Hausa Novels

Lu’u Lu’u 22

Sai kawai ta fashe da kuka ta matso kusanshi tace “Dama duk abinda ke faruwa shirinka ne? Ni da mahaifina da yar uwata duk muna cikin tsarinka ne?”

Girgiza kai tayi tana rage sautin kukan ta tace “Nayi nadamar saninka, ka daga yanzu na daina yarda da duk abinda kuke fad’a akan mahaifina, dama ina da kokonto akan haka, ta ya uba zai so kashe ‘yarsa, amma yanzu na fahimci komai, dalilin da yasa kake son na ci gaba da zama a nan ba wani dalili kenan.”

Rab’ashi tayi zata fkta sai kuma ta kalli fuskarshi tace” Zan je na ga mahaifina, i hate you.”

Da gudu ta fita a d’akin hakan yasa shi rasa me zai yi ma, to shi bai ga abin duk wannan rigimar ba, me take nufi to? Daga ganin wannan abun sai ta masa wata fasaara ta daban ?

Da sauri ya bi byanta ya fita a b’angaren na shi, sai dai yana fita tana shiga mota wani dogari ya rufe aka tayar, da kallo kawai ya bi motar dan mahaifinshi na tsaye ba zai yarda yayi wani yunkuri da zai janyo masa zargi ba.

The post Lu’u Lu’u 22 first appeared on 2gNovels.com.ng.

[ad_2]

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button