HAUSA NOVELINTEESAR 4

INTEESAR 4

tunkuyarta take kkrin fitowa da xata je

daura

ruwan wanka, inteesar na hawaye tace

“inna

don Allah kice ma Abba su barni na je gun

ya Aliyu tunda……” inna ta dakatar da ita a

fusace tace “kina danyan jegon xaki tafi gun

wani mahaukaci can,” inteesar ta fashe da

kuka tace “ni ki daina ce masa mahaukaci, ki

taimaka min kiyi ma Abba magana ” inna

tace “to baki isa ba don ubanki,” ta fice da

katuwar tukunyanta tana kwala ma kursum

kira ta siyo mata itace, inteesar ta xube kan

gado tana ci gaba da kuka, ta kai kusan awa

daya a hka taji ihun Husaini ta fito da gudu

ba tare da ta shirya ba, taga inna ce ke

masa wanka sae kunya ta kamata ynda ta

fito a rude, Anty tayi dariya tace “wanka ake

masa ba wani abu ba maman biyu,” inna ta

tabe baki tace “ki rabu da gantalalliya tana

danya da ita wae gun wancan mahaukacin

xata ya buge min ita a bnxa, shi fa ya janyo

ma kansa yar nn, wata shegiyar karuwar

mace me xubin kafurae ya auro suka dinga

walakanta min jikata sae ga shi wae har sun

haukatata ban sani ba, gashi ynxu Allah yyi

mata sakayya abunsu ya koma masu, ni dae

Alhmdllhi tunda jikata ta dawo lfya, miko

min tsummar can” inteesar ta juya ta koma

daki a sanyaye hawaye na bin kuncinta,

kursum ta shigo tana kallon inteesar tace

“Abba yace kije,”

.

….A hankali Inteesar tayi sallama ta shiga

falon Abba, ta xauna kasa tace “Abba gani”

Abba yace ta koma kan kujera, ta mike ta

xauna kan kujera tana kallon Abbanmu

dake ta bin ta da kallo, tayi murmushi ta

sunkuyar da kanta kasa, Abba yyi shiru snn

yace “ina yaran,” xata yi magana sae ga

kursum ta shigo rike da Hassan, Zainab na

biye da ita a baya rike da Hussain, duk Abba

ya amshesu yana kallonsu yana murmushi,

kmr ba jarirae ba suma idonsu kyar a kansa,

sae da ya tofa masu addua gaba daya snn

ya kwantar dasu kan kujera ita dae inteesar

kanta na kasa, Abba na kallon Abbanmu

yace “dota dinka knn ko Alhaji Umar ko,”

Abbanmu yyi murmushi yana kallon Zainab

yace “eh ita ce diyata ta farko,” Abba yyi

murmushi yace “Allah sarki sae naga suna

kama da inteesar,” Abbanmu yyi dariya yace

“hka ne kam,” kursum suka fita tare da

Zainab snn Abba yace “kina jina fateema,” ta

gyada masa kai yace “idan kin huta xaku

koma can india dasu Antynki amma fa sae

idan kina son komawa baxa mu takuraki ba,

nasan dae kina sane dae Aliyu bashi da lfya

ko,” kai kawae ta gyada masa tana hawaye,

Abba yace “ba kuka xakiyi ba, Addua xakiyi

masa,” a hankali tace “Abba ni na gama

hutawa mu tafi yau kawae,” Abbanmu yace

“yauwa fateema ashe kina da hankali gwara

kije gun mijinki tunda rashin ki ya jawo

masa wnn lalura,” bata ce komai ba Abba

yace “shknn fateema Allah yyi maki albarka,

amma ki bari gobe ku tafi sbda yaran nn kar

suyi xaxxabi je ki ki kira min momynki,” ta

mike ta fita daga falon, Abbanmu yace

“xanje gun wani abokina dake nn gadon

kaya,” Abba yace “to shknn Alhaji sae ka

dawo,” Abbanmu ya mike ya fita yana kiran

Anty a waya ya sanar da ita xae dan fita,

bayan fitarsa da minti biyar inteesar suka

shigo da momynta, Abba yyi mata bayanin

abinda suka tsara da Abbanmu kan cewa su

koma can india da inteesar gun Aliyu, momy

tace “hkn ma yyi, Allah dae ya basa lfya,”

