Lu’u Lu’u 29

Kallon bafaden yayi ya masa alama da zai iya tafiya, jinjina kai yayi ya tashi zai fita yace “Na barku lafiya.”
Yana kaiwa bakin k’ofar ya bud’e Umad kuma na tsaye bakin k’ofar, d sauri ya sake zubewa k’asa yana fad’in “D’an sarki jikan sarki, barka da warhaka shugaba na, barka, barka.”
Wani kallo Umad ya masa hakan yasa ya rab’ashi ya wuce sum sum sum, cikin takon isa ya shigo d’akin yana kallon mahaifin na shi da kuma yarinyar nan.
Wangale baki sarki Wudar yayi ya fara kame kame ya rasa abin fad’a, har saida Umad d’in ya tsaya gabanshi ya kalli yarinyar yace “Je ki.”
Da sauri jikinta na rawa ta kama hanya ta fice a d’akin, ganin haka yasa Wudar matsawa kusanshi ya dafa kafad’arshi yace “D’ana, ka gane ko? Wannan d’in ai…ita..”
A nutse ya k’urawa fuskarshi ido yana kallo yace ”
*Alhamdulillah*
The post Lu’u Lu’u 29 first appeared on 2gNovels.com.ng.
[ad_2]