Halimatus sadeeya

Yace Amma wuyanki yayi kauri Malika har abin naki yakai haka Wai mekike nufi da mune ko kingaji da Zama damune Dan Allah kiduba lokaci azamanki na matar aure me iyali yanzu karfe nawa tin safe Kika fita se yanzu Kika dawo gida Babu ruwanki da halin da iyalinki zasu shiga da ba kyanan kinsan me yafaru yau agidanki Babu irin Kiran da ban mikiba Baki daukaba karshema kashemin Kira kikai meyasa in kin tashi daga wajan aiki bakya dawowa gida kamar yanda sauran maaikata suke haka Mata masu iyali da suke aiki sukeyi agidansu seke kullin se kin shige yawo daga wajan aiki Wai Ina kike zuwa nagaji nagaji Malika daga yau narufe maganar zuwanki aiki agidannan kinbar aiki gaba Daya inhaka aikin banki yake Allan
yasinewa aikin gaya mace matar aure karnaga kafarki gobe tafita agidannan kinji nagaya miki
Wata dariya takwashe da ita tace ikwan Allah lanlai alyu Ni bance mekake nufi da niba ko kagaji da Zama da Ni se kai ai Kaine kagaji Dani tinda burinka ka wargazamin rayuwa Dan Allah kalli yanda na koma saboda haihuwar yaranka da kake duramin ciki Ina haife maka kamar wata kaza karewama karata kakaiwa mahaifina Dan Zan zufda ciki Dole nahakura Zan haife kandara wlh kamar yanda kagaji Dani Nima nagaji da Kai da yaranka wlh har kunya nakeji ace Ina da Yara har biyu ga na uku ze fito Dan haka ko unguwa bana zuwa da su bazan iya abin kunyaba da ka dameni da kira me Zan maka ko da zaka dawo ka fadamin ba se ganinka nayi ka dawoba ko da zakai tafiya sms ka turamin ta waya ban ganka Ido da Ido ba seyau Ni Ina ruwana da yaranka bakaine mesan yaraba inaruwana da abinda yafaru yau agidan ai da masu aiki zasu kula da komai mgnar kar naje aiki gobe kahana wlh baka isaba ai munyi Yar jejeniya da Kai dolene na cigaba da aikina fita Dole zuwa aiki se nayi gobe Wai tsayama zargina kake Ina nake zuwa Kar naje wajan Yan uwa da abokan arziki na sada zumunci ko malam in kagaji da Zama Dani ba Dole sallarni Nima nagaji da kandararran aurannan na takura da haihuwar Yara ba adadi kabani ta kardata ai tintini Dan ginka ke zigaka kakara aure kaje kayi Ni ka sakeni na wataya bansan haka kakeba na aureka wlh nazata irin wayanyannanne Ashe Ni da Dan kauye nake tare yanda naso Ni da Kai mu Gina rayuwarmu Amma inah kazo kabata komai aliyu wlh Yanzu banasan Zama da Kai Danni inaji Ina gani bazanci gaba da haihuwaba na ratantake kamar wata tsumma gobe in nafita aiki kasakeni kuma kadade baka Kira daddy kafada masaba
Ta zagayeshi tashige Yana kwalla Mata Kira ko waigowa batayiba binta dakinta yayi yamurda ze shiga yaji ta kulle taciki mgn yacigaba da Mata daga wajen
Yace wlh Kika fita gobe Sena Baki mamaki zanga yanda Zaki fita goben kinci darajar cikin jikinki yau wlh da Sena Baki mamaki ban taba dukan maceba Kuma Banda raayin dukan mace Amma yau da Sena karkaryaki Kuma nakwace yarana daga wajanki mahaukaci me irin halin dambobi Kai ai ko damba bazatai abinda kikeyiba mahaukaciya kawai ki koma isilamiya in bahakaba wlh zakiyi nadama Nan gaba
Haka yagaji da fadansa yatafi yakwanta
Yau sadiya tatashi Bata da lfy ciwan ciki na damunta ga amai da take ta kwarawa yaki tsayawa kuskusfa se yatashi acikin gidan su sadiya tin sunayi aboye har mgn ta fito fili suka Fara yadawa sadiya tafito bakin fanfo tana kwara amai
budar bakin habi cewa tai ikwan Allah lami wai me yake faruwa da kene ko ciki Kika Kuma samu tsofai tsofai dake anyi anyi azubar yaki zubewa karya takare asiri yatonu tin kinayi aboye har mgn tafito fili wannan Aman ai ba na rashin lfy bane na cikine Allah yaraba lfy zamusha raino da shagalin suna awai wayaga abin kunya
Kwashewa sukayi da dariya dukansu suka tafa
