HAUSA NOVELINTEESAR 4

INTEESAR 4

ni ai gun inteesar nace xanje ba Aliyu ba,” to

kawae yace mata don takaici ya fice daga

falon, inna aka shiga shirya kaya ba ji ba

gani har da su kitso, Abba kam da sassafe

ya bar gidan ranar da tace xata tafi lgs din,

bayan ya gaya ma momy abinda ake ciki da

kuma inteesar da basu gani ba don yaga

boye mata bashi da wani amfani, momy

batanuna masa komai ba, amma ba karamin

kukan tashin hankali tayi ba bayan fitarsa,

inna ta daga kai da sauri xata fara masifar

waye ya bude mata kofa ba sallama, suka yi

ido hudu da inteesar, inna ta yo waje da ido

ta mike da sauri tana kallon yaron hannunta

tace “me xan gani hka ni Rahmatu, har kin

haihu ban je ba kuma ban sani ba,” kawae

sae ta fashe da kuka tace “Amma Allah ya isa

tsakanina da yan gidan nn gaba daya, ynxu

anyi min adalci knn” takaici ya ishi inteesar

ga Anty a tsaye, gskya inna bata yi ba,

shigowa tayi ta xauna Anty ta kasa shigowa

sae kallon inna take, inna ta ciro waya tana

huci tace “maxa nemo min layin Bukar,”

kursum da gaba daya hankalinta na kan yan

biyu ita ma da mamaki ta karbi wayar takira

mata Abba ta mika mata, cikin daga murya

tace “amma Allah sae yyi mana hisabi da ku

Bukar, ynxu yarinyar nn ashe har ta haihu

ban sani ba, tun yaushe nake cewa a kai ni

aka ki kaini,” ta karashe maganar da

matsanancin kuka ta jefar da wayar,

Inteesar da haushi ya cika ta tace “Anty ki

shigo mana,” ganin har lkcin Anty na tsaye

tana kallon inna, Anty tayi murmushi ta

shigo falon ta xauna, wayar inna ya shiga

ringin kursum ta mika mata tace Abba ne, a

fusace tace “share mara mutunci kawae,

uwar me xae gaya min, maxa kije ki kira

min Zainabu don uwarta ita ma” inteesar

kam kunya ne ya isheta kawae, da ta sani da

gun momy kawae ta tafi, inteesar ta

kwantar da yaron hannunta ta bude fridge

ta ciro ruwa da lemotunda sun karya a

lagos, ta ajiye ma Anty snn ta dauko kofi

mata ajiye mata, Anty tace “da kin bar shi

kawae inteesar, cikin yyimaki sauki ynxu

ko,” inna ta mike da sauri tace “cikinta ke

ciwo,” inteesar ta galla mata harara bata ce

komai ba, kursum ta shigo rike da wayar

momy tace “inna wae Abba xae maki

magana,” inna tace “da’alla ni a rabu dani

me xae ce min,” ta fixge wayar ta kara a

kunne tace “me xaka ce min Bukar,” wace

inteesar din kasani, ae ni sae Allah ya saka

min gata nn da yan biyunta sun xo da wata

doguwar mata fara me dogon hanci, yo ina

xan sani Bukar,” ta katse wayar ta ajiye, tana

kallon Kursum tace “baki ce ma Zainabu ina

kiranta bne,” kursum tace “tana xuwa,”

inteesar na kallon kursum tace”kursum

Abba fa,” inna tace “yace yana xuwa,”

inteesar ta daure fuska tace “tare da bako

muke a waje inna,” inna tace “toki shiga da

shi falon Abban naku,” inteesar ta mike ta

fita ta yi kofar gida tace “Abbanmu ku

shigo,” har falon Abba ta kai sa, Zainab na

biye da ita a baya, ta bude fridge ta ciro

masa lemo da ruwa ta ajiye masa da kofi, yyi

mata godiya snn ta kama hannun Zainab

suka fita daga falon, a sanyaye momy ke

tahowa daga bangarenta duk da kursum

tace mata inteesar ceta xo sae ta kasa yrda

bayan ga abinda Abba ya fada mata jiya,

suna hada ido da momynta ta ruga a guje ta

rungumeta cikin farin ciki, ji tayi kmr ta fi

shekara rabonta da ita, momy kasa cewa

komai tayi sae hawaye, hkn ya ba inteesar

mamaki jikinta yyi sanyi tace “momy me ya

faru,” momy ta kasa cewa komai sae kallon

Zainab da take, da kyar momy tace “wacece

wancan,” inteesar tace “parent dinta suka

dawo dani gida momy suna da kirki ssae,

momynta na falon inna, muje ki ganta”

momy bata ce komai ba suka yi bangaren

inna.

