Hausa Novels

Lu’u Lu’u 17

D’auke idonshi yayi a kanta yace” Zafreen, shin ba ke kika bamu bayani akan sark’ar nan ba?”

Gyara tsayuwa tayi tace” E.”

D’orawa yayi da” Me yasa bakiyi tunanin hanyar da suka samu sark’ar ba? Kin tab’a jin mahaifiyarki tayi k’orafi akan b’atan sark’arta ne?”

Tsareshi tayi da ido tace” A’a, hasalima bamu san da b’atan sark’ar ba, daren da zan bar nan na fahimci bata tare da sark’ar.”

Buga sandarshi yayi k’asa sosai tare da d’aga sauti yace” To wannan dalilin ne yasa na rufeta, Juman ta ha’inceni ta yaudare ni, shiyasa na kawar da duk son da nake mata na hukunta ta.”

Da mamaki tace” Kana nufin Mah da hannunta a b’atan Zafeera kenan?”

Shiru ya mata ya juya ya shiga takawa a tsanake har ya koma kan kujerarshi ya zauna, waziri Khatar daya kalla yasa shi gyara tsayuwarshi ya kalleta yace” Gimbiyata, an samu sarauniya Juman da laifi dumu dumu na b’atan Zafeera, dan da bakinta ta fad’i hakan saboda ta kub’utar da ita.”

Dafe k’ugunta d’aya tayi ta cije leb’enta na k’asa tana girgiza kai, ta d’auki sakanni a haka kafin ta kalli sarki tace” Mahaifi na, yanzu haka tare muke da wanda ya sace ni ya kuma sace maka Zafeera.”

Da k’arfi ya mik’e akan kujerar yace” Me? Wanene shi? Yana ina? Me ya kawosa nan?”

Lumshe ido tayi ta motsa baki alamar tambayoyin sun hau mata kai ba kuma zata iya amsawa ba, a hankalce tace” Yana masaukin bak’i.”

Cikin zumud’i yace” Kenan suna can tare da Zafeera?”

” A’a.” Tana fad’a ta juya tana fad’in” Zan je na ga Mah, Adah ka rakani.”

Da kallo Adah dake kusa da sarki ya rakata yana jin takaicin iya shegen yarinyar nan, amma sarki Musail na kallonshi bai da zab’in daya wuce bin bayanta da sauri suka fita.

Suna fita sarki Musail ma ya kalli waziri yace” Wanene wannan? Me yasa ya zo nan bayan yasan zan iya halaka shi?”

Dhurani dake kan kujera kusa da waziri ne yace” Ka gafarce ni sarki na, ina ga ka fara had’uwa da shi, watak’ila akwai dalilinshi na zuwa nan.”

Da kallon tuhuma ya bishi yace” Kana nufin ko da magana ya zo na zauna na saurare shi? Bayan kuma ina zarginsa da nesanta ni da Zafeera.”

Waziri ma cewa yayi” Hakane sarki na, mu fara sauraranshi mu ji, ta haka zamu san inda Zafeera take.”

Jinjina kai yayi ya kalli Dhurani yace” Muje tare.”

Mik’ewa Dhurani yayi ya bi shi suka fita inda waziri ya ji haushin hakan, ya so aje da shi ya ji me ya kawosu me kuma za’a tattauna, hakan yasa shi jan tsaki ya fara safa da marwa dan ba zai iya zama ba har sai ya jie aka tattauna.

*Giobarh*

 

Duk da ta jima bata kwanta ba amma sai ga shi k’arfe 07:00 tana bugawa ta farka saboda sabon tashi, saida ta bud’a idon ta ne ta fahimci inda ta kwana, a gajiye kuma a kasalance ta yaye rufar ta sauka a gadon, gaban madubi ta k’arasa tayi tsaye tana kallon kanta da tunanin me zatayi ? Gudu zata fara da shi? Ko kuma gyaran makwancin data tashi? A sanyaye ta fad’a ban d’aki ta fara da wanke bakinta da fitsari sannan ta fito, gurin kaya ta fara dubawa dan ta ga ko zata samu k’ananan kaya na motsa jiki, saidai duka kaya ne manya a ciki irin wanda ta gani jikin matar nan ta jiya (Joyran).

