Lu’u Lu’u 18

Jujjuya masa baki tayi ta fizge hannunta tace” Wannan kuma kai ka jiyo, amma ka sani inhar zaka dinga nuna ban da mahimmanci yanzu a gareka to abinda zai dinga faruwa kenan.”
Nunata yayi kamar zai tsone mata ido yace” Ki sani ke baki isa ki lalata min shirina akan Zafeera ba, kina gani akan idonki zan aureta kuma babu yanda zakiyi.”
Rai b’ace tace” To ko ka shirya hujojjin da zasu kareka daga zargi da jifan mutane, dan tabbas zasu san meye alak’ata da kai, sannan su san bayani a game da sabon yarimansu dake hanyar shigow duniyar.”
Tab’e baki yayi yace” Ki sani zaki burmawa cikinki wuk’a ne, na farko ke ce zaune a gidana, na biyu babu wanda ya tab’a gani na a b’angaren ki musamman da dare, na uku kowa dake gidan nan ya shaida irin shigar da kike yi, sannan ki tuna wani abu! Gimbiya Zafeera ta fara bayyana mana wani abun wanda shi ma zai iya sake jefaki bakin al’ummata.”
Yana fad’a ya juya ya bi ta k’ofar da zat sadashi da fadarshi dan gudanar da mulkinshi.
*Khazira*
Sarki Musail na shigowa suka had’a ido da Bukhatir, cak ya tsaya ya furta “Bukhatir?”
Mik’ewa Bukhatir yayi yana murmushin munafurci yace “Ranka shi dad’e, barka da shigowa.”
Takawa sarki Musail yayi yana k’arasa shiga ciki yana fad’in “Bukhatir, me ya kawoka gida na? Me kake yi a nan? Dama kai ne bak’on da ya zo?”
Dhurani ne ya kalli sarki Musail yace “Shugaba me yake faruwa? Ka san shi ne dama?”
Kallon Dhurani kawai yayi bai ce komai ba ya sake matsawa kusa da Bikhatir, a kausashe yace “Me ya kawoka nan Bukhatir?”
A ladabce dan ya samu abinda ya ke so ya sunkuyar da kai yace “…
*Kuyi hak’uri da wannan, na so ya fi haka wallahi.*
*Alhamdulillah*
The post Lu’u Lu’u 18 first appeared on 2gNovels.com.ng.
[ad_2]