Tala ce taje wajan sadiya da take amai lokacin umma tataho wajanta
tala tace sannu sadiya kinji ko tazargade zaa jika Mata Tasha ko shawarace Dan Naga in budurwa kamar sadiya na irin wannan cewa ake cikine au mgnar cikin mukeyi da lami tasamu Kinga nazo Nan Ina subutar Baki cewa zanyi ko shawarace take da munta ahada Mata maganin shawara
Umma tace kaf dangina Babu Wanda yai abin kunya insha allahu se dai alheri Kuma mugun nufin mutun sedai yakoma kansa da yardar Allah bama nufin kowa da mugun nufi du wanda yake nufinmu da shi Allah yamaida Masa kayansa kansa kullin bakin mutun baze Fadi alheri ga Dan waniba sedai sharri haba Dan Allah sadiya akanta aka Fara cuta ai cuta nakan kowa Kuma Babu Wanda yafi karfinta sadiya Kuma ba kanta aka Fara aurar da kanneba abar Yaya agida aikin banza kawai du hakurin mutun se an kureshi bafa tsoran kowa nakeba yawan tashin hankaline banaso da alama kwanannan Zan koma Zaki agidannan wlh ko ganina bazakuso kuyiba in nakoma ainahin kalata indai Akan sadiya ne wlh Babu abinda bazan yiba Dan inaji Ina gani bazaku kashemin yataba da bakincikinku sannu sadiya in kin gama wanke bakin tashi muje asibiti kinji
Nan tabarta Baki sake tace ikwan Allah matan gida ku tayani gani daga zuwa dubiya Abu yazama Bala,i
Sukace Allah yakara gashinan tagaya Miki mgn gobema ka Kara ki barsu da abinda yake damunsu kin san yanzu kadan take jira saboda abinda ke jikin yarta mu za amayar Yara
Umma fitowa tayi ita da sadiya ta rike hannunta ta shigesu ko kallo Basu ishetaba bubu Wanda taiwa mgn tarufe dakinta sukai tafiyarsu asibiti sun Dade abakin titi Babu mota ga Rana da ake kwallawa ga sadiya karfinta yagama karewa niyar sume Mata take gashi se yunkurin amai take Amma saboda bakomai acikinta Babu abinda yake fita zaunawa sadiya tayi akasa gaba dayama sotake ta kwanta ga idanta yayi fari yakakkafe umma kuka kawai takeyi du motar da tataho setasa Mata hannu Amma Babu Wanda yakulata gashi bazata iya daukan sadiya sukoma gidaba gababu waya ahannunta duka wayoyinsu Babu caji saboda Babu wuta sunkai caji Kuma Bazata iya barin sadiya abakin titi ita kadaiba taje ko baban su sadiyar ta fadawa awajan sanaarsa ko da zata taho kannan sadiya dukansu suna makaranta durkusawa tayi gaban sadiya tana ta kuka Tama Dena tarar motar tana jiran ikwan Alla kawai
motocin alhaji aliyu me AZURFA ne sukazo shigewa dagudu tindaga nesa aliyu yahango su umma har suka karaso kusa dasu yaga umma se kuka take ga katuwar budurwa kwance ajikinta kamarma Bata motsi har sun shigesu yaiwa yaransa mgn yace su koma wajan su umma motocin na tsayawa aka bude Masa yafita da kansa yaransa na takemai baya dasauri yakarasa wajansu
Aliyu yace baiwar Allah meyake faruwa
Umma du tarude tace mutuwa zatayi Dan Allah ku temakamin mutuwa zatayi mota nake nema asibiti zamu shikenan sadiya Dan Allah karki mutu kiyi hakuri
Alyu yace ki kwantar da hankalinki yanzu za a kaita asibiti
Yaransa yaiwa mgn su daukota asata amota har daya yasa hannu ze dauketa kome aliyu yagani yaiwa me daukan nata mgn karya dauketa dakansa yasunkuya yasa hannu yadauki sadiya Babu wani kyankyami ko tana talaka ko akanshi yace umma tafara shiga mota tashiga ta zauna yakwantar Mata da sadiya ajikinta yaransa se yaban uban gidansu sukeyi saboda irin kyawawan halinsa basuyi mamakin daukan sadiya da yayiba saboda sunsan halayansa na da kyau fin hakama se yayi
umma da yake arude take ko kalar motocin dake jere gabanta da tsadarsu Bata kulaba ta yarta take Dan da acikin hankalinta take wlh bazata shigaba yanda duniya tabaci yanzu bazata shigaba ko nawa za a Bata Dan zata zata saceta zaayi