Halimatus sadeeya

Yace yarinyar tabani tausayi hmm matafa ba abin tausayi bane Dan ba mutuncine da suba Nima gatawanan Ina fama da ita
Wayarshice Tai Kara Yana dubawa yaga mahaifinsane cikin ladabi yadaga Kiran yahau gaisheshi daga Daya bangaran yaamsa mahaifin nashi
Yace aliyu meyake faruwa Kai da matarka takirani tana ta kuka tin safe tace jiya har dukanta kayi Kuma ka hanata zuwa wajan aiki kakuma kulkulle ko Ina na gidan kayi tafiyarka ko halin da take ciki baka damuba tace ko tashi sosai Bata iyawa saboda irin dukan da Kai Mata tin safe nake kiranka awaya Amma duka wayoyinka akashe dazu Kuma da nakira yarankane yadauka yace Kun shiga mitin Dan haka ban Kara nemankaba se yanzu nasan dai iyanzu kadawo gida kana tare da iyalinka Kai yanzu aliyu danrashin mutunci yaushe ka lalace kafara dukan iyalinka waiyau aliyu Kaine kaiwa matarka ta sunnah duka har kake zarginta tana neman maza ka hanata fita aiki ka kulleta ga ciki jikinta Dan rashin imani irin naka Kai ko darajar mahaifinta bazaka kallaba ka ragawa yarsa kasan du auran da zargi yashiga yaharamta,ko yanzu Ina Dadi takira mahaifinta ta fada Masa Nima yakirani yace shi ko kiranka beyiba Dan yasan halin yarsa Bata da gaskiya Kuma nasan wlh kawaice yake Mana Dan dare yayi yanzu da ka ganmu gidanka gobe karka kuskura kafita ka jiramu Ni da mahaifinta zamuzo da safe zaka hadu danine mutumin banza kawai Ina ganinka me hankali Ashe ba haka bane tinda nake da mahaifiyar,ka kataba ganin wani Abu yashiga tsakaninmu bare har nasa hannu na daketa jiyanda Kai shuru kana saurarata kamar na Allah
Aliyu yace ayi hakuri abbah du a abinda Malika tafada maka wlh karyane ba gaskiya bane Allah yakaimu gobe in kunzo gani gata zakuji me yahadamu
Yace haka zakace Mana Allah yakaimu goben in bahali zamu dauke yarinyar ka bumu takardarta
Shidai aliyu hakuri yake ta bayarwa har sukayi sallama da babansa kashe wayarma yayi gaba Daya yaajjeta jiyayi ranshi namasa Kuna sosai Wai malikace tahada Masa irin wannan sharrin lanlai Babu sauran kauna tsakaninsa da malika Ashe kiyaiyar da take Masa har takai haka ta,hada,Masa sharri wajan mahaifinsa ko kunya batajiba jiyayi baze iya kwanciyaba bandaki yashiga ya dauro alwala yatada nafila yadade Yana sallah yakaranta alqur,an yai adduo,I tukunna yaji zuciyarshi tamasa sanyi sosai kwanciyar,shi yayi ba dadewa bacci me Dadi yadaukeshi
Gari na wayewa malika Tai Shirin zuwa aiki tazo falo tazauna ta Dora daya Kan Daya se kada kafa take addua take Allah yasa aliyu yafito yanzu Dan tashirya irin tijarar da zatamai Dan sotake sunayi mahaifansu suzo su samesu ahaka takuma hada Masa wani sharrin Dan su dada yarda da maganganunta Dan sunyi waya da su abbah gasunan zuwa Kuma yau taci alwashin ko tahalin Kaka se ta fita wajan aiki daga Nan ta shige yawo
Shikuwa aliyu besan me yake faruwaba Koda yatashi yaje masallaci yai sallah be koma bacciba karatun qur,ani yatsaya yi har gari yayi haske sannan yai Shiri Yana jiran zuwan su abbah wayarshi ya dauko yakunna ko dadewa ba ayiba Kiran su abbah yashigo suke sheda Masa sun karaso suna falo suna jiranshi babu Bata lokaci yafito zuwa wajansu bayan sun gaisa
Mahaifin malika yace aliyu me yahadaku da malika Dan Ni nafi yarda da mgnarka Akan Tata
Nan aliyu yafada musu du abinda yake faruwa yace gatanan in karya nai Mata Amma ban taba dukan maceba bare matata ta sunnah
Abbah yace malika fadamin du abinda kikace aliyu na Miki tafara mgn bakin na rawa Dan mahaifinta yatsareta da Ido Dan yagano gaskiyarta Dan daga yatsareta da Ido in karya take Yana ganewa in,Ina tafara da kame kame
Mahaifinta yadaka Mata tsawa yace Zaki nutsu kiyi mgn ko Yaya kin sanni wlh yanzu Zan rufeki da duka makaryaciyar banza kawai mgnar da alyu yafada gaskiyane anyi haka ko baaiba
