HAUSA NOVELINTEESAR 4

INTEESAR 4

kmr wani mara lfya, ta

dauke kanta da sauri shima hka

.

A nutse Abba ya kira sunanta “fateemah,” ta

dago a hankali tana kallonsa, ya sauke ajiyar

xuciya yace “ko da yake ma bari na fara ta

kanki baaba,” inna na kallonsa tace “eh ina

ji,” yana kallonta yace “Baaba kar ki fara

magana nn ba tare da ance kiyi ba, duk me

xaki ji a nn don Allah karki bude bakin ki,

idan ana bukatar cewar ki xa’a sanar da ke,

don Allah dae nace,” inna ta tabe baki tana

girgixa kafa, ya maida dubansa ga Inteesar

da ta sunkuyar da kanta yace “fateema,”

wnn karan kasa dagowa ta kallesa tayi, bae

damu ba ya ci gaba “Ashe ke dama mara

hankali ce bansani ba,” inna tayi karaf tace

“kmr yaya,” Abba ya hade rae yana kallonta,

ta daga hannu da sauri tace “to nayi shiru,”

Abba na kallon Inteesar yace “ynxu abinda

nake so dake shine kawae ki gaya min

asibitin da kika je,” Hawaye ya cika idonta ta

kasa cewa komai, cikin daga murya Abba

yace “ba magana nake maki ba,” a hankali

Aliyu yace “ae Safeena ce tayi mata jagora

wae,” a fusace inna tace “ga magana nn

xaku tsaya kuna wani lauyewa, ni dae nasan

jikata baxata iya aikata wnn danyan aikin da

kanta ba” Abba yyi shiru yana kallon Aliyu

snn yace “kae wa yaga maka hka,” Aliyu

yace “ita da bakinta ta fada,” inteesar ta

watsa masa harara tace “ni ba muyi hka da

kai ba, kuma safeena bata yi min ko wani

jagora ba ni da kaina na tafi inda naje,

hasalima bata sani ba,” Aliyu ya yo waje da

ido da mamaki yace “kika ce me?” ta xaro

masa ido tace “ehh” ya dafe kansa yace

“innalillahi wa inna ilaihi raji un, kika sa naje

na ba yar mutane takarda ashe sharri kika

mata” Abba yace “takardar ka kai mata?”

Aliyu ya kasa cewa komai sae kallon inteesar

da yake, a rude Hajiya tace “kana da hankali

kuwa Aliyu, ka saketa fa kace?” Abba yace

“saki nawa kayi mata,” Aliyu ya sauke ajiyar

xuciya yace “daya,” snn ya ciro pen daga

Aljihunsa ya mike ya shiga dakin Abbansa

duk aka bi sa da kallo ya fito rike da farar

takarda ya isa study desk ya duka xae yi

rubutu Abba yace “meye hka kke yi Ali,” ya

dago bbu yabo bbu fallasa yace “ita ma

rubuta mata nata xanyi Abba” Abba ya daka

masa tsawa “kana da hankali kuwa, a

gabana don baka da kunya xaka dauko

takarda kana gaya min maganar bnxa,”

cikin daga murya Abba yace “dawo nn ka

xauna,” Hajiya tace “kambu, ae wlh baka isa

ba Alhaji, ita wancan din da ya saka ance

maka gata ne bata da, ae ita ma Wllh sae ya

rubuta mata nata, na rantse,” Abba ya mike

a fusace yace “fice min a falo Aisha, nace ki

fita,” ta mike tace “ae ko baka fada ba fita

xanyi, amma wllh kmr yanda tayi makirci

tasa ya saki matarsa ta arxiki ita ma sae ya

saketa, ae dama idan bata xama makira ba

sae Allah ma ya tambayeta, abu a jini,” ta fice

tana huci, inna tace “shegiya yar wahala, ae

in Aliyu ya saki Inteesar yau duk kuma sae

nasa dana ya rubuta maku takardarku wllh

wllh,” inteesar ta fashe da kuka tace “Abba

ni ka bar shi ya rubuta min takardata don

Allah don Annabi,” Abba ya daka mata tsawa

a fusace “rufe min baki, stupid” Anty

Nafeesa kam kasa cewa komai tayi sae

kallon inteesar take, momy dama hankalinta

na kan TV, Abba yyi shiru na wani dan lkci

snn yana kallon Aliyu yace “sae kaje ka

mayar da matarka,” Aliyu bae ce komai ba

sae da har lkcin kansa a kasa yake da

ganinsa kasan ran maxa ya baci, Abba ya

hade rae yana kallon inteesar yace “ynxu

dalilin cire cikin jikinki kawae nake son ki

gaya mana gaba daya mu ji,” hawaye ya cika

idon Inteesar tayi shiru kanta a kasa, har

sae da Haisam ya daka mata tsawa, “ba

magana ake maki ba,” a fusace inna ta mike

tace “ohh ni yau naga tsiya xasu kashe min

jika, kuma sun hanani magana ” ta fashe da

kuka xata bar falon, Abba yace “haba baaba

ki dawo muji daliin da yasa tayi hka, ae bbu

wanda yyi mata wani abun a nn,” da kyar

aka lallaba inna ta dawo ta xauna tana

share hawaye, Abba yace “muna jin ki

Fateema,” inteesar ta dago kanta a hankali

tana kallon Aliyun, taga shima kallonta yake,

ta kauda kanta tace “sbda bana sonsa

shima kuma baya sona yasa nayi hkn Abba,”

