HAUSA NOVELINTEESAR 4

INTEESAR 4

dauke kanta, suna nn xaune a hka har na

kusan minti sha biyar ya juya yana kallonta

yaga robon ruwan wasu mutane kawae

take kallo, ya kamo hannunta yace “xaki sha

ruwa ne inteesar” kai ta gyada masa ya

koma baya da mamaki yana kallonta, da

sauri ya mike yace “ina xuwa bari na kawo

maki kinji bata sake cewa komai ba yyi

hanyar stairs da sauri yana waiwayota

xuciyarsa na bugawa ya haura sama dauko

mata ruwa, tsam ta mike ta fara kalle kalle ta

bi hanyar da taga mutane na bi, da sauri

take tafiyar kmr ana turata, har ta isa gate

masu gadi suka bita da kallo don bbu

uniform din mahaukata jikinta, ta fice tayi

hanyr hagu duk da tafiya ce mai shegen

nisa tana ta tafiya har ta daina hango

asibitin, Aliyu ya sauko rike da ruwa da kofi

a hannu ya ga wajen wayam bbu fateema,

kalle kalle ya shiga yi a rude bae ga alamarta

ba, ya hango faruuq ya karasa gunsa da

sauri yace “fateema fa,” faruuq yace “wace

fateemar ba nn na bar ku tare ba,” ya dafa

faruuq ganin kafafuwansa sun kasa

daukansa yce “wlh nn na barta naje dauko

mta ruwa” cikin tsawa faruuq yce “wat?

Don me xaka barta ita kadae” tare suka

shiga xaga asibitin suna nemanta ta ko ina

amma basu gnta ba sune har gate duk Aliyu

ya birkice kmr wani xautattce, sae ga Anty

Nafeesa ta shigo asbitin rike da abinci da

mamaki ganin yanda suka tara jama’ah tace

“me ya faru” faruuq yy karfin halin cewa

“bamu ga fateema ba” kmr kar faruq ya fadi

hka sukaji Aliyu ya saki wata irin kara ae sae

da asibitin ya dauka sae kawae suka ga ya

sulale wajen.

Hajiya ta shigo asibitin rike da kayan

tsarabar da tayo ma yan Nigeria barin

safeena da uwarta tana dan rera wakarta,

jikin wani ward taga Nafeesa tsaye tana

kuka ssae ga wani likita da alamar dan

Nigeria ne yana lallashinta, da sauri ta

karasa kusa da ita tanakallonta tace “me ya

faru Nafeesa,” da kyar Anty Nafeesa na

girgixa kai tace “bamu ga inteesar ba,”

Hajiya tayi shiru tana kkrin boye murnar ta,

can kmr warce ta tuna abu da sauri tace

“Aliyu fa,” Anty Nafeesa ta kasa cewa komai

sae kuka, Hajiya ta juya a rude tana kallon

likitan dake gaban Anty Nafeesa tace “ina

da’na,” da sauri ta bude ward din da

inteesar take mai xata gani, Aliyu yana

dambe dalikitocin dake kansa sae Fateema

yake kira, hajiya ta fito a guje tayi kan Anty

Nafeesa a rude tace “me ya samu Aliyuna,”

likitan ne ya bata amsa “suma yyiya farfado

a hka shima ana ga kmr ya samu matsala a

kwakwalwa,” Hajiya ta fasa ihu tace”hauka

Aliyu yake yi hka,” kuka ta fashe da a rude ta

ciro wayarta ta shiga danne danne tana

gunjin kukasae rawa hannunta yake ta kara

a kunne, “hello salame kina jina maxa ku je

ku karya asirin nn da kuka yi ma inteesar ya

koma kan dana wllh,” ta katse kiran a rude

tana rusa kuka sae kallonta Anty Nafeesa

take da mamaki, cikin kuka tace “wlh

Nafeesa safeena ce da uwarta suka

haukatar da inteesar su suka haukatar da

ita suka gaya min,” Anty Nafeesa ta dafe kirji

ta kasa cewa komai ta fashe da kuka tayi

waje, Hajiya ta bita ita ma tana kukan kmr

mahaukaciya, Faruuq ya shigo asibitin a jike

don anyi ruwa ssae, bbu inda bae xaga ba a

india amma bae ga inteesar ba, ynxu ma

daga gidan talabijin da redio yake, duk ya

xama kmr wni mara lfya, ganin inda su Anty

Nafeesa ke kuka yasa da kyar yace “Aliyu fa,”