Tace eh anyi haka
Yace kenan mgnar duka ba gaskiya bane
Kai tadaga Masa
Mahaifinta besan sanda yatashi yadauketa da mariba yarufeta da duka ta ko Ina yace Ni Bari na dakeki tinda dukan kikeso har mijinki kikewa sharri bayan kece Baki da gaskiya Ni Daman nasan du abinda Kika ki,Rani Kika fadamin karyane Dan haka naki daukan mataki se naji daga bakin aliyu
Dakyar abbah da aliyu suka karbeta
Aliyu yace daddy ayi hakuri ba ita kadai bace Dan Allah
Dakyar abbah yabashi hakuri yahakura nasiha ababah yai musu Kuma yace Dole takoma aiki ai yasan dashi Kuma kafin tafara sunyi da wajewa sedai malika kartana zuwa ko Ina daga office ana tashi ta dawo gida takuma ce to yarda zata kiyaye tadena yawo
Dan shi Daddy hakuri kawai yakebawa aliyu du kunya ta kamashi Yana me jin haushin halayen yarsa malika
Malika tace abbah Ina da mgn
Yace muna jinki malika Fadi ko menene
Tace Dan Allah kuce Masa yadawomin da yarana Dan yace yakwacesu Kennan
Daddy zeyi mgn abbah yadaga Masa hannu yace haba alhaji kafiya zafi Wai meyasa Naga bayan danka aliyu kakebi itama Dole abata hakkinta Kuma Ni ta,tambaya bakaiba Dan,haka kajimu kawai yakali malika yace Dole Daman zaa dawo Miki da yaranki kinji kiyi hakuri cikin satinnan ko sati mezuwa yaranki zasu dawo dole da me kula da su
Aliyu yace Amma abbah
Rai abbah yahade yace banasan Jin komai nagama yanke hukunci mu zamu shige Allah yaimuku albarka
Alyu badan yasoba yai shuru danshi bashi da niyar dawo Mata da yaranta Dan yasan karya take ba kula da su zataiba du shirintane ta hada
Haka sukai masu rakiya suka tafi ko ciki malika Bata komaba Tai tafiyarta Daman da shirinta tafito ko sallama batayiwa aliyuba ko akanshi be damuba Daman yasaba in zata shige office ba sallama take masaba
aliyu komawa cikin gida yayi yaje yashirya gidan mahaifansa yaje Kai tsaye yaci abincin safe sannan yakarbi abincin da ze kaiwa su sadiya a asibiti Dan sune aransa tin jiya yaso yalekasu da dandare aikine yaimai yawa ko da ya Isa asibiti yasamu jikin sadiya da sauki sedai bacci take lokacin ta juya baya bega fuskartaba Kuma shi ba irin mutanan,Nan bane masu kurillah bare Kuma mace da ba birgeshi takeba ko kallo Bata isheshiba dan shi bilkakki haushin Mata yakeji
Umma tace bawan Allah Ni bansan da wana irin godiya Zan makaba mahaifin yarinyar yaso ku hadu yai maka godiya Allah beyi zaku haduba yadade anan ko Allah zesa kazo ya ganka yai maka godiya Kuma ko sunanka ban saniba bare inda kake yaje har gida yaima godiya Akan alherin da Kai Mana Allah yasaka da alheri Allah yabiyama bukatunka na alheri
du da aliyu dariya Bata dameshiba se da yai dariya Dan shi dariyama maganarta tabashi yace Kai umma Wai Akan Dan wanna abinda nai muku zemin godiya haba Ni base yamin godiyaba ko ke umma Dan Allah karki Kuma yimin godiya inaga ko Baki haifeniba kin kusa haifata kilama kin haifi kamata Albarkar manya nake nema kuyimin adduar alheri Kun gamamin komai arayuwata munyi mgn da Dr yace in yaga jikin da sauki gobe ze sallameku inaga in da lokaci Zan dawo da dandare insha allahu in Kuma ban samu damar dawoba shikenan Allah yakuma hadamu da alheri Zan turo direba yamaidaku gida gobe
Umma ita tsayawa tayi tana kallanshi rasa me zatace Masa tayi har yafice daga dakin mutumun na birgeta ga Kamala ga kwarjini da yake Mata in ta ganshi da kyar tabude Baki tace Allah me iko insha allahu kullin Zan dinga binka da adduar alheri nasan sadiya ma zatana maka addua kullin tinda kaceci rayuwarta a lokacin da take tsakanin mutuwa da rayuwa shi baya gajiya da alheri bawan Allah wannan Kayan abinci da yakawo Mana wanima Ni ban taba cin irinshiba bare agidanmu matarsama na da kirki tadau nauyin dafawa akawo Mana Allah yabiyaku