Suna shiga falon inna, inna ta fara ma

momy jaraba, “ynxu abinda kuka min kun

kyauta knn Zainabu,” Momy bata tanka inna

ba ta shiga gaida Anty, Anty ta amsa da

fara’arta, inna tace “magana nake maki

Zainabu,” Anty tace “mama bana tunanin

sun san da Haihuwar inteesar fa,” inna ta

galla mata harara tace “ya xaki ce min hka,

ke me kika sani,” Anty tayi murmushi tace

“to mu a india muka tsinci inteesar tana

nakuda sati biyu da suka wuce, a hannuna

inteesar ta haifa yaran nn, kuma bayan ta

dawo hankalinta na tambayeta gun wa taxo

a india, tace ita ma bata san wa ya kawota

ba, satin ta kusan biyu a gidanmu muka

maido da ita nan Nigeria da mai gidana,”

inna tayi tsaki tace “ni ban gane

shirmamman hausan nn naki ba, uwar wa

inteesar ta sani a india da xa ki ganta a can,

da ma lagos kika ce min, wnn karya kike yi”

sallamar Abba ne yasa inna yin shiru tace

“ka xo kaji min karyar bnxa Bukar wae a

india aka ga inteesar tana yawo,” Abba ya

shigo falon yana kallon inteesar da mamaki,

ya xauna ba tare da ya shirya ba ya sauke

wani ajiyar xuciya ya dafe kansa yace

“Alhmdllhi,” inna tace “ta me,” kasa ba inna

amsa yyi yana kallon Anty yace “baiwar

Allah a ina kuka ga wnn yarinyar don Allah,”

Anty tace “a new delhi ni da mai gidana

mun

fito daga wani plaza,” Abba yace “Allah

ubangiji ya taimake ku kuma kmr ynda kuka

taimakeni ya saka maku da alkhairi,” inna

tace “yau naga tsiya, wae me ke faruwa ne,”

Abba ya juya yana kallon inna yace “baaba

yau kusan wata uku knn Fateema bata cikin

hankalinta bamu gaya maki ba, mu ne har

india daga lgs nemo lafiyarta satinmu uku a

india aka nemeta aka rasa yau sati biyu da

kwanaki knn da muke nemanta a india……”

inna ta katse sa da sauri tace “kmr ya bata

cikin hankalinta, hauka take ko me,” Abba

yace “kwarae kuwa baaba amma wa ya

bamu karfin gwiwan xuwa mu gaya maki

wnn mummunan lbrin mara ddin ji , baaba

na shiga damuwar da ban taba shiga ba a

rayuwata, ynxu hka Aliyu na can a asibitin

shima ba hankalin tun bayan da muka nemi

fateema muka rasa, su Nafeesa da Haisam

ae duk suna can” tunda Abba ya fara

magana inteesar ta tsaya da mamaki tana

kallon Abba, wae ita ce tayi hauka, maganar

Abba ta karshe yasa ta hawaye, inna ta mike

jikinta na rawan bala’i tace “waye ya

haukatar min da jikata a gaya min don

bamu

gaji hauka a xuri’armu ba,” Abba ya sauke

ajiyar xuciya bae ce komai ba, kuka ssae

inteesar take, hka ma momy, Anty kam

jikinta yyi sanyi, don bata san a haukace

suka tsinci inteesar ba, kuma bata ga alamar

hkn ba, inna ta dinga ihu da kuka a gidan

wae a kaita gidansu safeena tasan baxae

wuce aikin asiri ba su suka mata asiri, Abba

ya mike bae bi ta kan inna ba ya fice a

xuciyarsa yana hamdalar bayyanar inteesar

da gaggawa hka, wae bayan komai ya lafa

inna ta sani amma dubi reactions dinta

yasan bae yi kuskuren rashin gaya mata da

bae yi ba, yana fita Nafeesa ya fara kira ya

sanar mata snn ya shiga falonsa ya tarar da

Abbanmu xaune yana kallon news, yace

“ashe bako gareni basu sanar da ni ba,” ya

bashi hannu suka gaisa snn ya shiga yi

masa gdya kafin yyi masa bayanin abinda

ya faru. Momy ta mike ta fita tayi

bangarenta ganin irin haukan da inna take

ba ji ba gani, Anty na bata hkuri, “ki kyaleni

nayi yarinya, a haukatar min da jika bata yi

masu komae ba, kuma nayi shiru, ae da

wani

abu ya sami inteesar a duniyar nn da kowa

kashinsa ya bushe a gidan nn, shi kuma

Aliyu ya karata da haukansa tun da shi ya

siyar ma kansa dama na sha gaya masa shi

mahaukaci ne,” ta karashe maganar tana

huci ta shige daki, inteesar dae sae kuka

take duk hnklinta na gun Aliyu da Abba yace

ke hauka sbda ita, Anty ta shiga hada ma

Hassan dake kuka abinci, inteesar ta mike ta

bi inna daki jikinta a sanyaye, katuwar

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button