Hausa Novels

Lu’u Lu’u 23

Muryarshi ta tsinta yana fad’in “Ki ci abinci gimbiya.”

Da sauri ta kalleshi sannan ta kalli sauran kujerun guda goma cas amma su biyu ne kawai, d’an kallonshi tayi a sanyaye tace “Pah! Ina Mahh?”

Fuskarshi ta ga ta fara canzawa sai kuma ya wayance yace “Ki ci abinci, zaki ganta.”

Kallonshi tayi da tunanin kenan har yanzu tana rufe? In kam hakane dole tayi wani abu a kai, ajiyar zuciya ta sauke a hankali tace “To yar uwata fa?”

Murmushin yak’e ya mata yace “Tana shiryawa ne, zata zo yanzu.”

Jinjina kai tayi ta fara cin abinci sannu sannu, tana ci tana k’iyasta kud’in da aka kashe wurin dafa abinci da kuma dad’inshi, cikin k’agauta ya sake fad’in “Ki yi sauri ki ci abinci, bayinki na jiranki zasu rakaki sashenki kiyi wanka, talakawan gari suna waje suna jiran jin wani abu daga bakinki.”

Kallonshi tayi da mamakin jin furucinshi kamar na wanda baya taula kalamansa, jinjina kai kawai ta sake yi alamar to, shi kuma kallon fuskarta yayi sanda ta kalli plate d’in gabanta, harara ya sakar mata yana k’aramar k’wafa a ranshi yake ayyana” Babu ta yanda za’a yi ki zo cikin sauk’i, na tabbata wata k’ulalliyar suka k’ula miki ki zo ki min, kafin ki aiwatar zan kasheki ni kuma, mutuwarki kuma zata zama kamar had’ari babu wanda zai tuhume ni.”

Sam mantawa yayi da maganar zuci yake har saida ya furta” Tsinanniya kawai, ki mutu ko na huta.”

Da sauri ta d’ago jin yayi magana amma ba ta ji me yace ba tace” Pah magana kake?”

Da sauri ya girgiza kai yace” A’a karki damu, idan kin kammala ki je kiyi wanka ana jiranki.”

Lura da tayi kamar a matse yake da tayi wankan yasa ta cire hannunta a abincin ta ja kujerar ta baya tace” Zamu iya tafiya?”

Hadiman dake gefensu ya kalla yace” Ku rakata zuwa b’angaren ta,ku tabbatar kun kula min da yarinya.”

Rusunawa sukayi sosai su ukun kafin su rufa mata baya d’aya a gaba, wata duniyar aljannar suka kai ta a matsayin masaukinta, nan ma lokaci ta b’ata tana k’arewa sashin kallo, d’aya daga cikin hadiman ne tace” Bari na duba ruwan da aka had’a mi idan bai huce ba.”

Zata shiga ban d’akin Ayam tayi saurin cewa” Baki ji ba.”

Tsayawa tayi ta amsa, a nutse tace” Karki saka min ruwan mai zafi.”

Jinjina kai tayi tace” To bari sai a canza.”

Ban d’akin ta shiga inda d’aya daga ciki ta mik’owa Ayam babban towel sai k’amshi yake, tana shirin kallabin data yana a kai suka ji ihun wacce ke ban d’akin nan, da gudu suka shiga su ukun dan ganin ko lafiya, ai kam daf da bahon ruwan suka ganta hannunta d’aya a cikin ruwan wutar lantarki sai janta take.

Hankali tashe Ayam tace “Ku samo mana busashen abu.”

Da gudu suka fito ita kuma tana kallonta sai kakkarwa take, saidai ina kafin su dawo har rai yayi halin sa.

The post Lu’u Lu’u 23 first appeared on 2gNovels.com.ng.

[ad_2]

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button