ta fashe masu da kuka ssae tace “Abba

tunda na taso ya Aliyu ke cutata a gidan nn,

tun ban san kaina ba, ban san me nayi masa

ba ko dan ba gidan ubana bne, ya tsaneni

kuma baya son bude ido ya gan ni cikin

gidansu, ko uwar da ta haifeni ma bae bari

ba, idan an manta randa ya daga hannu xae

mareta to ni ban manta ba, kuma har gobe

baxan manta ba, ban san me muka yi masa

ba, duka bbu wanda ban sha a hannun

Aliyu ba, idan ba a manta ba wani rashin

lfya da nayi na kwana da kwanaki shi shine

sanadin sa, amma ban fada ma kowa ba,

har ka hada mu aure Abba, kuma tunda ka

hada mu abba ko sau daya ban taba jin

ddin xaman gidansa ba, sae nayi sati biyu

ban daura idona a kansa ba, bae san ci na

ba bae san sha na ba, kullum a wahale nake

cikin gidan, to a hka yake son na haifa masa

yara, wllh Abba bana sonsa ka taimakeni

kasa ya bani takardata ynxun nn, biyayya

kawae yyi maka yake xaune da ni gida daya

a matsayin matarsa,” ta fashe da

matsanancin kuka takasa ci gaba, tun da ta

fara magana Aliyu ke kallonta baki bude.

 

Ganin bbu wanda ya iya cewa komai a falon don duk jikinsu yyi sanyi ya sa inteesar ta tsagaita

kukan

da take ta cigaba “snn Abba ni bada

yardana ya

sake aure ba, hasalima ni ban san xae yi

aure ba

sae ranar da ya kawo ni gunka da daddare

kke

tambayata ko nasani, to a nn ne ma nasan

aure

xae yi, kuma dama tun a hanya yyi threatn

dina

kan cewar ko me xaka tambayeni nace

nasani,

kuma Abba har yau yaki daukar batun

karatuna

da muhimmanci da nayi magana sae ya

dinga

hantarata wae baxan iya course din da nace

nake so ba, kuma Abba da yake cewa na

xubar

masa da ciki a tambayesa ko kula dani da

cikin

yake, Abba sae nayi kwana uku ban gansa

ba

gashi bbu abinda nake iyawa kullum a

wahale

nake kwana nake yini a gidan ga kuma

yunwa,

tunda ba iya girkin nake ba,” tayi shiru tana

share

hawayenta snn a hankali tace “lastly Abba

kayi

hakuri ba rashin kunya nake maka ba,

amma ka

tausaya min kayi masa magana ya sauwaka

min,

don baxan koma gidansa ba wllh na gama

aurensa,” Aliyu ya mike yana mata wani

mugun

kallo yana huci yace “munafuka,

makaryaciya

kawae, ki xo ki shake ni na baki takardar

taki

kuma wllh sae kinyi da kin sanin xubar min

da

ciki,” ya juya xae bar falon Abba ya dakatar

da

shi a fusace, inteesar ta fashe da kuka tace

“wllh Abba kace ya bani takardata bana

auren

kuma, bana sonsa,” Abba yana kallon Aliyu

yace

“dawo ka xauna,” ya kai minti kusan biyar a

tsaye kmr baxae xauna ba, sae da Anty

Nafeesa

tace “ba magana ake maka ba ka tsaya ma

mutane kallon rainin wayo,” ya juya ya

kalleta,

snn ya koma inda yake ya xauna yana ma

inteesar wani irin kallon, da ganinsa kasan

ran

maxa ya gama bacewa, Abba yace “cikin

maganganun da Fateema tayi a nn akwae

wanda

xaka karyata,” ya kauda kansa bae ce komai

ba

sae huci da yake, Abba yace “gud, dama tun

ba

yau ba nasan halinka, na kuma san xaka iya

aikata duk abinda fateema ta lissafo a nn,

kai

kam ban san wani irin mutum bne Aliyu,

kuma

gwara da Fateema ta gaya min abubuwan

da ta

dde tana boyewa a cikinta tana cutar

kanta,” ya

juya yana kallon Inteesar yace “amma

fateema

ke abinda kika aikata a ganin kinyi dai dai

knn,

me xaki ce ma mahaliccinki, ashe dama

karamin

tunani gare ki ban sani ba” inteesar dai

kanta na

kasa tana hawaye ta kasa cewa komai, Abba

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button