cikin kuka Hajiya tace “wllh ya haukace

faruuq ku ceci rayuwar da’na ku nemo

inteesar, ina inteesar ta shiga don Allah a

nemota,” ta fashe da wani matsanancin

kuka ta xube wajen, sae kallonsu ake

gwanin ban tausayi, faruuq ya dafa bango

ya kai minti kusan biyar a hka da kyar ya

haura sama ya shiga ward din da inteesar

take, duk alluran da suka dinga yi ma Aliyu

bae nutsu ba don hauka karara ya dinga

gwada masu, duk aka fita aka kulle dakin

aka barshi shi daya ya dinga buge buge

yana jijjiga kofar abun dae ba ddin ji,

likitocin suka hana faruuq shiga ya jingina

jikin bango hawaye ya cika idonsa da kyar

ya ciro wayarsa ya shiga neman layin

Haisam, muryarsa na rawa yace “Haisam

abu ya baci Haisam inteesarta fita daga

asibitin, Aliyu baya cikin hankalinsa shima

brain dinsa ta samu matsala, ka sanar da

Abba baxan iya gaya masa ba” bae jira me

Haisam xae ce ba ya katse wayar sae

hawaye. Inteesar kamnata tafiya abunta sae

dae idan taji kmr an mintsileta a mararta ta

xauna ta huta snn ta ci gabada tafiya ko ina

tabi sae an kalleta, hadari ya hadu garin

ssae tana ta tafiya abunta kowa nata kkrin

ganin ya isa gidansa, har daga karshe ruwa

mai karfi ya sauka ta xauna kan wani dakali

ruwan ya dinga dukanta amma bata damu

ba, har ruwan ya tsagaita bayan kmr awa

biyu, ta mike da kyar ta ci gaba da tafiya

tana rawan sanyi, kasa ci gaba datafiyar tayi

dae dae wai babban plaza ta dalilin wani

mugun ciwo da taji mararta da kugunta

nayi a tare da kyar ta ja kafa ta samu wani

gefen mota ta durkushe gaban plazan tana

rike da kugunta sae rawan sanyi take tana

yarfe hannu alamar axaba, indiawa sae

kallonta suke suna wuce ta, don su dama

basu gaji taimko ba ko a tsakaninsu, kuka ta

shiga yi ganin ta kasa daure ciwon Abbanta

ta shiga kira tana juye juye jikin motar da

take taji an bude motar ta koma baya da

sauri, da ganinsu matada miji ne, matar na

kallonta da yaran india tace “keme kike yi a

nn,” kai ta daga tana kallonsu bakaken fata

ne kmr ita amma da gani xasu Haifeta, ta

mike da kyar tana rike da kugunta xata bar

wajen matar tace “amma ke yar Nigeria ce

kuma bahaushiya ko,”ko kallon matar bata

yi ba taku daya biyu ta xube wajen tana

wayyo cikinta, matar ta juya tana kallon

mijinta dake tsaye kmr wani tsoko yana

kallonsu tace “Abbanmu kalli fa yar uwar mu

ce ga kuma alamar bata da lfya mu taimaka

mata,” bata jira me xae ce ba ta karasa kusa

da inteesar da sauri ta dago ta tana kallonta

tace “sannu kinji yan mata daga ina kike

hka,” inteesar bata ce komai ba sae girgixa

kai da take don axaba, matar ta dagota da

sauri ta saka ta bayan mota ita ma ta shiga

tace”mu je Abbanmu,” ya shiga motar ya

tada suka bar wajen, ihu ta dinga masu a

mota duk ta rikice jin axaba na neman

kasheta matar na rike da ita tana tofa mata

addua, mijin ma duk ya rude yace “asibiti

xamu ko,” tace “A’a muje gida kawae xan

karbi haihuwar,” babban gida ne ssae,

matar tace “ka taimaka min mu fito da ita

Abbanmu,” ya xagayo yana kallon inteesar

da ta gama fita hayyacinta ciwo ya ci

karfinta, tace “help me mana Abbanmu,” ya

koma baya da sauri har lkcn yana kallon

inteesaryace “baxan iya ba, bari na kira

maku yan aiki,” yyi cikin gidan da sauri sae

gashi ya fito da yan aiki suka taimaka mata

ta shiga ciki da inteesar

.

.. Da taimakon matar Inteesar ta Haifo

santala santalan yaranta maxa biyu, ba

karamin wahala ta ci ba, matar ta tausaya

mata ssae, babban likitace don hka tayi

mata duk abinda ya kamata snn ta kaita

bedroom dinta ta kwantar da ita kan ta

hado mata tea har tayi baccin wahala, mai

gidanta kuwa kasa xaune yyi har sae da

inteesar ta haihu, snn hankalinsa ya kwanta,

matar ta gyara yaran ta kaisu gefen uwarsu

ta kwantar dasu gashi gaba dayansu basu

da lfya, inteesar bata farka ba sae can tsakar

dare matar na xaune gefenta rike da dayan

yaron dake ta kuka ta kwantar dashi tana

mata sannu, kai kawae inteesar ke gyada

mata, ta kira yan aiki su kawo mata tea,

suka kawo suka ajiye, matar tace maxa ki

sha ki basu nono yunwa suke ji kuma duk

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button