki cika akansu kuga irin kudin da muke kashewa bokayanmu suna banko musu asiri Amma yaki ya kamasu yanda mukeso ko yakamasu asirin yafara aiki muna murna daga baya se yawargaje kuga uwar dukiyar da muka kashe Akan Khadija da ya’yanta Amma abanza musamman uwar taurin Kai sadiya kuga har alkawari malam gobe da nisa yai Mana sadiya ita da aure har abada kuga boka na barno shima abinda yace Mana kenan waiyau gashi sadiya tayi aure auran da du acikin yaranmu Babu Wanda yatabayin irinsa daga dangin malam har na Khadija Babu Wanda aka taba yiwa irin auran da akayiwa sadiya Wai inama tasamo me arziki haka Dan wulakanci Babu abinda muka sani Akan bikin se gani mukayi anayi