Abba yace”Ameen don son Annabi,” inteesar

ta mike ta fita ta bar masu falon ta koma

falon inna, kmr ba jego take ba garau take

jin kanta, a bakin kofa ta tar da inna tana

masu lafiyayyan girki inna tace “Allah sarki

Aliyu, wae wani irin ciwo aka ce yake yi hka,

a dawo min da jikana gida kawae na nema

masa magani,”ko kallonta inteesar bata yi

ba ta shiga falo Anty ta sata gaba ta shanye

kunun da inna ta dama mata don har lkcn

bata yi wani break din kirki ba, kasa sukuni

tayi ranar Allah Allah take kawae gobe yyi ta

je ta ga Aliyu duk hnkalinta yyi gunsa,

momyce ta dawo da yaran daga gun Abba

suna kuka ta bai ma mamarsu su ta fita,

wajen karfe uku Anty ta tafi bangaren

momy inna kuma ta tafi nemo ganyen

darbejiya, inteesar nata fama da Hassan

dake ta yi mata rigima kursum na rike da

Hussaini, kursum tace “wae sunansu knn,”

inteesar tace “A’a ba a rada masu suna ba

har ynxu ae, wae ina su khadija” kursum

tace “khadija na gidan Zainab bata da lfya,

rahma kuma na can gidansu mamarmu”

inteesar tace “Allah sarki Zainab, Hajiya da

umma fa,” kursum tace “hajiya tayi tafiya,

umma kuma tana can gidansu Fadila ta kara

kashe aurenta, shine Abba yace su tafi su

bar masa gidansa,” inteesar tayi shiru da

mamaki tana kallon kursum, can tace

“yaushe hkn ya faru,” kursum tace “kusan

wata biyu knn, inna ce tace Abba ya koresu

ko ita ta bar masu gidan,” inteesar bata

sake cewa komai ba amma ko kadan bata

jin ddin abinda inna ke yi, fira suka dinga yi

da kursum har inna ta dawo duk ta hada

xufa da darbejiyarta tace “da kyar na samo

wnn, maxa ki tube ki shiga bayi ki jira ni na

juyo ruwan,” inteesar ta mike da sauri tace

“ke dawa, wllh baxa kiyi min wanka ba da

girmana kuma da wnn abun, to wae ca nayi

maki banyi wanka bne,” inna tace “yau naga

tsiya, har wani wanka kike yi dubi ynda kike

tafiya kmr wata rubabbiya, wa ya sani ma

ko da ruwan sanyi ake maki wanka a can”

ko kallonta inteesar bata yi ba ta fice daga

falon tayi gun momynta. Washegari har

airport Abba ya kai su a motarsa aka bar

Zainab gun momy don xasu dawo, inteesar

bata ji ddin rashin fitowar da momy tayi ta

rakasu ba, basu samu jirgin da xae je india

ranar ba a Aminu kano don hka sae da suka

fara xuwa lgs snn suka kama hanyar india

 

.. Da yamma inteesar da Abbanmu suka

kama hanyar asibitin da Aliyu yake bayan

sun huta can gida, a motar Abbanmu suke

tafiyar sae bin ko ina take da kallo india yyi

mata kyau ssae, Anty na gida da yan biyu

don xaxxabi ssae suke tun bayan saukansu

da safe, suna isa asibitin gaban inteesar ya

shiga faduwa suka yi parkin, suka fito

Abbanmu ya shiga kiran Anty Nafeesa kmr

ynda Abba yace masu, ta fito da sauri ta

rungume inteesar tana hawayen murna ita

ma kukan ta fara yi, a hka ta jata suka shiga

asibitin, Inteesar taje da gudu ta rungume

Haisam da hawaye ya cika idonsa ganinta ya

ma rasa me xae ce, da kyar ya iya cewa “ina

yaran inteesar,” ta goge hawayen fuskarta

tace “suna gun Antyna,” ido hudu suka yi da

Hajiya dake rabe wani lungu kmr marainiya

Hajiya ta taso tana hawaye ssae ta rungume

inteesar ta kasa cewa komai, kuka ssae

inteesar take, murya na rawa Hajiya tace “ki

yafe mani inteesar ba don halina ba,” kasa

cewa komai inteesar tayi sae gyada mata

kai take, Haisam ya gaida Abbanmu dake

tsaye, hka ma Anty Nafeesa da Hajiya duk da

basu sansa ba suka basa kujera ya xauna,

inteesar sae kalle kalle take, taji ba a ce mata

komai kan Aliyu ba, cire kunya tayi tana

kallon Haisam a hankali tace “ya Haisam, ya

Aliyu fa,” ya dan yi shiru snn yace “xaki

gansa akwae likita a dakin ne ynxu,” ta

gyada masa kai jikinta a sanyaye, Anty

nafeesa tace “ina yaran inteesar, Abba yace

da su kuka taho” inteesar tace “suna gun

Antyna a can gida,” bbu wanda ya sake

cewa komai cikinsu har likitan dake dakin

ya fito, Haisam ya mike ya bisa da turanci

yake tambayarsa xa a iya shiga a gansa,

likitan yace xa a iya shiga amma kar wanda

yaje kusa da shi,” inteesar ta mike da sauri

gabanta na faduwa nn da nn hawaye ya

cika idonta, tayi hanyar kofar Haisam ya

dakatar da ita, da kyar ta juyo tana kallonsa,

Haisam ya karasa yace ta koma baya, ba dan

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button