Rufewa tayi ta koma kusa da tagar gurin, bud’ewa labulen tayi hakan yasa hasken safiyar shigowa d’akin, ta madubin ta dinga kallon tarin shukokin wanda suka mata kyau take kuma ayyana lallai zasuyi k’amshi gurin kuma zai yi sanyi.

Da sauri ta saki labulen ta nufi k’ofa dan fita ta shak’i wannan daddad’an oxygen d’in, tana bud’e k’ofar ta fara takawa, fitowarta tayi daidai da bud’a d’akin sarauniya Kossam da wata hadimar tayi d’auke da farantin abincinta, a ladabce ta gaishe da Ayam d’in ta amsa, fuskarta a sake tace “Dama da mutum ne a nan?”

Da girmamawa tace “E ranki shi dad’e, ai d’akin sarauniya ne.”

D’aga girarta tayi sama tace “Oh ! Zan iya shiga ciki?”

A ldabce tace “E to ranki shi dad’e zaki iya.”

Hannu ta kai ta bud’e k’ofar ita ce a gaba hadimar na bayanta, ganin matar kwance yasa Ayam kallon hadimar tace “Bata da lafiya ne?”

“E, ai ta jima kwance a haka.” Ta fad’a sanda take aje farantin hannunta, da tausayi Ayam ta kalli Kossam da idonta ke rufe tace “Me yake damunta ne?”

Girgiza kai tayi tace “A gaskiya ban sani ba, shekara uku da fara aikina a nan, nima a haka na sameta.”

Da mamaki ta waro ido tace “Shekara uku? To ita shekara nawa ta d’auka a haka?”

Cike da jimami tace “A yanda na ji suna fad’a shekara ashirin kenan.”

Da k’arfi tace “What? Oh my God.”

Ta fad’a tana k’arasawa ga Kossam, zaune tayi bakin gadon ta rik’o hannunta, kamar ta tsikareta da allura sai kawai ta tsam ta bud’a idonta ta zuba akan Ayam d’in, wani tattausan murmushi Ayam ta sauke ta kalli hadimar tace “Ta farka, tana magana ne?”

Girgiza kai tayi tace “A’a ranki shi dad’e.”

Kallon Kossam ta sake yi, sanyayyan murmushi ta sakar mata a karo na biyu ta sake jimk’e hannunta, cikin taushin murya tace “Kina ji a ranki kamar ki ce wacece ni ko?”

K’urawa fuskarta ido tayi tana son ta ga ko zata amsa lata da ido, sai kawai ta ji ta d’an jimk’i hannunta, kallon hannayen na su tayi sai kula ta sake kallonta tace “Kin gaji da kwanciyar nan haka ko?”

Sake jimk’e hannunta tayi, da sauri ta sake kallon hannayen na su, k’ura mata ido tayi tace “Kina so kiyi magana ne?”

Sake damk’e hannunta tayi, jinjina kai Ayam tayi tce “Zaki yi magana, zaki samu lafiya nan kusa ke ma.”

Mik’ewa tayi tsaye ta kalli hadimar tace “Taimaka min mu gyara mata jikinta ta ci abinci.”

Zaro ido tayi hadimar tace “A’a ranki shi dad’e, ai babu mai alhakin bata ko da ruwa ne sai mai girma Joyran.”

A yatsine ta kalleta zatayi magana sai kuma ta ji Kossam ta sake rik’e hannunga gam a cikin na ta kamar za’a rabasu, kallonta tayi da mamaki ta kalli hannayen na su, nazartarta tayi sosai ta shiga karantar yanayinta, sai kawai ta kalli hadimar tace “Wacece haka kuma?”

Tausasa murya tayi tace “K’anwar sarauniya ce, ita ke kula da ita tsawon lokaci.”

Mik’ewa tayi daga rank’wafawar tace “Kuma dole sai ita ce zata iya kula da ita, babu wani wanda zai iya saka hannunsa da sunan taimako?”

A tsawace tace “Malama kama min ita.”

Da sauri ta matsa suka kamata ta dinga nunawa Ayam d’in yanda suke taimaka mata, har baki saida ta wanke mata da mai ta tsefe mata kai sannan tace ma hadimar “Samo mata kayan sakawa.”

Da sauri hadimar dake mamakin iko na wannan yarinya ita ma tace “Ai kayanta suna d’aya d’akin, mai girma Joyran ce tasa aka mayar da su can.”

Previous page 1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button